Sashe 150
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kuka take sosai tace "Lallai ashe baka da wayo ban sani ba. Abinda Adda Salame tayi min ALKHAIRI NE babba a gareni. Yau da banyi wannan makantar ba maimakon murna Karami zan shiga rudani mara misaltuwa ne akan dawowar mahaifinku. Ko kasan cewa ko banyi auren soyayya ba dole zan nemi mijin aure saboda inganta rayuwarka da ta yayarka? Da yanzu ina da 'ya'ya da wani mutumin ba Zayyan Tureta ba fa Karami. Kana tsammanin duk wanda na aura ga zuri'a tsakaninmu zan iya barinshi kai tsaye saboda naku mahaifin ne? Kasan girman dake tattare da aure irin wannan kuwa. Ga mijin da nake so ya dawo amma wani yayi mana shamaki. Kila Allah Ya jarabceni da son sa fiye da babanku"
Ta sake fashewa da kuka " nayi imani da yanzu mahaifinku yana cikin kuncin rayuwa duk da tarin arzikin da ya samu. Ciki ne dani Karami da ta ina kake tunanin Umminka zata sami wani rabon ta rabu da wani mijin da yara ta dawowa tsohon mijinta...ka duba girman wannan alkhairi da Allah Ya bamu ka gode Masa domin ni wannan kadai ya isheni dalilin da na yafewa Addata"
Bai taba tunani makamancin wannan ba amma duk abinda ta fada masa gaskiya ne. Kukansu suka yi sosai sannan yace "duk da haka Ummina bazan iya ba. Ki yi min addu'a zan sami wata in kawo miki"
Salame da Rahima sunji komai haka Radhiya wadda fitsari ya koro tun tsayuwar su Rahima a wurin take bayansu tana jin komai. Ganinta kawai suka yi ta wucesu ya bude kofar dakin ta shige tsakanin Ummi da Karami suna hawaye.
Rahima kuwa da sauri ta matsa yadda babu mai hangosu daga cikin dakin ta shiga na kusa dashi da bata san ko na waye ba tana fitar da numfashi da kyar ta rike kirjinta tana dannawa. Salame ta gigice ta dafata "Rahimata yaya? Me ya sameki"
A matukar raunane ta kalli Salamen idonta babu hawaye ta ce "Umma, don Allah nima ki soni kamar yadda Ummi ke son su Adda Radhiya. Wallahi Umma idan kika soni ko...uhmm nayi miki alkawarin zan zama 'ya tagari a wurinki ko banyi kudi ba zanyi miki biyayya."
Magana take kamar zautacciya saboda tsananin tashin hankali ace mahaifiyarta, hasken rayuwarta, inuwar jindadinta ta aikata mummunan abu irin wannan.
Salame sai hawayen mai cikea nadama sosai taji Rahiman ta kama hannunta "Umma nima kiyi min addu'a don wallahi ina son Ya Emzee...kinji kirjina Umma yana min zafi saboda na rabu da shi. Bazan iya zama da shi ba har abada saboda zaiyi ta kallonmu da laifin da muka yiwa Ummi"
Kukan Salame ya dadu ta rungume Rahima sosai a jikinta "ba ke kika yi laifin ba nice nayi kuma zan je na nemi yafiyarta."
"Duk abinda kika yi nima na dauka Umma. Shi baya gudun Ummi sai ni zan gujeki....Allah Ya kiyaye"
Salame ta dago kan Rahima ta ce "kiyi kuka Rahimata kiji sanyi a ranki. Idan Mairama tace sai na kwanta na bata hakuri sannan zata yarda Karami ya aureki zanyi...Rahimata kiyi hakuri kullum kuka nake sakaki akan son zuciyata"
Mikewa Rahima tayi harda karfin halin murmushi "ba kuka nake ba Umma kizo muje ana tsere mu cigaba da kallo"
Kafin Salame ta ankara Rahima ta fita daga dakin ta durkushe a wurin ita kuwa tana kuka mai tsananin taba zuciya...waye ya aiketa kuma me ya rudeta ta rinka lalata rayuwarta da ta iyalinta da hannunta.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Alhamdulillah!
Alhamdulillah!!
Alhamdulillah!!!
Cikin amincin Allah a yau Ya nufeni da cika alkhairina gareku na kawo muku karshen KDM. Jinjinar ban girma gareku baki daya ahalin groups dinnan. Nagode Allah Ya bar zumunci.
