Sashe 149
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kin ji ki kuma, shiru ya kamata kiyi ki rinka taimaka mata idan tana son wani abu"
Gyada kai tayi sai kuma ta hau murmushi "Amma kai baka yi murna bane? Ni fa na matsu naji ranar haihuwar"
Hannunsa ya sakalo a kafadarta yana jinjina wautarta "Addata ta kaina ina tausayin Hamma nasan ya gamu da shiririta"
"Kai dalla me ka sani, Hammana yana ji dani sosai don wallahi jiyama da dadd......"
A gigice Emzee ya fara neman kofar fita daga falon yana cewa "na shiga uku don Allah kada ki fada"
Ya kai bakin kofa tace "kai wank...."
"Sai anjima" yace da sauri ya fita yana tunanin ko dai wanka za ta ce yayi mata tunda tace yana ji da ita.
Tabe baki tayi da ya fita din tace "meye don na fada maka ya tayani wanke-wanke ba abin farincikinka bane ace mijin yayarka yana sonta" wani tunani ne ya darsu a zuciyarta bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba harda rike ciki "shege Emzee ko dai yasan me akeyi ne...tabdi gara ya nemo mata mu kaishi."
Ta nufi part din 'yan matan gidan inda su Zahra suke ta kuma ganin Emzee da tiyo yana wanke fuska ta zuci tace sumumu kasau wannan idan kayi aure matarka ta shiga dubu da soyayya. Cikin 'yan uwata ta shige tare dasu Fauziyya ana mata tsiya bakin ya kasa ramawa. Bayan isha Awwab ya kirata wai tazo su tafi ta rasa yadda zata yi. Can sai ga Tante Nasara ta kirata suka fita har wajen gate sannan ta daga waya ta kira Yousuf. Da faransanci tace masa,
"Ga kanwarka nan ka kaiwa mijinta kafin Zainab ta cinyeni"
Ya kwashe da dariya "Mam ina sonki wallah"
"Da na kyaleka ka boye matarka ko? Zamu hadu a gida ne sai ka gaya min wanda ya baka shawarar satar amarya" ta ce tana dariya.
Tare suke da Awwab a kofar gidan Alh Ghoumar ko minti biyu ba'ayi ba suka iso. Baya Awwab ya bude mata ta shiga ta gaishe da Yousuf tana tambayarsa Arifah yace wurinta zasu je.
Wani katafaren hotel ne da yake cikin jerin manya a kasar baki daya suka shiga. Hawa na bakwai Yousuf ya bude mata wani daki bayan ya kira Arifah yace tare suke sannan suka juyo shi da Awwab zasu siyo musu abinci.
Radhiya da Arifah suka rungume junansu suna murna. Arifah ke fada mata yadda daga Yousuf zai kaita gida ranar dinner suka kare a hotel.
Radhiya tayi ta dariya suka koma hirar sabuwar rayuwarsu. Arifah ta girmi Radhiya sannan ta fita wayewa musamman ta wannan fanin. Shawarwari ta shiga bata yadda zata ajiye kunya ta bawa mijinta kulawar da ta dace.
"Kinga ba mazauni bane idan ba kya kulawa dashi yanzun nan wata zata rabaki dashi"
"Dena fada Sis" tace da rawar murya bata fatan ganin wannan rana. Ko zaiyi mata kishiya bata burin ace saboda gazawarta ne sai dai hali na rayuwa.
Goma da rabi suka dawo Yousuf ya shigo yace mijinta na jiranta a waje. Tana fitowa ta fada jikinsa sai da yayi mamaki kuma ya nuna jindadinsa sosai ita kuwa sabon karatun Arifah ta dauka.
"Miss me?" Yace yana mata jagora zuwa nasu dakin.
"So much Hammana"
"Love me?"
"For as long as I live" tace tana kashe masa ido.
Bude dakin yayi dama ya ajiye musu kayansu ya rungumeta "ki rinka sassauta min babyna wannan sabon salon naki zai hanani abin arziki"
Zama yayi ta dare cinyarsa abinta tana magana cikin jan rai "wane abin arziki da za kayi?"
"Uhmm wai da yau dai na bar amarya ta huta gajiya...to amma"
Tana ganin abin zaiyi gaba ta tashi tana raba idanu "kayi hakuri Hammana ji nayi ance wai haka yana kara kauna"
Guje-guje suke a dakin taki bari ya kamata yana cewa "kaunar zan nuna miki ai wadda ta karu"
"Chèri bani da lafiya fa"
"Harda karyar ciwo kike yi?"
