Sashe 54
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ko gobe kana iya fadawa Alhaji ya fara shiri anyi masa kwacen mata"
"Ahhh garin yaya labari ya wuceni?" Yace cikin farinciki.
Nan ta labarta masa yadda suka yi da Awwab ranar da ya dawo. Shiru Daddy Haroun yayi har Mummy ta fara tunanin ko zai ce ita ta hada.
Da sanyin jiki tace "Babu hannuna fa a ciki Daddy, wai ashe shiru suka yi 'yar banzar yarinyar nan tace sai ta gama makaranta."
"Abinda ban gane ba shin Awwab din Major kike nufi ko wanne?"
Gambo da saurin fushi ta soma harzuka "Awwab nawa garemu? Idan baka so ne sai inji saboda dan yayata ne kake kinsa ko me"
Ya san halin matarsa da saurin hawa kamar farashi kuma dai daga dawowarsa bai shirya rigima da ita a wannan daren ba.
"Idan Hassana yayarki ce ni kuma ko ban aureki ba kin san dai kanwata ce. Akwai maganar da naji game da Awwab din ne shiyasa kika ga haka amma gobe dama munyi da Major zai zo muyi magana da Alh Baba sai mu fara clearing issue din"
"Wani abu ne ya faru da Awwab din?"
"Kinsa batun matar nan da yaranta da yake ta damuwa dasu iyalin sojan da suka je Liberia tare?"
"Sosai kuwa, Ghazalatu ma har gidan iyayenta taje ta kwana. Shine tafiyar da nace maka sunyi da Mami din"
"Yarinyar wajenta Major yayi min magana akan yana son hadasu da Awwab. Gobe zai zo a gaban su Baba Karami ya gabatar da zancen domin aje ayi magana da iyayensu. Ni da kaina na fara sanar dashi tun a saudiyya"
Ko a jikin Mummy Gambo wannan bayani "rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu ne ya janyo amma tunda yanzu sun fada ai shikenan"
"Idan kuma ya riga ya fadawa iyayen yarinyar fa?"
"Sai aje a basu hakuri. Daddy ba wani abu bane ba fa na tada hankali don Allah."
**********
An wayi gari Major yana shirin tafiya gidan Alh Baba inda zai hadu da nasa mahaifin, baban Mami da ake kira Baban Biyu saboda sune manya a 'ya'yansa don bai sami haihuwa da wuri ba sai da ya auro mahaifiyarsu. Cikon na hudun nasu suna Germany ya rasu kuma bisa umarnin Alh Baba jikokinsa biyu daya na wurin mace dayan kuma na namiji za'a aurawa Zahra da Fauziyya.
Mami ke fada masa tafiyar Awwab din da ya sulale ya gudu Sumaila duk da Major ya fada masa zasu je gidan Alh Baba da ya dawo daren jiya. Dadi yaji har ransa "kice ko yau aka bukaci sadaki na mika kawai. Allah Yayi musu albarka. Sun gama min komai"
Amare Zahra da Fauziyya sun fara gyaran jiki. Wata mata ke yi musu anan cikin gidan. Da Major zai fita sai Zayyana kadai a falo itama zaman jiransa take yi. Hajiyar shagwaba ta rinka marairaice masa wai ya bata kudi Ibrahim yace mata anayin kanwar amarya day jiya da suka yi waya.
Dariya yayi harda kyakyatawa "shi Ibrahim din da kansa ya fada miki haka?"
"Eh Daddy don Allah ka bani kudin yadda za'ayi min nawa invitation card din"
"Kece amaryar?"
"Nice mai gayyata amma kuma bani da outfit da zai dace. Please Daddy"
Hularsa ya cire ya dan sosa gaban kansa. Yanzu idan yace mata ba'ayi da wahala ta yarda. Ta rinka jero masa tambayoyi kenan shi kuma fitar ce a gabansa.
"Jeki ki fadawa Mami kuyi shawara kafin na dawo"
"Thank you Daddy" ta rungume shi tana murna sannan ta wuce sakin Mami.
