Sashe 110
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Karasa min shi zaka yi?" Ummi tace suka sa dariya.
"Yau daya dai nima inyi shagwaba irinta Adda" Emzee ya zagaya bayan babansa ya sako hannuwansa suka zagaye wuyan baban.
"Anya Zayyan ba zamu jira idan matarka ta haihu nayi goyon ba..na jika ne kamar buhun siminti" Zayyan yace yana riko hannuwan nasa da suke wurin wuyansa.
Ummi ta yi gaba kuwa "Ah to ku bari na tafi don kada ma na dorar"
Emzee zai sake shi kenan ashe Zayyan shammatarsa yayi sai ji yayi ya raba kafafunsa da kasa ya zagaye falon dashi. Kunya sosai ta kama Emzee sai gashi zai gudu daga falon Zayyan ya janyoshi ya rungume.
"Allah Yayi muku albarka"
"Amin Daada" ya amsa da 'yar kwallarsa. Kasa yayi da gudu Zayyan ya kife akan kujera.
"Fillo yau fa sai kinyi min tausa"
"Kai da kake jin goyo nima bari nazo na hau"
Wani kallo yayi mata kasa-kasa ta tashi tayi gaba da sauri. Har yanzu tana jin kunyar mijin nata da baya rabo da tsokana kamar ba babba ba.
***********
Kwana biyun nan Radhiya bata komai sai bacci. Ita bata san ma ashe basa samun hutu ba sai da ta dawo gida. A rana ta biyu sai ga Yousuf ya iso. Yayi wani fes dashi aka fara tsokanarsa ya kusa zama ango saboda yadda Babban Arifah ya matsu da tayi aure bai ga dalilin jira ba. To shima baban Yousuf din ya matsu nasa tilon dan yayi aure shiyasa tun a waya su ka gama daidaitawa da Excellency. Abu ne na manya kuma kowa yana ji da nasa.
Da yamma Emzee ya kaishi gidansu Arifah yace to ya nemi mai dawo dashi don yasan yau din ta dabance a wurinsu. Shi kuwa gobe zai koma Kaduna makaranta yana da abubuwan yi. Yana komawa gida an kawo copy na farko na aikin su Radhiya. Sakawa akayi a falon Daada, Ummi, Bigman da Camera man da uwar gayya. Taken National Anthem aka fara kafin nuna mutane a garuruwa daban daban na kasar da muryar Radhiya tana bada takaitaccen uwa ma bada mama Nigeria uwar 'ya'ya da yawa.
Daga nan fa aka shiga shirin sosai. Komai yayi tamkar kana kallon film da aka bata lokaci wurin kawata shi. Abin ya kayatar da Zayyan matuka. Mai camera dai Excellency ya sallame shi amma duk da haka Zayyan yayi ihsani sosai. Bigman kuwa cewa yayi rabin kudin zai karba saboda shi kiransa kawai da akayi ya bude masa ido da abubuwan da bai taba tunaninsu ba bare ya damu. Hasali ma dai bai dauki soja da wata daraja ba da ta wuce idan ya gansu suna checking a hanyoyi ya zagesu sama da kasa ya wuce abinsa. Alfarmar da yake roko shine idan wannan shiri zai cigaba don Allah yana son zama daraktansa kada su nemi wani. Inda baiyi musu ba sai a fada masa ya gyara shima yanzu yake wayewa da aikin. Su Ummi sunji dadi nan take Radhiya ta turawa Supervisor dinta sannan ta kara da doguwar wasika game da zato da suka yi mahaifinta soja ya rasu da dawowarsa. Cikin minti talatin matar ta kirata a waya ta tayata murna kuma ta yaba matuka da aikin na awa guda da aka yi a Nigeria. Sunyi mamakin saurinta tunda wata biyar aka bata. Basu san dan Nigeria da dagewa bane.