Abinda na rubuta mai amfani Allah Yasa ni daku mu amfana. Wanda yake na kuskure Ya kawar da hankulanmu daga kai Ya yafe min.
Ina rokonku alfarmar wannan wata mai daraja da zamu shiga duk wadda na taba yiwa ba daidai ba ku yafe min, nima na yafe muku.
Abu na karshe muna rokon Allah Ya Dubi sojojinmu Ya amintar da rayuwarsu Ya karesu a duk inda suke.
Don Allah kada mu manta a rike min amana domin na kawo muku wannan labari ne kashi na daya da na biyu a hade. Wasunku sun sani ba karamin aiki bane zaman typing da hada labari. Don Allah ba don ni ba yadda muka hadu lafiya mu rabu lafiya kada kowa ya shiga hakkin kowa.
SonSo Fisabilillah
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Kasa zama Salame tayi ta tashi bin bayan Rahima sai ganin Mairama tayi tana dube dube. Ita take nema saboda Radhiya ta fada mata cewa sun ji komai. Daurewa tayi ta saki fuska ta nunawa Salamen kofar dakin tana so ta shiga su yi magana. Ita yanzu neman sulhu take yi saboda yadda damuwar Rahima ta zame mata kamar an ajiye mata dutsen dala a zuciya.
Su na shiga kuwa ta juyo tana hada hannuwa ga idanunta sunyi ja sosai ta ce "Mairama nayi miki ba daidai ba nima na sani. Ba ke kadai ba duk wanda ya rabeni na cutar dashi na cuci kaina kuma, amma ki yiwa Allah da ManzonSa kada Rahimata ta biya bashin da ba ita taci ba"
Mairama tana iya ganin gaskiyar maganganun Salame. Idan ma ba ta tuba bane don girman laifinta kallo daya za ka yi mata kasan cewa she is desperate, ta kai kololuwar bukatuwa da neman agaji a wurin wadda ta dade tana farautar farincikinta.
"Adda Salame nan ba muhallin wannan maganae bane ki bari mu koma gida" ta ce mata tare da mikewa za ta fita.
Da sauri Salame ta tashi ita ma "babu damuwa Abujan zan biki wallahi"
Murmushi Mairama tayi ganin cikin lokaci kalilan Salame ta sauya. Za ta bude kofa kenan ta ga hannunta ta riko nata hannun da dan saurinta.
"Tsaya dai mu yita da wajewa Mairama kinga a nan wurin...." ta fita ta tsaya daga kofar dakin inda suka tsaya dazu da Rahima "naji komai lokacin da kike fadawa Karami cewa kin yafe min. Kinga an rufe wannan shaftar kada sai mun tafi kice ba haka ba, ni kuma nasan naji da kunnuwana"
Guntun tsaki Mairama tayi da dariya, mai hali baya fasa halinsa "tun kafin ki ce komai na riga na yafe miki Adda"
Wani abu taji ya sauka daga makoshinta ta saki murmushi korayen hakoran nan su ka bayyana. A take zuciyar Mairama ta soma tashi ta danyu baya.
Cikin sigar rainin wayo wadda za ta nuna Salame har kullum Salame ce sai ana mata uzuri ta ce "sai naji kuna zancen ciki kuma? Ina ke ina sake haihuwa an fara girma ga 'ya'ya suna tafiya gidan miji"
Idan ta biye mata ba fa shiryawa zasuyi ba sai ma dai a karawa rigimar fetur. Amma ko yaya sai ta dan rama za ta ji dadi.
"Soyayyar kenan Adda, ba dare ba rana kullum miji yana dokinka. Indau kuma batun auren Radhiya ne kada wannan ya dameki ni nan harda matar Karami sai mun kara haihuwa" tana fada a zuciyarta tana cewa (Allah Kada ka nuna min wannan bakar rana)
Ta sake tabawa Salame inda yake mata kaikayi ta ce "zaki sha aiki kuwa don indai Rahimata ni ta biyo za ki kwatsa 'ya'ya kamar dabino. Za dai kiyi masa maganar ko? Ba yabon kai ba ni ban taba ganin 'ya mai ladabi da biyayyarta ba. Nake fada miki halin Sahabbai ta gado"
Ran ta yana baci da maganganun farkon gashi na karshen suna bata dariya shiyasa kawai ta fita tana murmushi da rokawa 'yar uwarta shiriya.