Ta girgiza kai tana shagwabe masa "a'a lafiyata kalau ni dai kayi hakuri"
"Na hakura janbaki kawai zaki bani..."
Daga inda take ta taho gareshi da saurinta ta hade bakinsu "ba kayi bayani bane tun dazu kasa ina wani tunanin"
"Tunanin naki ma zai tabbata kema kin sani"
**********
Washegari tun shabiyu suke tsakanin gidajen kawunan nasu ita da Arifah wadda aka kawo officially. Sai yamma aka yi wasan hawan rakuma a wani babban fili inda amare da angwaye kai harma su Ummi da Daada suka yi shigar gargajiya ta 'yan kabilar tamasheq. Yousuf da Awwab sun sha rawani buzaye sak.
Radhiya da Arifah kuma nasu kayan harda sarkoki, abin hannu, na gashi da na hanci duk an makala musu sunyi kyau sosai. Kowacce amarya angonta ya taimaka mata ta hau rakumi su na rike da akalarsa an rufe rabin fuskar amaren suka zagaya wurin dasu ana ta daukar hoto.
Salame tayi kallo ta ga abin mamaki a zuri'ar dangin mijin Mairaman da ta wulakanta. Kannen Halifa da matar Alh Salisu sun zo kai kace sun fita matsayi a wurin saboda yadda ta zubar da mutumcinta a baya.
Ana tafawa amare da angwaye ance suyi tsere akan rakuman Emzee ya kalli Addarsa da mijinta ya zauna a bayanta ya rike linzamin rakumin da suke kai ya kalli Rahima da take kallonsu itama abin yana burgeta ya ce
"nima in zo in samarwa kaina buzuwa ko ma hau rakumi da bikinmu"
A can gefe take zaune mutane duk anyi gaba kallon tsere shine ya biyota don kawai ya bata haushi.
Wani matashi kyakkyawan gaske cikin jikokin Alh Sidi ta nuna masa duk da zafin kalamanta tana murmushi "Ya Emzee to ko muma a hada namu bikin ne? Ka ga Aman yace muna komawa zai zo wurin Ummi"
Hadari ma yafi fuskar Emzee kyan gani ya ce "yazo yayi mata me?"
"Maganar aure ce don yace ba da wasa yake ba" ta yi masa wani dan banzan murmushi da ya daure masa zuciya.
"Saboda an rasa mazajen aure a Nigeria daga zuwanki kwana daya a nan za ki ce kunyi maganar aure da wani" ya ce yana huci.
Kwafa tayi a zuci tana jindadin ko ma fushin me yake da ita bai dena sonta ba "Abin ne yazo mana a bazata"
"To bari kiji in fada miki indai Aman ne yana yana shaye-shaye ah to sai ki nemi wani"
Hannuwanta ta rungume tana kallon saitin Aman din "sai inyi masa addu'a Ya Emzee yanzu ba'a gudun mutum don hali taimaka masa ake ya chanja"
Bai san ya soma fada ba yace "inji uban wa? So kike ya rinka dukanki a gida? Ke wai da wane yare ma kuka magana bayan bai iya hausa ba"
Rahima ta dake tayi murmushin da ya sake kawata fuskarta "ko babu yare mun fahimci juna...Ya Allah Ka bani...."
Kishi tuni ya rufe masa idanu yace "Shut up, wallahi kika ce Ya baki Aman sai na tattakaki a wurin nan"
Ranta ya soma suya saboda bacin rai "Sai na fada din...Allah Ka "
Hannu ya daga zai mareta Mairama cikin bacin rai duk da bata san me ya hadasu ba amma ihunsa da daga hannunsa gareta ya matukar bata haushi.
"Muhammad kana hauka ne?" Ta daka masa tsawa.
Daga bayanta Salame ce ita kuma rashin ganin sanyin idaniyarta Rahima Idris Sumaila ne ya kawota wurin. Da sauri ta je ta kama hannun Rahiman wanda idonta ko gezau sai tarin ajiyar zuciya da take saukewa.
Ummi ta damki hannun Emzee saboda bata taba ganinsa haka ba dayake filin a gefen gidan Alh Ghoumar ne tattaki kadan suka shiga gidan. Dakin uwargidansa ta wuce dashi suna zuwa ta rufe kofar ta juyo a fusace.