***********
Bayan kwana biyu Radhiya tana ta rubutu ta saka computer a gaba tana hada report akan project dinta a daki. Sanye take da dogon wando da rigar sanyi tayi parking gashinta a tsakiya ba a nutse ba wani ya zazzaro ta gefe da bayan. Ummi ce ta shigo da plate din fruits da ta yanka ta mika mata.
Fuskarta a sake take tace "Gashi 'yar gatan Daada kun maidani 'yar aiki ko" sai dai har ranta Alheran tana burgeta. Waye zaice yarinyar za ta nutsu haka har ta bawa karatu mahimmanci.
"Ummina yi hakuri so nake na gama ne kafin jibin da zamu tafi Sumaila"
"Wasa nake yi miki. Nima ina so inga kina kokari ai." Leka aikin tayi ta dan karanta wasu layuka ta koma ta zauna akan gado "kin kusa gamawa ne?"
"Inzo?" Ta tambaya don tasan kila akwai abinda Ummin take son cewa.
Kujerar gaban working table din ta juya zuwa bangaren Ummi tana fuskantarta.
Murmushi Mairama tayi kafin ta soma magana a nutse "Alheran maganar aurenki da Awwab ce ta taso"
Gabanta taji ya buga da ta tuna wancan karon yadda abubuwa suka kasance. Umminta ta kula sai ta kwantar mata da hankali.
"Wancan karon na rabaku ne domin samar da maslaha. Yanzu kuwa sai inda karfina ya kare babu mai rabaki da Awwab sai Allah"
Kunya ta kama Radhiya saboda Ummi bata saba yi mata magana haka ba. Dauke kai tayi kamar bata kula da 'yar ta ta ba ta cigaba da magana.
"Nasara ta fada min cewa idan iyaye maza sun zo jibi akan maganar Arifah da Yousuf zasu roki alfarmar ayi auren karshen watan nan saboda basa son a ja lokaci kuma a ganinsu sauki nw tunda zasu zo taron baban naku dama. To shima maigidan nata ya fadawa Daada shine Daddy dinku ya yanke shawarar idan anyi finalizing maganar a haka to za'a daura auren Arifah ranar asabar ke kuma lahadi domin kawo sauki. Zai kama 27th da 28th December. Biki sai bayan sati biyu lokacin kinga an gama taron karrama Daada sannan munyi namu"
Ai jikin Radhiya sai yayi sanyi da ta gama lissafi a kanta kwanakin basu fi sha wani abu ba. Nutsuwarta ta nema ta rasa duk ta wani firgice.
Hawaye ta soma "Shikenan ni daga dawowar Daada sai aure"
"Ki godewa Allah da yanzu haka za'a aurar dake mahaifinki yana kasa"
Kuka ta fashe dashi sosai Ummi tace ko tayi shiru ko ta kira Awwab tace masa ya nemi wata ita ta fasa. Da saurinta ta dago kai sai taji kunya.
"Ki kwantar da hankalinki na yarda da Awwab kuma kema kin sani zuri'ar su Mami sunfi karfin komai wurinmu. Sannan ki zama cikin shiri daga Sumaila wurin Innawuro zaki zauna sai ana kwana uku daurin aure tace gyara zata yi miki. Mun riga munje da Daada da kina can aiki"
Tashi Radhiya tayi ta dare gadonta da tsalle "ni ko gadon ban mora ba Ummi zaku koreni"
"Sai ki zauna morar gado sarkin shirme"
Bayan kwana biyu suka tafi Sumaila ita da Ummi taron da Malamijo ya shirya. Emzee ya riga ya koma makaranta bazai fito ba sai gab da taron da za'ayi. Washegarin zuwansu sauran 'ya'yansa kowa ya gama zuwa. Su Habu da Bature sun ajiye iyali shima Ayuba saura watanni kadan bikinsa.