**********
Emzee dakin da suka yi masauki ya tafi ya kwanta yana ta juyi ya rasa shawarar da ya kamata ya dauka cikin dimbin shawarwarin da zuciyarsa take bashi akan Rahima. Bari dai su koma gida yayi magana da Daada. A haka gani yake soyayya bata yi masa adalci ba ta kaishi inda baya son zuwa kuma babu alamun za ta fiddo shi nan kusa.
Radhiya kuwa da ta fito janyeta akayi za'a cigaba da hotuna jikinta duk babu kwari. Awwab ya kula da yadda tayi zuru-zuru kwalliyar ta goge saboda cabewar da tayi da hawaye sai ta goge kawai shiyasa ganinta haka ya shiga damuwa saboda bata da walwala. Samu yayi ya faki ido saboda yamma da tayi hankalin iyaye yayi nesa dasu ya fitar da ita daga wurin. Rawaninsa ya cire ya nemar musu taxi ko Yousuf bai nema ba suka koma hotel dinsu.
A hanya bai ce mata komai ba sai da suka shiga dakinsu ya rage mata kayan jikinta da danginsu sarkoki da sauran kayan adon ya zaunar da ita a gefen gado sannan ya zauna a kasa a gabanta ya dora kafafunta akan cinyarsa yana matsawa a hankali.
"Me ya sameki Alheran?"
Dama kiris take jira kawai ta fashe masa da kuka. Hankalinsa a tashe ya tashi ya zauna a gefenta ya rungumeta tayi kukan ta gaji. Sai da ya lura numfashinta ya soma dawowa daidai ya sake tambayarta.
Da kyar ta iya fada masa abinda ya riga yaji daga wurin Daada lokacin da suka je Sumaila bayan Salame ta daketa. Sai dai yayi matukar kaduwa game da dalilin makantar Ummi da kuma karshen bayanin Radhiyan wanda shine musabbabin kukanta a yanzu.
"Hammana ka tuna lokacin da aka ce na hakura da kai saboda kada na bata zumunci?"
Ya gyada kai yana tuna lokaci mai daci da ya shude a rayuwarsa. Ya azabtu da rashin cikar burinsa ya kuma ji haushin amincewarta a lokacin taki goya masa baya. Siririyar muryarta da ta dashe saboda kuka ce ta katse shi yaji ta ce,
"It was so painful Chèri sai lokacin ma na fara sonka sosai. Yanzu yaya Emzee zai ji? Yana son Rahima ashe kuma yana gudunta saboda Ummi. Emzeee yana da sa abu a rai nasan da wahala yau ya iya bacci"
Awwab sakin baki yayi yana kallon ikon Allah. Radhiya ta cigaba da fadin halin da kaninta zai shiga cike da tausayawa.
Hade bakin nasa yayi ya ce "yanzu duk wannan hawayen na Emzee ne ba ma Ummi ba?"
Ta sake fashewa da kuka " nayi imani da yanzu mahaifinku yana cikin kuncin rayuwa duk da tarin arzikin da ya samu. Ciki ne dani Karami da ta ina kake tunanin Umminka zata sami wani rabon ta rabu da wani mijin da yara ta dawowa tsohon mijinta...ka duba girman wannan alkhairi da Allah Ya bamu ka gode Masa domin ni wannan kadai ya isheni dalilin da na yafewa Addata"
Bai taba tunani makamancin wannan ba amma duk abinda ta fada masa gaskiya ne. Kukansu suka yi sosai sannan yace "duk da haka Ummina bazan iya ba. Ki yi min addu'a zan sami wata in kawo miki"
Salame da Rahima sunji komai haka Radhiya wadda fitsari ya koro tun tsayuwar su Rahima a wurin take bayansu tana jin komai. Ganinta kawai suka yi ta wucesu ya bude kofar dakin ta shige tsakanin Ummi da Karami suna hawaye.
Rahima kuwa da sauri ta matsa yadda babu mai hangosu daga cikin dakin ta shiga na kusa dashi da bata san ko na waye ba tana fitar da numfashi da kyar ta rike kirjinta tana dannawa. Salame ta gigice ta dafata "Rahimata yaya? Me ya sameki"
A matukar raunane ta kalli Salamen idonta babu hawaye ta ce "Umma, don Allah nima ki soni kamar yadda Ummi ke son su Adda Radhiya. Wallahi Umma idan kika soni ko...uhmm nayi miki alkawarin zan zama 'ya tagari a wurinki ko banyi kudi ba zanyi miki biyayya."
Magana take kamar zautacciya saboda tsananin tashin hankali ace mahaifiyarta, hasken rayuwarta, inuwar jindadinta ta aikata mummunan abu irin wannan.