Daddy Haroun da Gambo ne karshen zuwa falon na Alh Baba. Sun shigo Major yana gaisawa da surukansa Bilal wanda zai auri Fauziyya da Fawaz mai auren Zahra. Su dinma zuwansu kenan yiwa Alhajin barka da dawowa. Suna fita bayan gaishe gaishe tsakanin su Mummy Gambo da iyayensu ta tashi ta koma bangarensu.
Falon akwai 'yan uwansu maza manya wadanda duka tushensu daya ne banda iyayen nasu guda uku. Hira suka taba kadan ana tambayar iyalan juna da dan abinda ba'a rasa ba.
"Mustapha" Alh Baba ya kira Major wanda ya tattaro hankalinsa ga uban nasu "Dan uwanka yayi min zancen akwai yarinya 'yar wajen abokin aikinka da kake son hadawa aure da Muhammad ko?"
"Eh Alhaji"
"Major nace me zai hana mubi abin a sannu kada a takura yaron nan saboda son kara kulla zumunci azo a bata shi"
Daddy Haroun yace saboda yana bukatar damar kawo zancen Ghazalatu.
Murmushi Major yayi "in sha Allahu wannan matsalar ina tsammanin ta riga ta kau. Maganar da nake maka yana hanyar Sumaila zai je wurin yarinyar"
Baba Karami shine mahaifin Major kuma ya fada masa komai kafin ya kawo zancen nan. Murmushi yayi irin na dattijai "to idan sun hada kansu Alh Baba ina ganin ba sai an tsaya bata lokaci ba ko yaya kace?"
"Kwarai kuwa, ya kamata ya ajiye iyali hakan ne zai sa ko ina yaje gida zai nufo ba yawon kasashe ba"
Daddy Haroun sai ya rasa yadda zai bullowa lamarin. Kafin ya fito sai da ya tabbatar da magana daga wurin Ghazalatu. Shirun ba zai zama alkhairi ba kada aje ayi hukuncin da zai jawo matsala a gaba.
"Jiya Gambo take fada min Awwab din da Ghazalatu sun daidaita kansu ashe. Ina ganin me zai hana mu jira ya dawo aji ta bakinsa"
Murmushi sosai Alh Baba yayi yana nuna farincikinsa bisa yadda al'amura suka kasance. Lallai ba karamin kara hade zumunci za'ayi ba idan akayi wannan auren saboda iyayensu duka 'yan dangi ne.
"Wannan shine tuwo na mai na" inji Baban Biyu.
"Kai da baka san da wannan din ba kake kokarin nema masa auren wata?"
Baba Karami ya tambayi Major wanda zancen gabadaya yazo masa a bazata.
"Wallahi ban sani ba Baba"
"Tunda abu yazo da haka Mustapha ita waccan yarinya a barta. Ko bai aureta ba daga ko ina zaka iya tallafawa rayuwarsu. Idan yaso sai ya auri kanwarsa" Baban Biyu yace yana bin 'yan uwansa da kallo domin neman amincewarsu.
Hankalin Major tashi yayi sosai bai taba zaton da faruwar wannan lamari ba. To garin yaya shi bai sani ba kuma Mami ma baya tsammanin ta sani.
"Gambo cewa tayi tana so a hadasu ko sun hada kansu ne? Wallahi ni ban taba jin zancen ba. Babarsu ma bana jin ta sani"
Daddy Haroun sai ya ga tambayar kamar yana nufin kirkira suka yi shi da matarsa sai yaji ransa ya sosu "ba wani abu ne na jayayya ba Major, tunda da alamu kafi son ya auri ita waccan yarinya sai ayi haka din."
Sassauta murya Major yayi duk kuwa da cewa nasa ran har yafi na Daddy Haroun baci "ba zamuyi haka ba, mamaki kawai nake yi nace ban sani ba amma ba wai na karyata bane."