Tun dare aka fara soye soyen nama da kayan miya kai kace biki ne za'ayi washegari. Yara da manya abin ya zame musu sabo amma kowa murna yake yi. Shadaya na safe washegari kowa da kowa ya hallara a katuwar tsakar gidan da aka saka mata rumfa da tabarmi. Kujera daya ce a tsakiya Malamijo ya hakimce abinsa bayan an bude taro da addu'a yace kowa ya tashi ya gabatar da kansa masu 'ya'ya kana gama fadin naka yaranka su fadi nasu.
Salame ce ta fara tashi tana ta hura hanci tasha leshi mai kyau amma fa ita daban shima daban. Yadda ta matsawa Halifa lamba cewa tayi idan ya bari aka ganta a wulakance to kansa ya wulakanta. Cikin shagunan mahaifinsa yaje ya siyo mata mai kyau kuwa bai tsaya kanta ba ya siyowa duka yaranta sannan ya bawa Hibbah na Rahima yace ta kai dinki amma kada ya kai girmanta. Har kofar gida ya kai mata sai taji dadin zuwan nasa fiye da kayan. Ciki ta kaishi wurin kakarta ta kasa boye farincikinta tana ta cewa ga yayanta na Kano. Babanta ya saya mata mayafi mai kyau daidai aljihunsa da ya dace da kayan sai gata tayi wani irin kyau kakarta tayi ta wasa ta kafin ta fito. Da ta iso gidan a cike daya daga cikin kannenta ta gani ta tambayesu ina Ummansu yarinyar a tsiwace tace mata ta duba mana ko ta bata ajiya ne. Ajiyar zuciya tayi ta rinka dubawa ta ganota a can gefe taki sakarwa 'yan uwanta jiki. Yawan mutane yasa ta zauna a kusa da wata mai kama da larabawa sai wani irin kamshi take yi tayi kyau cikin jar atampa super.
Radhiya ta dukufa yiwa Awwab text bata kula da ita ba sai ta taji Salame tana fadin sunanta ta ajiye wayar a cinyarta ta koma saurarenta.
"Sunana Salame kamar yadda kuka sani kuma mijina Alhaji ne don ya sauke farali tun kafin wasu su fara rike naira"
Rahima cusa kanta tayi a cinyarta saboda kunya Halifa yaji kamar yayi tsuntsu ya bar wurin.
"Babban dana ma da babansa duka alhazawan ne yayi karatu a kasar Misira ne ko ...." neman Halifa ta rinka yi da ido ya dukar da kai.
"Zauna haka Salame bari yaran suyi da kansu za'afi gane juna" Hajjo ta dakatar da ita. Malamijo ya samu ta dawo bayan ta gama fushin yanzu sannu a hankali yake binta.
"Halifa sunana a Kano muke da zama"
Salame tayi caraf ta amshe "waye zai ganeka a haka? Ka fada musu sunan babanka Alh Salisun kwari wanda kowa yake gani a talabijin"
Duk da ita ta haifeshi ko kadan baiji dadi ba dama ga kadaicin rashin zuwan Emzee saboda makaranta. Yana zama Rahima ta mike a kunyace. Ita bata san mutanen gidan sosai ba Radhiya kuwa ta bita da kallo.
"Sunana Rahima Usman" ta kara da sunan mahaifinta a zatonta haka ya kamata tayi tunda taji an yiwa Halifa fada.
"Kin manta baki ce musu me buga iska a titin...."
"SALAME!!!" Malamijo yayi mata wata irin tsawa da shi kanshi baya jin ya taba daga murya irin haka. Wata irin dabi'a ya karance ta da ita yanzun nan. 'Ya'yan da ta haifa da masu kudi sune mutane Rahima kuma bata da amfani. Da girmanta ta janyo wa kanta zubewar mutumci a gaban kannenta da 'ya'ya.
Ummi sai tayi saurin mikewa domin katse shirun da ya ratsa wurin ana ta kallon Salame.