Salame sai hawayen mai cikea nadama sosai taji Rahiman ta kama hannunta "Umma nima kiyi min addu'a don wallahi ina son Ya Emzee...kinji kirjina Umma yana min zafi saboda na rabu da shi. Bazan iya zama da shi ba har abada saboda zaiyi ta kallonmu da laifin da muka yiwa Ummi"
Kukan Salame ya dadu ta rungume Rahima sosai a jikinta "ba ke kika yi laifin ba nice nayi kuma zan je na nemi yafiyarta."
"Duk abinda kika yi nima na dauka Umma. Shi baya gudun Ummi sai ni zan gujeki....Allah Ya kiyaye"
Salame ta dago kan Rahima ta ce "kiyi kuka Rahimata kiji sanyi a ranki. Idan Mairama tace sai na kwanta na bata hakuri sannan zata yarda Karami ya aureki zanyi...Rahimata kiyi hakuri kullum kuka nake sakaki akan son zuciyata"
Mikewa Rahima tayi harda karfin halin murmushi "ba kuka nake ba Umma kizo muje ana tsere mu cigaba da kallo"
Kafin Salame ta ankara Rahima ta fita daga dakin ta durkushe a wurin ita kuwa tana kuka mai tsananin taba zuciya...waye ya aiketa kuma me ya rudeta ta rinka lalata rayuwarta da ta iyalinta da hannunta.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Alhamdulillah!
Alhamdulillah!!
Alhamdulillah!!!
Cikin amincin Allah a yau Ya nufeni da cika alkhairina gareku na kawo muku karshen KDM. Jinjinar ban girma gareku baki daya ahalin groups dinnan. Nagode Allah Ya bar zumunci.
Abinda na rubuta mai amfani Allah Yasa ni daku mu amfana. Wanda yake na kuskure Ya kawar da hankulanmu daga kai Ya yafe min.
Ina rokonku alfarmar wannan wata mai daraja da zamu shiga duk wadda na taba yiwa ba daidai ba ku yafe min, nima na yafe muku.
Abu na karshe muna rokon Allah Ya Dubi sojojinmu Ya amintar da rayuwarsu Ya karesu a duk inda suke.
Don Allah kada mu manta a rike min amana domin na kawo muku wannan labari ne kashi na daya da na biyu a hade. Wasunku sun sani ba karamin aiki bane zaman typing da hada labari. Don Allah ba don ni ba yadda muka hadu lafiya mu rabu lafiya kada kowa ya shiga hakkin kowa.
SonSo Fisabilillah
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Kasa zama Salame tayi ta tashi bin bayan Rahima sai ganin Mairama tayi tana dube dube. Ita take nema saboda Radhiya ta fada mata cewa sun ji komai. Daurewa tayi ta saki fuska ta nunawa Salamen kofar dakin tana so ta shiga su yi magana. Ita yanzu neman sulhu take yi saboda yadda damuwar Rahima ta zame mata kamar an ajiye mata dutsen dala a zuciya.
Su na shiga kuwa ta juyo tana hada hannuwa ga idanunta sunyi ja sosai ta ce "Mairama nayi miki ba daidai ba nima na sani. Ba ke kadai ba duk wanda ya rabeni na cutar dashi na cuci kaina kuma, amma ki yiwa Allah da ManzonSa kada Rahimata ta biya bashin da ba ita taci ba"
Mairama tana iya ganin gaskiyar maganganun Salame. Idan ma ba ta tuba bane don girman laifinta kallo daya za ka yi mata kasan cewa she is desperate, ta kai kololuwar bukatuwa da neman agaji a wurin wadda ta dade tana farautar farincikinta.
"Adda Salame nan ba muhallin wannan maganae bane ki bari mu koma gida" ta ce mata tare da mikewa za ta fita.
Da sauri Salame ta tashi ita ma "babu damuwa Abujan zan biki wallahi"
Murmushi Mairama tayi ganin cikin lokaci kalilan Salame ta sauya. Za ta bude kofa kenan ta ga hannunta ta riko nata hannun da dan saurinta.
"Tsaya dai mu yita da wajewa Mairama kinga a nan wurin...." ta fita ta tsaya daga kofar dakin inda suka tsaya dazu da Rahima "naji komai lokacin da kike fadawa Karami cewa kin yafe min. Kinga an rufe wannan shaftar kada sai mun tafi kice ba haka ba, ni kuma nasan naji da kunnuwana"
Guntun tsaki Mairama tayi da dariya, mai hali baya fasa halinsa "tun kafin ki ce komai na riga na yafe miki Adda"
Wani abu taji ya sauka daga makoshinta ta saki murmushi korayen hakoran nan su ka bayyana. A take zuciyar Mairama ta soma tashi ta danyu baya.