"Duk da haka ya auri wadda ka zaba masa tun farko ita Ghazalatu ayi maganarta daga baya idan ta sami wani"
"To iyayen 'ya'ya. Idan kun gama yanke baku hukuncin sai ku saurari nawa. Mustapha, Haroun, nawa hukuncin shine Muhammad zai auri Ghazalatu. Ita kuma wannan yarinya tunda bamu riga mun shiga ciki ba Allah Ya bata wani. Bazan so wata baraka ta taso a cikinku ba saboda wannan dalili. Hakan yayi ko?" Ya juya ga Baban Biyu da Baba Karami. Duka su biyun sun nuna amincewarsu.
Major bai yi shiru ba duk da haka saboda ance mai daki shi yasan inda yake yi masa yoyo. Shine yasan Zayyan kuma shi yasan me yasa yake kwadayin hada alakar auratayya a tsakanin zuri'arsu. Burinsa su dunkule ta yadda ko bayan ransu a gaba zuri'arsu zata zamo daya. Wannan shine tanadinsa ga Awwab kamar yadda yadda yake da kudirin hada Ibrahim da Zayyanatu.
"Alhaji ku gafarceni ban tari numfashinku ba. Ina neman alfarmar don Allah a bashi damar hadasu duka. Yarinyar da nake magana a kai Radhiya ban baro kakaninnta ba sai da nayi musu alkawarin hadata aure da Awwab"
"MUSTAPHA!!!"
Baba Karami ya daka masa tsawa da kakkausar murya. Duk cikin iyayen nasu ma shine mara fada amma yadda ya kira sunnan dan nasa ya bashi tsoro.
"Alh Baba ya yanke hukunci, mu mun amince sai kaine da ka haifi Muhammadu kake son nuna mana iyakarmu? Da can wane dalilin ne yasa kayi musu alkawari batare da kayi shawara da kowa cikinmu ba?"
"Ku gafarceni Baba in sha Allahu yadda kuka ce hakan za'ayi. Zanje na basu hakuri."
Babu abinda Daddy Haroun bai sani ba game da labarin dan uwan nasa shiyasa yaji tausayinsa da yace ya riga ya fadawa iyayenta. Ai da kunya ace kuma ya koma yace musu an fasa "Baba don Allah kuyi hakuri kada maganar nan ta janyo rikici. A bar Awwab ya auri yarinyar. Ghazalatu kuma ko cikin 'yan uwa sai a sama mata wani"
"Ka bar wannan magana Haroun in sha Allahu Ghazalatu zai aura. Zanje nayi musu bayani"
Alh Baba ma nasa ran ya soma baci yace "nace na gama magana kuma nan da wata uku za'ayi auren. Idan ya dawo ka turo min shi. Ku tashi ku tafi kuma kada ku yarda maganar nan ta kai kunnen iyalanku. Biki ne dasu ku barsu su gama a nutse bana son kananan maganganu"
Sun fito Major ya rasa abinda yake yi masa dadi. Daddy Haroun yana son farincikin 'yarsa ta wani bangaren yana duba cikin tsakar da dan uwansa zai shiga. Jikin motar Major suka tsaya drebansa ya taso da sauri Daddy yayi masa alama da ya basu wuri.
"Major ka bani lokaci zanyi magana da su Alhaji. Babu girma ka koma ka cewa mutanen nan an fasa ko abu makamancin haka"
Murmushi yayi kansa ya kulle yana neman mafita "ka bar maganar, nine nayi abu bisa rashin sani dama saboda haka zanyi kokarin daidaitawa. Tunda sun hada kansu da kanwarsa bamubda dalilin cewa wani ya hakura" yayi maganar da tunanin cewa idan da gaske hasashen Mami akansa da Radhiya gaske ne ita za'a ce ta hakura kenan saboda ita ba danginsu bace? Kuma da kunya matuka ya kalli idon Daddy yace tasa 'yar ta hakura.