"Sunana Mairama daga Adda Salame sai ni"
"Yau daya dai nima inyi shagwaba irinta Adda" Emzee ya zagaya bayan babansa ya sako hannuwansa suka zagaye wuyan baban.
"Anya Zayyan ba zamu jira idan matarka ta haihu nayi goyon ba..na jika ne kamar buhun siminti" Zayyan yace yana riko hannuwan nasa da suke wurin wuyansa.
Ummi ta yi gaba kuwa "Ah to ku bari na tafi don kada ma na dorar"
Emzee zai sake shi kenan ashe Zayyan shammatarsa yayi sai ji yayi ya raba kafafunsa da kasa ya zagaye falon dashi. Kunya sosai ta kama Emzee sai gashi zai gudu daga falon Zayyan ya janyoshi ya rungume.
"Allah Yayi muku albarka"
"Amin Daada" ya amsa da 'yar kwallarsa. Kasa yayi da gudu Zayyan ya kife akan kujera.
"Fillo yau fa sai kinyi min tausa"
"Kai da kake jin goyo nima bari nazo na hau"
Wani kallo yayi mata kasa-kasa ta tashi tayi gaba da sauri. Har yanzu tana jin kunyar mijin nata da baya rabo da tsokana kamar ba babba ba.
***********
Kwana biyun nan Radhiya bata komai sai bacci. Ita bata san ma ashe basa samun hutu ba sai da ta dawo gida. A rana ta biyu sai ga Yousuf ya iso. Yayi wani fes dashi aka fara tsokanarsa ya kusa zama ango saboda yadda Babban Arifah ya matsu da tayi aure bai ga dalilin jira ba. To shima baban Yousuf din ya matsu nasa tilon dan yayi aure shiyasa tun a waya su ka gama daidaitawa da Excellency. Abu ne na manya kuma kowa yana ji da nasa.
Da yamma Emzee ya kaishi gidansu Arifah yace to ya nemi mai dawo dashi don yasan yau din ta dabance a wurinsu. Shi kuwa gobe zai koma Kaduna makaranta yana da abubuwan yi. Yana komawa gida an kawo copy na farko na aikin su Radhiya. Sakawa akayi a falon Daada, Ummi, Bigman da Camera man da uwar gayya. Taken National Anthem aka fara kafin nuna mutane a garuruwa daban daban na kasar da muryar Radhiya tana bada takaitaccen uwa ma bada mama Nigeria uwar 'ya'ya da yawa.
Daga nan fa aka shiga shirin sosai. Komai yayi tamkar kana kallon film da aka bata lokaci wurin kawata shi. Abin ya kayatar da Zayyan matuka. Mai camera dai Excellency ya sallame shi amma duk da haka Zayyan yayi ihsani sosai. Bigman kuwa cewa yayi rabin kudin zai karba saboda shi kiransa kawai da akayi ya bude masa ido da abubuwan da bai taba tunaninsu ba bare ya damu. Hasali ma dai bai dauki soja da wata daraja ba da ta wuce idan ya gansu suna checking a hanyoyi ya zagesu sama da kasa ya wuce abinsa. Alfarmar da yake roko shine idan wannan shiri zai cigaba don Allah yana son zama daraktansa kada su nemi wani. Inda baiyi musu ba sai a fada masa ya gyara shima yanzu yake wayewa da aikin. Su Ummi sunji dadi nan take Radhiya ta turawa Supervisor dinta sannan ta kara da doguwar wasika game da zato da suka yi mahaifinta soja ya rasu da dawowarsa. Cikin minti talatin matar ta kirata a waya ta tayata murna kuma ta yaba matuka da aikin na awa guda da aka yi a Nigeria. Sunyi mamakin saurinta tunda wata biyar aka bata. Basu san dan Nigeria da dagewa bane.
