← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 157

Sashe 73

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ba amin ba wallahi wannan addu'a sai 'ya'ya"

"Matsoraciya, tunda kika kunso gara kiyi da yawa kawai"

Dariya tayi tana fatan Allah Ya kawowa Ummi miji tayi aure itama.

"Dama magana ce akan Radhiya da Awwab. Ki taimaka mu fitar da Mami kunyar marasa kunya Mairama. Dazu idan kinji irin kalaman batanci da suke fadawa Mami a gidan da akayi kamu sai kin kusa kuka."

Shiru Ummi tayi tana nazari. Itama sun yi da ita batare da sun gane ita bace suka zageta tas akan ta likewa Mami ita da 'ya'yanta. Ai kuwa zata taya Mami nuna musu kurensu ita ce fa Mairo 'yar kunamar Malamijo. 

"Zainab kisha kuruminki kawai ki zuba min ido wannan karon. Ni har za'a nuna min rashin mutumci ina diyar Ali Gidado? Kawaici ne kawai nake yi domin inganta musu zumunci amma tunda abin ya zama haka idan kinje gida ki fadawa Baba Hadir suyi magana da Major. Awwab na dawowa daga Ukraine a daura musu aure da yarinyar nan"

Da karfi Mama ta mike saboda farinciki har sai da cikinta ya amsa amma bata hakura ba ta rungume Ummi.

"Wani sha'ani sai bikin 'yar mutan Agadas. Kin biyani ko ba soso da sabulu kin wanke ni da kyau. Su Awwabu za'a shiga sahun manya kice"

Ummi ta dafe kai da kunya "wannan zancen ba dani ba"

"Wai da mu fara gyara amarya tun yanzu in soma aike" ta fada da shakiyanci ai kuwa tayi nasarar korar Ummi daga dakin tana cewa abu kusan wata goma gaba take wannan tunani tun yanzu.

**********

"Is it true you be Aboki?" Inyamurin ya tambayi Zayyan da gurbataccen turancinsa wanda aka fi sani da pidgin english.

"Ni bahaushe ne idan abinda kake nufi kenan" ya amsa masa da turanci cikin calm and gentle voice dinsa.

Ko a zaman kurkuku Zayyan ya fita daban saboda yadda zuciyarsa take mai kyau Allah Ya sanya masa kwarjini da haiba a cikin mutanen da yake.

Inyamurin ya daka tsalle yaga dan kasarsu ya rungume shi. Zayyan bai nuna kyama ga mutumin ba shima ya rike shi. Magana ya koma yi da normal turanci

"Sati na biyu a Wing B cikin wahalar mutanen da muke daki daya dasu. Wani Warden (gandiroba) ne jiya yace idan sun sake tabani nace ni dan uwan Zayyan ne."  Kallon Zayyan din yayi sosai "kasan me ya bani mamaki?"

"Sai ka fada"

"Ina ambaton sunanka nace kasarmu daya suka watse. Nayi mamaki matuka gaskiya. Who are you?"

Bai cika son yawan magana ba amma kuma baya son wulakanta mutum ba farko da ya gani a wurin da yake matsayin dan uwansa na kasa daya. Takaitaccen tarihin rayuwarsa ya bawa mutumin sai gashi yana hawaye.

"Yanzu kai soja ne kuma kayi wadannan shekarun babu wanda ya taba nemanka?"

"Nawa kundin qaddarar kenan"

"Aboki ni sunana Chibuzor Kalu. Matata ce 'yar kasar nan amma a UK muke da zama. Ta haihu ne tazo ganin gida da baby, to dama munyi da ita ni zanzo daukarsu. Ni dai bansan yaya akayi ba aka kamani da kwayoyi a jakata. Ka ganni nan ko taba bana sha amma anyi mana kudin goro kowa ya ga Igbo man sai yayi masa kallon mai ha'inci. Sun kulleni ne ana can ana binciken ainihin wanda ake zargin ya saka min kwayoyin a cikin kayana"

Zayyan ya tausaya masa domin yakan sami labarai akan masu harkar kwayoyi irin tsananin da suke shiga idan an kama su.