"Mafi dacewa Major ya auri su biyun. Ka sa min ido zan sake magana dasu."
"Ahhh garin yaya labari ya wuceni?" Yace cikin farinciki.
Nan ta labarta masa yadda suka yi da Awwab ranar da ya dawo. Shiru Daddy Haroun yayi har Mummy ta fara tunanin ko zai ce ita ta hada.
Da sanyin jiki tace "Babu hannuna fa a ciki Daddy, wai ashe shiru suka yi 'yar banzar yarinyar nan tace sai ta gama makaranta."
"Abinda ban gane ba shin Awwab din Major kike nufi ko wanne?"
Gambo da saurin fushi ta soma harzuka "Awwab nawa garemu? Idan baka so ne sai inji saboda dan yayata ne kake kinsa ko me"
Ya san halin matarsa da saurin hawa kamar farashi kuma dai daga dawowarsa bai shirya rigima da ita a wannan daren ba.
"Idan Hassana yayarki ce ni kuma ko ban aureki ba kin san dai kanwata ce. Akwai maganar da naji game da Awwab din ne shiyasa kika ga haka amma gobe dama munyi da Major zai zo muyi magana da Alh Baba sai mu fara clearing issue din"
"Wani abu ne ya faru da Awwab din?"
"Kinsa batun matar nan da yaranta da yake ta damuwa dasu iyalin sojan da suka je Liberia tare?"
"Sosai kuwa, Ghazalatu ma har gidan iyayenta taje ta kwana. Shine tafiyar da nace maka sunyi da Mami din"
"Yarinyar wajenta Major yayi min magana akan yana son hadasu da Awwab. Gobe zai zo a gaban su Baba Karami ya gabatar da zancen domin aje ayi magana da iyayensu. Ni da kaina na fara sanar dashi tun a saudiyya"
Ko a jikin Mummy Gambo wannan bayani "rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu ne ya janyo amma tunda yanzu sun fada ai shikenan"
"Idan kuma ya riga ya fadawa iyayen yarinyar fa?"
"Sai aje a basu hakuri. Daddy ba wani abu bane ba fa na tada hankali don Allah."
**********
An wayi gari Major yana shirin tafiya gidan Alh Baba inda zai hadu da nasa mahaifin, baban Mami da ake kira Baban Biyu saboda sune manya a 'ya'yansa don bai sami haihuwa da wuri ba sai da ya auro mahaifiyarsu. Cikon na hudun nasu suna Germany ya rasu kuma bisa umarnin Alh Baba jikokinsa biyu daya na wurin mace dayan kuma na namiji za'a aurawa Zahra da Fauziyya.
Mami ke fada masa tafiyar Awwab din da ya sulale ya gudu Sumaila duk da Major ya fada masa zasu je gidan Alh Baba da ya dawo daren jiya. Dadi yaji har ransa "kice ko yau aka bukaci sadaki na mika kawai. Allah Yayi musu albarka. Sun gama min komai"
Amare Zahra da Fauziyya sun fara gyaran jiki. Wata mata ke yi musu anan cikin gidan. Da Major zai fita sai Zayyana kadai a falo itama zaman jiransa take yi. Hajiyar shagwaba ta rinka marairaice masa wai ya bata kudi Ibrahim yace mata anayin kanwar amarya day jiya da suka yi waya.
Dariya yayi harda kyakyatawa "shi Ibrahim din da kansa ya fada miki haka?"
"Eh Daddy don Allah ka bani kudin yadda za'ayi min nawa invitation card din"
"Kece amaryar?"
"Nice mai gayyata amma kuma bani da outfit da zai dace. Please Daddy"
Hularsa ya cire ya dan sosa gaban kansa. Yanzu idan yace mata ba'ayi da wahala ta yarda. Ta rinka jero masa tambayoyi kenan shi kuma fitar ce a gabansa.
"Jeki ki fadawa Mami kuyi shawara kafin na dawo"
"Thank you Daddy" ta rungume shi tana murna sannan ta wuce sakin Mami.