***********
Bayan kwana biyu Radhiya tana ta rubutu ta saka computer a gaba tana hada report akan project dinta a daki. Sanye take da dogon wando da rigar sanyi tayi parking gashinta a tsakiya ba a nutse ba wani ya zazzaro ta gefe da bayan. Ummi ce ta shigo da plate din fruits da ta yanka ta mika mata.
Fuskarta a sake take tace "Gashi 'yar gatan Daada kun maidani 'yar aiki ko" sai dai har ranta Alheran tana burgeta. Waye zaice yarinyar za ta nutsu haka har ta bawa karatu mahimmanci.
"Ummina yi hakuri so nake na gama ne kafin jibin da zamu tafi Sumaila"
"Wasa nake yi miki. Nima ina so inga kina kokari ai." Leka aikin tayi ta dan karanta wasu layuka ta koma ta zauna akan gado "kin kusa gamawa ne?"
"Inzo?" Ta tambaya don tasan kila akwai abinda Ummin take son cewa.
Kujerar gaban working table din ta juya zuwa bangaren Ummi tana fuskantarta.
Murmushi Mairama tayi kafin ta soma magana a nutse "Alheran maganar aurenki da Awwab ce ta taso"
Gabanta taji ya buga da ta tuna wancan karon yadda abubuwa suka kasance. Umminta ta kula sai ta kwantar mata da hankali.
"Wancan karon na rabaku ne domin samar da maslaha. Yanzu kuwa sai inda karfina ya kare babu mai rabaki da Awwab sai Allah"
Kunya ta kama Radhiya saboda Ummi bata saba yi mata magana haka ba. Dauke kai tayi kamar bata kula da 'yar ta ta ba ta cigaba da magana.
"Nasara ta fada min cewa idan iyaye maza sun zo jibi akan maganar Arifah da Yousuf zasu roki alfarmar ayi auren karshen watan nan saboda basa son a ja lokaci kuma a ganinsu sauki nw tunda zasu zo taron baban naku dama. To shima maigidan nata ya fadawa Daada shine Daddy dinku ya yanke shawarar idan anyi finalizing maganar a haka to za'a daura auren Arifah ranar asabar ke kuma lahadi domin kawo sauki. Zai kama 27th da 28th December. Biki sai bayan sati biyu lokacin kinga an gama taron karrama Daada sannan munyi namu"
Ai jikin Radhiya sai yayi sanyi da ta gama lissafi a kanta kwanakin basu fi sha wani abu ba. Nutsuwarta ta nema ta rasa duk ta wani firgice.
Hawaye ta soma "Shikenan ni daga dawowar Daada sai aure"
"Ki godewa Allah da yanzu haka za'a aurar dake mahaifinki yana kasa"
Kuka ta fashe dashi sosai Ummi tace ko tayi shiru ko ta kira Awwab tace masa ya nemi wata ita ta fasa. Da saurinta ta dago kai sai taji kunya.
"Ki kwantar da hankalinki na yarda da Awwab kuma kema kin sani zuri'ar su Mami sunfi karfin komai wurinmu. Sannan ki zama cikin shiri daga Sumaila wurin Innawuro zaki zauna sai ana kwana uku daurin aure tace gyara zata yi miki. Mun riga munje da Daada da kina can aiki"
Tashi Radhiya tayi ta dare gadonta da tsalle "ni ko gadon ban mora ba Ummi zaku koreni"
"Sai ki zauna morar gado sarkin shirme"
Bayan kwana biyu suka tafi Sumaila ita da Ummi taron da Malamijo ya shirya. Emzee ya riga ya koma makaranta bazai fito ba sai gab da taron da za'ayi. Washegarin zuwansu sauran 'ya'yansa kowa ya gama zuwa. Su Habu da Bature sun ajiye iyali shima Ayuba saura watanni kadan bikinsa.