"Karami baka taba yi min abinda ya sosa min rai kwatankwacin na yau ba saboda haka kafin nayi maka hukunci ka bude baki ka fada min me ya hadaka da Rahima har kake tunanin idan ka mareta zamu wanye lafiya"
Salame lokacin tana rike da hannun Rahima ta kama hannun kofar za ta bude Rahima ta hanata tana girgiza kai. Itama ta gaji so take ta san me tayi masa. Wannan wahalar soyayya har ina kullum yana azabtar mata da zuciya.
Ga mamakin Ummi sai kawai Emzee ya saka mata kuka ya dora kansa a kafadarta. Rahima na jin sautin kukansa itama ta fara nata yayin da jikin Salame yayi sanyi.
Sai da yayi mai isarsa yana cije lebe yace "Ummi I love her so much, wallahi Ummi Rahima nake son aure kamar zanyi hauka saboda son da nake mata"
Salame ta yiwa Rahima kallon tambaya wanda ita kuma taji furucinsa a bazata duba da yadda yake kyararta yanzu. Dariyar Ummin suka ji.
Fuskarta tana nuni da zallar farinciki ta dora hannu akan fuskarsa "Allah sarki Zayyan Turetana ya girma, to waye ya fada maka ana dukan mace idan ana sonta? Ko tace bata son karamin sojan Mairama ne?"
Takaici ya kama shi "Ummi yaya kike dariya this is not funny at all. Rahima fa nake nufi. Rahiman Gwaggo Salame wadda ta makantaki tsahon shekara goma"
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Rahima da Salame suka fada a tare jikinsu na rawa. Salame bata son Rahima taji zancen nan da wuri sannan a yau a yanzu taji wata katuwar nadama ta lullubeta a gaban 'yar cikinta.
Emzee ya soma ruwan hawaye "Ummi ni bansan 'yar Gwaggo Salame bace da bazan fara sonta ba, bakiji zuciyata ba Ummi ki rinka yi min addu'a Allah Ya yaye min. Ta yaya zan so 'yar wadda bata son mahaifiyata kullum burinta kiyi kuka"
Mairama ma sai ta fashe da kuka Emzee ya rungume mahaifiyarsa yana jin dacin zuciya da rashin adalcinta na son Rahima.
Hawaye na kwaranya a idanun Mairama tana share masa nasa ta ce "Karami idan kana son kanwarka nayi maka izini ka manta da komai ka nemi soyayyarta"
"A'a" ya shiga girgiza kai.
Gyada kai tayi sai kuma ta hau murmushi "Amma kai baka yi murna bane? Ni fa na matsu naji ranar haihuwar"
Hannunsa ya sakalo a kafadarta yana jinjina wautarta "Addata ta kaina ina tausayin Hamma nasan ya gamu da shiririta"
"Kai dalla me ka sani, Hammana yana ji dani sosai don wallahi jiyama da dadd......"
A gigice Emzee ya fara neman kofar fita daga falon yana cewa "na shiga uku don Allah kada ki fada"
Ya kai bakin kofa tace "kai wank...."
"Sai anjima" yace da sauri ya fita yana tunanin ko dai wanka za ta ce yayi mata tunda tace yana ji da ita.
Tabe baki tayi da ya fita din tace "meye don na fada maka ya tayani wanke-wanke ba abin farincikinka bane ace mijin yayarka yana sonta" wani tunani ne ya darsu a zuciyarta bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba harda rike ciki "shege Emzee ko dai yasan me akeyi ne...tabdi gara ya nemo mata mu kaishi."
Ta nufi part din 'yan matan gidan inda su Zahra suke ta kuma ganin Emzee da tiyo yana wanke fuska ta zuci tace sumumu kasau wannan idan kayi aure matarka ta shiga dubu da soyayya. Cikin 'yan uwata ta shige tare dasu Fauziyya ana mata tsiya bakin ya kasa ramawa. Bayan isha Awwab ya kirata wai tazo su tafi ta rasa yadda zata yi. Can sai ga Tante Nasara ta kirata suka fita har wajen gate sannan ta daga waya ta kira Yousuf. Da faransanci tace masa,
"Ga kanwarka nan ka kaiwa mijinta kafin Zainab ta cinyeni"
Ya kwashe da dariya "Mam ina sonki wallah"
"Da na kyaleka ka boye matarka ko? Zamu hadu a gida ne sai ka gaya min wanda ya baka shawarar satar amarya" ta ce tana dariya.
Tare suke da Awwab a kofar gidan Alh Ghoumar ko minti biyu ba'ayi ba suka iso. Baya Awwab ya bude mata ta shiga ta gaishe da Yousuf tana tambayarsa Arifah yace wurinta zasu je.