Daddy Haroun da Gambo ne karshen zuwa falon na Alh Baba. Sun shigo Major yana gaisawa da surukansa Bilal wanda zai auri Fauziyya da Fawaz mai auren Zahra. Su dinma zuwansu kenan yiwa Alhajin barka da dawowa. Suna fita bayan gaishe gaishe tsakanin su Mummy Gambo da iyayensu ta tashi ta koma bangarensu.
Falon akwai 'yan uwansu maza manya wadanda duka tushensu daya ne banda iyayen nasu guda uku. Hira suka taba kadan ana tambayar iyalan juna da dan abinda ba'a rasa ba.
"Mustapha" Alh Baba ya kira Major wanda ya tattaro hankalinsa ga uban nasu "Dan uwanka yayi min zancen akwai yarinya 'yar wajen abokin aikinka da kake son hadawa aure da Muhammad ko?"
"Eh Alhaji"
"Major nace me zai hana mubi abin a sannu kada a takura yaron nan saboda son kara kulla zumunci azo a bata shi"
Daddy Haroun yace saboda yana bukatar damar kawo zancen Ghazalatu.
Murmushi Major yayi "in sha Allahu wannan matsalar ina tsammanin ta riga ta kau. Maganar da nake maka yana hanyar Sumaila zai je wurin yarinyar"
Baba Karami shine mahaifin Major kuma ya fada masa komai kafin ya kawo zancen nan. Murmushi yayi irin na dattijai "to idan sun hada kansu Alh Baba ina ganin ba sai an tsaya bata lokaci ba ko yaya kace?"
"Kwarai kuwa, ya kamata ya ajiye iyali hakan ne zai sa ko ina yaje gida zai nufo ba yawon kasashe ba"
Daddy Haroun sai ya rasa yadda zai bullowa lamarin. Kafin ya fito sai da ya tabbatar da magana daga wurin Ghazalatu. Shirun ba zai zama alkhairi ba kada aje ayi hukuncin da zai jawo matsala a gaba.
"Jiya Gambo take fada min Awwab din da Ghazalatu sun daidaita kansu ashe. Ina ganin me zai hana mu jira ya dawo aji ta bakinsa"
Murmushi sosai Alh Baba yayi yana nuna farincikinsa bisa yadda al'amura suka kasance. Lallai ba karamin kara hade zumunci za'ayi ba idan akayi wannan auren saboda iyayensu duka 'yan dangi ne.
"Wannan shine tuwo na mai na" inji Baban Biyu.
"Kai da baka san da wannan din ba kake kokarin nema masa auren wata?"
Baba Karami ya tambayi Major wanda zancen gabadaya yazo masa a bazata.
"Wallahi ban sani ba Baba"
"Tunda abu yazo da haka Mustapha ita waccan yarinya a barta. Ko bai aureta ba daga ko ina zaka iya tallafawa rayuwarsu. Idan yaso sai ya auri kanwarsa" Baban Biyu yace yana bin 'yan uwansa da kallo domin neman amincewarsu.
Hankalin Major tashi yayi sosai bai taba zaton da faruwar wannan lamari ba. To garin yaya shi bai sani ba kuma Mami ma baya tsammanin ta sani.
"Gambo cewa tayi tana so a hadasu ko sun hada kansu ne? Wallahi ni ban taba jin zancen ba. Babarsu ma bana jin ta sani"
Daddy Haroun sai ya ga tambayar kamar yana nufin kirkira suka yi shi da matarsa sai yaji ransa ya sosu "ba wani abu ne na jayayya ba Major, tunda da alamu kafi son ya auri ita waccan yarinya sai ayi haka din."
Sassauta murya Major yayi duk kuwa da cewa nasa ran har yafi na Daddy Haroun baci "ba zamuyi haka ba, mamaki kawai nake yi nace ban sani ba amma ba wai na karyata bane."
