Sashe 95
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dan bata rai tayi "ba cikinku daya ba Halifa, ko zaka so ace wani bare suke roko? Wai kuwa ina dayar nan bana rike sunanta"
"Rahima? Tana can nasu gidan" yace da rashin damuwa.
"Ni kuwa da zaka gyara zumuncinku da ka burgeni. Dube ku duk bamu saba da juna ba haka su Ummi ma. Ita da Gwaggo Salame ban san yaushe suka hadu karshe ba"
"Ke Ummanmu ko gidan Malamijo bata zuwa in fada miki."
Yanayin zumuncin nasu baiyi mata dadi ba. Shi kuma da yake babba a nasu gidan sai taji ya kamata ta bashi shawarar gyara tsakaninsa da kannensa. Ko ba komai yana cikin rufin asiri zai kyautu ya rinka dan taimaka musu. Sunyi nisa suna tattaunawa Awwab ya shigo yaci karo dasu suna dariya hira tayi dadi. Tuni fuskarsa ta chanja ya koma ya kira wayarta. Tana dauka fito kawai yace ta tashi.
A bakin mota ta ganshi ya jingina bayansa ya harde kafafunsa da hannuwa a kirgi.
"Sannu da hira" yace fuska babu fara'a.
"Hira kuma?"
"Ba ita kike yi ba na taso ki"
Duka girarta biyu ta rinka dagewa tana wani juya masa ido da dariya "Chèri kishi kake yi? Oh my, my , my sai naji na koma wata sarauniya"
Sakin baki yayi ya kalleta kafin ya girgiza kai "mutum ma baza'a barshi ya nuna bacin ransa ba"
Kashe masa ido tayi tace "no chance baby" Wani irin kallo ya bita dashi ta tsure "kasan Allah subutar baki ne ba baby zan ce ba"
"Ah kawai kice kin girma. Daga fara saka min sunaye nan gaba ni din zaki dauke"
Kamar tayi masa kuka ta sake cewa fitowa yayi kawai.
"Saboda shine a ranki ko? Kinji me Daada yace dai ki fara hada kayanki"
Dagewa tayi bisa subutar baki ne shi kuma yayo ta zolayarta sai gashi sun koma hirarsu mai dadi.
"Please ni dai bana son yadda yaron nan yake shige miki. Nasan dan uwanki ne bazan rabaku amma ni dai a kula kinji ko. Ina kishinki sosai Schatzi"
"In sha Allah Cheri amma nima fa kada kaje kana yiwa 'yan matan jirgin nan masu dan skirt dariya wallahi. If not za ka ganni a mafarki muna fada"
"Naji...kuma banda zuwa rugar Barkindo ki rinka zuwa hira wurin Dr Zakari. Nasanki da likitoci ba sauki"
Dariya ya bata sosai. Ita sai yanzu ta gane ashe lab attendant ne ba likita ba "ka doke kowa fa ni sai dreba ko ba abin hawa"
Sunyi ta hira kamar kada su rabu don washegari karfe bakwai zai bar gida. Da safe da wuri ta tashi don suyi sallama duk da wayar da suka dade suna yi cikin dare don ma ya dage sai ta kwanta. Bayan tafiyarsa ba jimawa su Zahra su ma suka dauki hanya ita da Raji sai kuma tawagar su Ummi. Gidan sai yayiwa su Mami shiru don ma Fauziyya tana nan amma Ibrahim da Zayyana duk sun bisu. Shi Ibrahim zasu yi kwanaki kadan da Emzee a Sumaila su dawo Kano gidan nasa kakannin.
***********
Tun dare Malamijo yake ya da habaici a cikin gidansa wanda Hajiyayye bata fahimta ba.
"Gobe iwar haka watan tatse rashin mutumcin wasu zai tsaya."
Hajiyayye tana sakace hakori zazzaro masa idanu "me kenan kake nufi"
"Zancen zuci ne ya fito fili. Ko an hana magana ne ban sani ba?"