Cikin sigar rainin wayo wadda za ta nuna Salame har kullum Salame ce sai ana mata uzuri ta ce "sai naji kuna zancen ciki kuma? Ina ke ina sake haihuwa an fara girma ga 'ya'ya suna tafiya gidan miji"
Idan ta biye mata ba fa shiryawa zasuyi ba sai ma dai a karawa rigimar fetur. Amma ko yaya sai ta dan rama za ta ji dadi.
"Soyayyar kenan Adda, ba dare ba rana kullum miji yana dokinka. Indau kuma batun auren Radhiya ne kada wannan ya dameki ni nan harda matar Karami sai mun kara haihuwa" tana fada a zuciyarta tana cewa (Allah Kada ka nuna min wannan bakar rana)
Ta sake tabawa Salame inda yake mata kaikayi ta ce "zaki sha aiki kuwa don indai Rahimata ni ta biyo za ki kwatsa 'ya'ya kamar dabino. Za dai kiyi masa maganar ko? Ba yabon kai ba ni ban taba ganin 'ya mai ladabi da biyayyarta ba. Nake fada miki halin Sahabbai ta gado"
Ran ta yana baci da maganganun farkon gashi na karshen suna bata dariya shiyasa kawai ta fita tana murmushi da rokawa 'yar uwarta shiriya.
**********
Emzee dakin da suka yi masauki ya tafi ya kwanta yana ta juyi ya rasa shawarar da ya kamata ya dauka cikin dimbin shawarwarin da zuciyarsa take bashi akan Rahima. Bari dai su koma gida yayi magana da Daada. A haka gani yake soyayya bata yi masa adalci ba ta kaishi inda baya son zuwa kuma babu alamun za ta fiddo shi nan kusa.
Radhiya kuwa da ta fito janyeta akayi za'a cigaba da hotuna jikinta duk babu kwari. Awwab ya kula da yadda tayi zuru-zuru kwalliyar ta goge saboda cabewar da tayi da hawaye sai ta goge kawai shiyasa ganinta haka ya shiga damuwa saboda bata da walwala. Samu yayi ya faki ido saboda yamma da tayi hankalin iyaye yayi nesa dasu ya fitar da ita daga wurin. Rawaninsa ya cire ya nemar musu taxi ko Yousuf bai nema ba suka koma hotel dinsu.
A hanya bai ce mata komai ba sai da suka shiga dakinsu ya rage mata kayan jikinta da danginsu sarkoki da sauran kayan adon ya zaunar da ita a gefen gado sannan ya zauna a kasa a gabanta ya dora kafafunta akan cinyarsa yana matsawa a hankali.
"Me ya sameki Alheran?"
Dama kiris take jira kawai ta fashe masa da kuka. Hankalinsa a tashe ya tashi ya zauna a gefenta ya rungumeta tayi kukan ta gaji. Sai da ya lura numfashinta ya soma dawowa daidai ya sake tambayarta.
Da kyar ta iya fada masa abinda ya riga yaji daga wurin Daada lokacin da suka je Sumaila bayan Salame ta daketa. Sai dai yayi matukar kaduwa game da dalilin makantar Ummi da kuma karshen bayanin Radhiyan wanda shine musabbabin kukanta a yanzu.
"Hammana ka tuna lokacin da aka ce na hakura da kai saboda kada na bata zumunci?"
Ya gyada kai yana tuna lokaci mai daci da ya shude a rayuwarsa. Ya azabtu da rashin cikar burinsa ya kuma ji haushin amincewarta a lokacin taki goya masa baya. Siririyar muryarta da ta dashe saboda kuka ce ta katse shi yaji ta ce,
"It was so painful Chèri sai lokacin ma na fara sonka sosai. Yanzu yaya Emzee zai ji? Yana son Rahima ashe kuma yana gudunta saboda Ummi. Emzeee yana da sa abu a rai nasan da wahala yau ya iya bacci"
Awwab sakin baki yayi yana kallon ikon Allah. Radhiya ta cigaba da fadin halin da kaninta zai shiga cike da tausayawa.
Hade bakin nasa yayi ya ce "yanzu duk wannan hawayen na Emzee ne ba ma Ummi ba?"