"Duk da haka ya auri wadda ka zaba masa tun farko ita Ghazalatu ayi maganarta daga baya idan ta sami wani"
"To iyayen 'ya'ya. Idan kun gama yanke baku hukuncin sai ku saurari nawa. Mustapha, Haroun, nawa hukuncin shine Muhammad zai auri Ghazalatu. Ita kuma wannan yarinya tunda bamu riga mun shiga ciki ba Allah Ya bata wani. Bazan so wata baraka ta taso a cikinku ba saboda wannan dalili. Hakan yayi ko?" Ya juya ga Baban Biyu da Baba Karami. Duka su biyun sun nuna amincewarsu.
Major bai yi shiru ba duk da haka saboda ance mai daki shi yasan inda yake yi masa yoyo. Shine yasan Zayyan kuma shi yasan me yasa yake kwadayin hada alakar auratayya a tsakanin zuri'arsu. Burinsa su dunkule ta yadda ko bayan ransu a gaba zuri'arsu zata zamo daya. Wannan shine tanadinsa ga Awwab kamar yadda yadda yake da kudirin hada Ibrahim da Zayyanatu.
"Alhaji ku gafarceni ban tari numfashinku ba. Ina neman alfarmar don Allah a bashi damar hadasu duka. Yarinyar da nake magana a kai Radhiya ban baro kakaninnta ba sai da nayi musu alkawarin hadata aure da Awwab"
"MUSTAPHA!!!"
Baba Karami ya daka masa tsawa da kakkausar murya. Duk cikin iyayen nasu ma shine mara fada amma yadda ya kira sunnan dan nasa ya bashi tsoro.
"Alh Baba ya yanke hukunci, mu mun amince sai kaine da ka haifi Muhammadu kake son nuna mana iyakarmu? Da can wane dalilin ne yasa kayi musu alkawari batare da kayi shawara da kowa cikinmu ba?"
"Ku gafarceni Baba in sha Allahu yadda kuka ce hakan za'ayi. Zanje na basu hakuri."
Babu abinda Daddy Haroun bai sani ba game da labarin dan uwan nasa shiyasa yaji tausayinsa da yace ya riga ya fadawa iyayenta. Ai da kunya ace kuma ya koma yace musu an fasa "Baba don Allah kuyi hakuri kada maganar nan ta janyo rikici. A bar Awwab ya auri yarinyar. Ghazalatu kuma ko cikin 'yan uwa sai a sama mata wani"
"Ka bar wannan magana Haroun in sha Allahu Ghazalatu zai aura. Zanje nayi musu bayani"
Alh Baba ma nasa ran ya soma baci yace "nace na gama magana kuma nan da wata uku za'ayi auren. Idan ya dawo ka turo min shi. Ku tashi ku tafi kuma kada ku yarda maganar nan ta kai kunnen iyalanku. Biki ne dasu ku barsu su gama a nutse bana son kananan maganganu"
Sun fito Major ya rasa abinda yake yi masa dadi. Daddy Haroun yana son farincikin 'yarsa ta wani bangaren yana duba cikin tsakar da dan uwansa zai shiga. Jikin motar Major suka tsaya drebansa ya taso da sauri Daddy yayi masa alama da ya basu wuri.
"Major ka bani lokaci zanyi magana da su Alhaji. Babu girma ka koma ka cewa mutanen nan an fasa ko abu makamancin haka"
Murmushi yayi kansa ya kulle yana neman mafita "ka bar maganar, nine nayi abu bisa rashin sani dama saboda haka zanyi kokarin daidaitawa. Tunda sun hada kansu da kanwarsa bamubda dalilin cewa wani ya hakura" yayi maganar da tunanin cewa idan da gaske hasashen Mami akansa da Radhiya gaske ne ita za'a ce ta hakura kenan saboda ita ba danginsu bace? Kuma da kunya matuka ya kalli idon Daddy yace tasa 'yar ta hakura.
"Mafi dacewa Major ya auri su biyun. Ka sa min ido zan sake magana dasu."