Shi da yake da saurin sabo sai gashi Chibuzor ya zama tamkar wani dansa. Ko ina tare zaka gansu a cikin prison dinnan har aka gama zaman shari'arsa na tsahon wata bakwai ana fafatawa aka gano sharri ne kawai aka yi masa. Ranar da zai fita yayi kuka har ya gode Allah. Bai san haka shakuwa take da tasiri ba sai da zai rabu da Lt Zayyan Muhammad Tureta.

"Sir please ka bani address dinka, a ina zan sami Maman Alheran?"

Karo na farko tun bayan shigowarsa wannan kangi Zayyan ya sami kansa da zubar hawaye. Shin yasa rai da zai sake shakar iska freedom ko kuwa? Akwai rabon idanunsa su sake kallon na Mairama masoyiyarsa da Alheran da kuma abinda Allah Ya azurtasu dashi? Rungume Chibuzor yayi yana hawaye ya fada masa sunan barrack din da ya zauna.

"Tell them Lieutenant Zayyan Muhammad Tureta is alive"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: "Alheran ZM Tureta"

Gajeren faduwar gaba taji lokacin da daya daga cikin malamansu kuma supervisor dinta ta leko da kanta ta kofar seminar hall din ta kira ta.

Duka daliban da suke aji daya tare su kadai suke zaune banda ita. Nasara tana zaune a kusa da ita cikin kujerun da aka zube a korido din domin zama ko hutawa tana karfafa mata gwiwa.

"Tante" Radhiya tace kamar tayi kuka.

"Ina nan ina jiranki kinji ko...jeki" Nasara tace da murmushi.

Kungiyar ma'aikatan jarida na kasar France ne suka rarraba kudade a fitattun jami'o'insu suna neman zaratan dalibai. Gasa ce suka saka na neman zakaran gwajin dafi inda aka baiwa daliban damar kowa ya kawo wata matsala da yake tunanin zaiyi kyau a bude program a kanta imma ta gidan TV ko rediyo domin wayarwa al'umma kai da kuma taimakawa ga wadanda abin ya shafa.

Dalibai uku ake son zaba a kowacce jami'a 'yan aji uku ko hudu za'a basu grant (tallafi na kudi) suje suyi aikin da suka kawo na wata shida su dawo makarantar dashi. Wandanda suka yi nasara kofa ce babba zata bude musu ta arzikin samar da program da kila duniya duka sai tasan da zamansu. Radhiya ta kusa wata tana ta bincike akan topic din da ya kamata tayi karshe ta tsaya akan abu guda bayan tayi magana da Ummi da Baba Hadir. Su kadai suka sani sai Nasara. Jiya ko runtsawa ta kasa yi ta gama hada slides na power point da zata yi presenting sannan ta dukufa sallah da addu'a. Yousuf shine babban malaminta na addini bayan ta dawo kasar. Bakin gwargwado tana da nata ilimin tun a gida don kafin su gama secondary ita da Emzee sunyi sauka. To amma ilimi na sauran fannonin addini Yousuf yayi fice wurin zaburar da ita a kansa shiyasa matsayi daban ta bashi. Tana girmama shi sosai idan suna tare sai ka rantse wata muguwar nutsattsiya ce babu rigimar nan.

Sai da ta gama addu'ar Annabi Yunus da salatin Annabi SAW sannan ta kalli zoben hannunta mai harafin A, aa hankali ta kaishi bakinta ta sumbata. Computer dinta ta bude aka jona ta projector wakilan kamfanin Dupont Broadcast Corporation (DBC) da malaman jami'ar da suke musu alkalanci suka fuskanceta.