Wani katafaren hotel ne da yake cikin jerin manya a kasar baki daya suka shiga. Hawa na bakwai Yousuf ya bude mata wani daki bayan ya kira Arifah yace tare suke sannan suka juyo shi da Awwab zasu siyo musu abinci.
Radhiya da Arifah suka rungume junansu suna murna. Arifah ke fada mata yadda daga Yousuf zai kaita gida ranar dinner suka kare a hotel.
Radhiya tayi ta dariya suka koma hirar sabuwar rayuwarsu. Arifah ta girmi Radhiya sannan ta fita wayewa musamman ta wannan fanin. Shawarwari ta shiga bata yadda zata ajiye kunya ta bawa mijinta kulawar da ta dace.
"Kinga ba mazauni bane idan ba kya kulawa dashi yanzun nan wata zata rabaki dashi"
"Dena fada Sis" tace da rawar murya bata fatan ganin wannan rana. Ko zaiyi mata kishiya bata burin ace saboda gazawarta ne sai dai hali na rayuwa.
Goma da rabi suka dawo Yousuf ya shigo yace mijinta na jiranta a waje. Tana fitowa ta fada jikinsa sai da yayi mamaki kuma ya nuna jindadinsa sosai ita kuwa sabon karatun Arifah ta dauka.
"Miss me?" Yace yana mata jagora zuwa nasu dakin.
"So much Hammana"
"Love me?"
"For as long as I live" tace tana kashe masa ido.
Bude dakin yayi dama ya ajiye musu kayansu ya rungumeta "ki rinka sassauta min babyna wannan sabon salon naki zai hanani abin arziki"
Zama yayi ta dare cinyarsa abinta tana magana cikin jan rai "wane abin arziki da za kayi?"
"Uhmm wai da yau dai na bar amarya ta huta gajiya...to amma"
Tana ganin abin zaiyi gaba ta tashi tana raba idanu "kayi hakuri Hammana ji nayi ance wai haka yana kara kauna"
Guje-guje suke a dakin taki bari ya kamata yana cewa "kaunar zan nuna miki ai wadda ta karu"
"Chèri bani da lafiya fa"
"Harda karyar ciwo kike yi?"
Ta girgiza kai tana shagwabe masa "a'a lafiyata kalau ni dai kayi hakuri"
"Na hakura janbaki kawai zaki bani..."
Daga inda take ta taho gareshi da saurinta ta hade bakinsu "ba kayi bayani bane tun dazu kasa ina wani tunanin"
"Tunanin naki ma zai tabbata kema kin sani"
**********
Washegari tun shabiyu suke tsakanin gidajen kawunan nasu ita da Arifah wadda aka kawo officially. Sai yamma aka yi wasan hawan rakuma a wani babban fili inda amare da angwaye kai harma su Ummi da Daada suka yi shigar gargajiya ta 'yan kabilar tamasheq. Yousuf da Awwab sun sha rawani buzaye sak.
Radhiya da Arifah kuma nasu kayan harda sarkoki, abin hannu, na gashi da na hanci duk an makala musu sunyi kyau sosai. Kowacce amarya angonta ya taimaka mata ta hau rakumi su na rike da akalarsa an rufe rabin fuskar amaren suka zagaya wurin dasu ana ta daukar hoto.
Salame tayi kallo ta ga abin mamaki a zuri'ar dangin mijin Mairaman da ta wulakanta. Kannen Halifa da matar Alh Salisu sun zo kai kace sun fita matsayi a wurin saboda yadda ta zubar da mutumcinta a baya.
Ana tafawa amare da angwaye ance suyi tsere akan rakuman Emzee ya kalli Addarsa da mijinta ya zauna a bayanta ya rike linzamin rakumin da suke kai ya kalli Rahima da take kallonsu itama abin yana burgeta ya ce
"nima in zo in samarwa kaina buzuwa ko ma hau rakumi da bikinmu"
A can gefe take zaune mutane duk anyi gaba kallon tsere shine ya biyota don kawai ya bata haushi.
Wani matashi kyakkyawan gaske cikin jikokin Alh Sidi ta nuna masa duk da zafin kalamanta tana murmushi "Ya Emzee to ko muma a hada namu bikin ne? Ka ga Aman yace muna komawa zai zo wurin Ummi"
Hadari ma yafi fuskar Emzee kyan gani ya ce "yazo yayi mata me?"
"Maganar aure ce don yace ba da wasa yake ba" ta yi masa wani dan banzan murmushi da ya daure masa zuciya.