Tun dare aka fara soye soyen nama da kayan miya kai kace biki ne za'ayi washegari. Yara da manya abin ya zame musu sabo amma kowa murna yake yi. Shadaya na safe washegari kowa da kowa ya hallara a katuwar tsakar gidan da aka saka mata rumfa da tabarmi. Kujera daya ce a tsakiya Malamijo ya hakimce abinsa bayan an bude taro da addu'a yace kowa ya tashi ya gabatar da kansa masu 'ya'ya kana gama fadin naka yaranka su fadi nasu.
Salame ce ta fara tashi tana ta hura hanci tasha leshi mai kyau amma fa ita daban shima daban. Yadda ta matsawa Halifa lamba cewa tayi idan ya bari aka ganta a wulakance to kansa ya wulakanta. Cikin shagunan mahaifinsa yaje ya siyo mata mai kyau kuwa bai tsaya kanta ba ya siyowa duka yaranta sannan ya bawa Hibbah na Rahima yace ta kai dinki amma kada ya kai girmanta. Har kofar gida ya kai mata sai taji dadin zuwan nasa fiye da kayan. Ciki ta kaishi wurin kakarta ta kasa boye farincikinta tana ta cewa ga yayanta na Kano. Babanta ya saya mata mayafi mai kyau daidai aljihunsa da ya dace da kayan sai gata tayi wani irin kyau kakarta tayi ta wasa ta kafin ta fito. Da ta iso gidan a cike daya daga cikin kannenta ta gani ta tambayesu ina Ummansu yarinyar a tsiwace tace mata ta duba mana ko ta bata ajiya ne. Ajiyar zuciya tayi ta rinka dubawa ta ganota a can gefe taki sakarwa 'yan uwanta jiki. Yawan mutane yasa ta zauna a kusa da wata mai kama da larabawa sai wani irin kamshi take yi tayi kyau cikin jar atampa super.
Radhiya ta dukufa yiwa Awwab text bata kula da ita ba sai ta taji Salame tana fadin sunanta ta ajiye wayar a cinyarta ta koma saurarenta.
"Sunana Salame kamar yadda kuka sani kuma mijina Alhaji ne don ya sauke farali tun kafin wasu su fara rike naira"
Rahima cusa kanta tayi a cinyarta saboda kunya Halifa yaji kamar yayi tsuntsu ya bar wurin.
"Babban dana ma da babansa duka alhazawan ne yayi karatu a kasar Misira ne ko ...." neman Halifa ta rinka yi da ido ya dukar da kai.
"Zauna haka Salame bari yaran suyi da kansu za'afi gane juna" Hajjo ta dakatar da ita. Malamijo ya samu ta dawo bayan ta gama fushin yanzu sannu a hankali yake binta.
"Halifa sunana a Kano muke da zama"
Salame tayi caraf ta amshe "waye zai ganeka a haka? Ka fada musu sunan babanka Alh Salisun kwari wanda kowa yake gani a talabijin"
Duk da ita ta haifeshi ko kadan baiji dadi ba dama ga kadaicin rashin zuwan Emzee saboda makaranta. Yana zama Rahima ta mike a kunyace. Ita bata san mutanen gidan sosai ba Radhiya kuwa ta bita da kallo.
"Sunana Rahima Usman" ta kara da sunan mahaifinta a zatonta haka ya kamata tayi tunda taji an yiwa Halifa fada.
"Kin manta baki ce musu me buga iska a titin...."
"SALAME!!!" Malamijo yayi mata wata irin tsawa da shi kanshi baya jin ya taba daga murya irin haka. Wata irin dabi'a ya karance ta da ita yanzun nan. 'Ya'yan da ta haifa da masu kudi sune mutane Rahima kuma bata da amfani. Da girmanta ta janyo wa kanta zubewar mutumci a gaban kannenta da 'ya'ya.
Ummi sai tayi saurin mikewa domin katse shirun da ya ratsa wurin ana ta kallon Salame.
"Sunana Mairama daga Adda Salame sai ni"