Bakar abaya ta saka mai kyau da karancin ado irin wadda wuyata zagaye ne kawai bai sauka kasa ba. Adon duwatsunta maroon ne shiyasa tayi nadi da maroon din mayafi tana sanye da loafers suma maroon da suka zame mata yawancin takalman zuwa makaranta. Hall din an kashe duka fitilu babu sauran haske sai wanda yake fita daga makeken screen din projector din.

Bata ce musu komai ba sai wani gajeren video na sakan goma sha biyar da ta kunna musu. Filin yaki ne baka jin komai sai tashin bomabomai da harbi gami da ihun mutane da kukan yara. Wuri ne na firgici da tsoratarwa ga wanda bai san yaya mutanen da suke da 'yan uwa a wuraren da rikici ke ballewa suke ji ba. A tsakiyar wannan tashin hankali sojoji ne wani ya kwanta akan yara biyu ya toshe musu kunne saboda karar bomb. Wani ya dauko wata mata mai tsohon ciki yana gudu da ita ga jini ya wanke masa fuska alamun shima yaji rauni. Wani likita ne a cikin sojojin ya duka gaban dan uwansa soja da hannunsa ya fita saboda tashin bomb. Kai jama'a mutane ne a cikin tsanani basu san ina suka dosa ba. Duka mutanen da suke wurin tuni Radhiya ta kwashe hankulansu da tunaninsu ya dawo ga abinda zata gabatar.

Hoton karshe ya tsaya ne akan wadannan sojoji kowa da abinda yake yi na ceton al'ummar da babu lallai ma na kasarsa ne ta dora musu katon question mark (alamar tambaya).

Cikin turancinta da sautin muryarta zai baiwa mai sauraro damar gane cewa faransanci ya zaunu a bakinta tace.

"Who are they?"

Alkalai basu san me zata gabatar ba amma sun fara gyada kai in approval.

Murmushi tayi da ya kawata fuskarta ta dora da cewa "My name is Alheran and this. Is. The Military Voice"

Hotunan screen din sai suka sauya inda zaka ga wani sojan rungume tsakanin iyayensa, wani da 'ya'yansa, wani amaryarsa, wani matarsa da tsohon ciki wani kanne da yayyensa suna dariya, suna murmushi ko suna hawaye.

"Tun farkon lokaci yana daga abinda yake daga darajar kasashe yawan rundunar sojoji ko mayakansu. Sai dai mukan manta da cewa wadannan sojoji 'ya'ya ne, maza, iyaye kuma 'yan uwa ga wasu. Suna tafiya filin daga a lokutan da iyalansu suke tsananin bukatarsu. Sauran mutane suna zuwa wurin aiki su koma gida soja idan ya fita filin daga shi da jindadi sai ranar da yayi sa'ar komawa ga iyalansa lami lafiya. Cikinsu ko kunsan mutum nawa ne suka tafi iyalansu suna kuka suma suna na zuci amma basu dawo ba?"

Hotunan suka karkata ga iyalan sojoji suna kuka, wani wurin kuma gawarwarkin sojoji ne, wasu kuwa sojojin ne da nakasar rasa wasu bangarori na jikinsu.

"Kama daga KIA (killed in action), MIA (missing in action), dawowa gida da nakasa ta gabobi ko lalurar da take shafar kwakwalwa wadannan sojoji suna wahala matuka a duniya. Amma duk wanda ya dawo da wata tawaya ta jikinsa sai ya zama mutum mara amfani ga al'ummarsa. Babu abinda suka sani ko suka iya sai tsaro amma tunda basu da lafiyar yinsa shikenan amfaninsu ya kare. A haka rayuwar sojoji nawa muka manta saboda babu abinda zamu mora a tare dasu. Idan sun mutu iyalansu kadai ke da asara. Wasu sai dai su koma garuruwansu babu abokai, wasu matansu sun kasa zama dasu, yaransu kila sun girma sai dai su kare rayuwarsu cikin kadaici da jin kawunansu tamkar basu da wani sauran amfani"
Chapter 73 · 0% Book details