"Saboda an rasa mazajen aure a Nigeria daga zuwanki kwana daya a nan za ki ce kunyi maganar aure da wani" ya ce yana huci.
Kwafa tayi a zuci tana jindadin ko ma fushin me yake da ita bai dena sonta ba "Abin ne yazo mana a bazata"
"To bari kiji in fada miki indai Aman ne yana yana shaye-shaye ah to sai ki nemi wani"
Hannuwanta ta rungume tana kallon saitin Aman din "sai inyi masa addu'a Ya Emzee yanzu ba'a gudun mutum don hali taimaka masa ake ya chanja"
Bai san ya soma fada ba yace "inji uban wa? So kike ya rinka dukanki a gida? Ke wai da wane yare ma kuka magana bayan bai iya hausa ba"
Rahima ta dake tayi murmushin da ya sake kawata fuskarta "ko babu yare mun fahimci juna...Ya Allah Ka bani...."
Kishi tuni ya rufe masa idanu yace "Shut up, wallahi kika ce Ya baki Aman sai na tattakaki a wurin nan"
Ranta ya soma suya saboda bacin rai "Sai na fada din...Allah Ka "
Hannu ya daga zai mareta Mairama cikin bacin rai duk da bata san me ya hadasu ba amma ihunsa da daga hannunsa gareta ya matukar bata haushi.
"Muhammad kana hauka ne?" Ta daka masa tsawa.
Daga bayanta Salame ce ita kuma rashin ganin sanyin idaniyarta Rahima Idris Sumaila ne ya kawota wurin. Da sauri ta je ta kama hannun Rahiman wanda idonta ko gezau sai tarin ajiyar zuciya da take saukewa.
Ummi ta damki hannun Emzee saboda bata taba ganinsa haka ba dayake filin a gefen gidan Alh Ghoumar ne tattaki kadan suka shiga gidan. Dakin uwargidansa ta wuce dashi suna zuwa ta rufe kofar ta juyo a fusace.
"Karami baka taba yi min abinda ya sosa min rai kwatankwacin na yau ba saboda haka kafin nayi maka hukunci ka bude baki ka fada min me ya hadaka da Rahima har kake tunanin idan ka mareta zamu wanye lafiya"
Salame lokacin tana rike da hannun Rahima ta kama hannun kofar za ta bude Rahima ta hanata tana girgiza kai. Itama ta gaji so take ta san me tayi masa. Wannan wahalar soyayya har ina kullum yana azabtar mata da zuciya.
Ga mamakin Ummi sai kawai Emzee ya saka mata kuka ya dora kansa a kafadarta. Rahima na jin sautin kukansa itama ta fara nata yayin da jikin Salame yayi sanyi.
Sai da yayi mai isarsa yana cije lebe yace "Ummi I love her so much, wallahi Ummi Rahima nake son aure kamar zanyi hauka saboda son da nake mata"
Salame ta yiwa Rahima kallon tambaya wanda ita kuma taji furucinsa a bazata duba da yadda yake kyararta yanzu. Dariyar Ummin suka ji.
Fuskarta tana nuni da zallar farinciki ta dora hannu akan fuskarsa "Allah sarki Zayyan Turetana ya girma, to waye ya fada maka ana dukan mace idan ana sonta? Ko tace bata son karamin sojan Mairama ne?"
Takaici ya kama shi "Ummi yaya kike dariya this is not funny at all. Rahima fa nake nufi. Rahiman Gwaggo Salame wadda ta makantaki tsahon shekara goma"
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Rahima da Salame suka fada a tare jikinsu na rawa. Salame bata son Rahima taji zancen nan da wuri sannan a yau a yanzu taji wata katuwar nadama ta lullubeta a gaban 'yar cikinta.
Emzee ya soma ruwan hawaye "Ummi ni bansan 'yar Gwaggo Salame bace da bazan fara sonta ba, bakiji zuciyata ba Ummi ki rinka yi min addu'a Allah Ya yaye min. Ta yaya zan so 'yar wadda bata son mahaifiyata kullum burinta kiyi kuka"
Mairama ma sai ta fashe da kuka Emzee ya rungume mahaifiyarsa yana jin dacin zuciya da rashin adalcinta na son Rahima.
Hawaye na kwaranya a idanun Mairama tana share masa nasa ta ce "Karami idan kana son kanwarka nayi maka izini ka manta da komai ka nemi soyayyarta"
"A'a" ya shiga girgiza kai.