"Kayi abarka. A dai kula ne kada yawan surutun ya tasar min yara kasan halinsu. Yanzu duk naman da suka ci sai kaji suna neman kari"
Dauriya kawai yake a kai gobe amma yana cikin tashin hankalin rashin sanin ina shanunsa. Yau tun asuba yake gonar. Tsagerin yaron nata da yaje daukan wasu sai ya kasa saboda ganin idonsa da wasu bakin fuskoki dole ya tafi.
"Allah Ya hada fuskokinku da sarkin mayu dai amaryata" Malamijo yace harda hade hannuwa irin na mai addu"a.
Cikin Hajiyayye kuwa ya cure wuri guda a take kamar zata yi zawo "wannan wane irin mugun fata ne Malamijo?"
"Ban gane mugun fata ba. Yanzu kamar ni kinsan dadin da zanji duk ranar da na hadu da Mai Martaba Sarkin Kano Dan Lamido kuwa?"
Rai a bace tace "to meye hadin sarkin Kano da sarkin mayu?"
"Meye ne naga kin soma gumi? Namu sarkin shine sarkin Kano. Ke kuma naku Sarkin mayu. Yadda nake son ganin namu kuma nake kaunarki shine ne nake miki fatan haduwa da naku kema"
"To ba amin ba...kaga ni kudi nake so kamar dubu dari karshen wata yaran nan namu kowanne ana yi masa yanka shi kadai saboda rage karfin maitar"
Allah Yaso shi ba don abinda yaji da kunnuwansa ba da yanzu hankalinsa in yayi dubu ya tashi akan neman kudin. Amma yanzu sai cewa yayi tayi hakuri zai tanadar mata zuwa dare gobe.
Saboda samun wuri harda yi masa tsaki tace "to a hanzarta"
"To ranki ya dade"
Matsawa tayi akan katifar tana nuna masa wuri "taho mu kwanta ni bacci nake ji"
Hadiyar yawu yayi saboda sai yanzu da yake sansano tsira ya kara tabbatar da kazantarta da muguwar rama. Wa ya aike shi kwanciya kusa da ita karshe kasusuwan jikinta suje suyi masa sartse ko su soke shi.
Karfe takwas na safe ya soma kiran Ummi wai yana fata yaran sun taho tace masa tare zasu zo da ita harda Halifan Salame.
"In kin barni na ma manta da sunansa tunda uwarsa bata san mutumcina ba. Wannan yaro ina tsammani kamaninsa ma sun bace min. Kinga sai kun taho dai. A hanzarta do Allah"
Ta gama tabbatarwa lallai babu lafiya gidan nasu. Sun kimtsa kowa ya fito suka yi sallama dasu Mami da Mama.
Emzee da akace ya sako kayan makaranta sai ya sami irin shirt dinnan da ake yi da zane zanen khakin sojoji ya saka akan bakin wando. Radhiya kuma atampa ta saka da mayafi tayi kyau sosai. Umminta kuma wani lace ne dan ubansu mai tsada da kyau ta saka green da orange ta dora orange din mayafi da farin gilashinta tayi kyau sosai Zayyan ji yayi kamar a dage tafiyar ko na awa guda ne ya samu ya yaba mata yadda ya dace. Dadinsa ma mota guda Daddy ya bashi da dreba daga shi sai ita. Motar gidansu Halifa kuma mai wuri uku ce yaran suka duru a ciki.
Abinka da tafiyar sammako da kuma rashin tsaye tsaye a hanya karfe hudu suna cikin garin Sumaila. Shekarun baya ne suka rinka dawowa Zayyan. Zuwansa garin nan na karshe lokacin da Mairama tazo yawon arba'in din Alheran ne. Yanzu gashi Alheran dinsa aure yake shirin yi mata. Bacci ko na minti biyar bai iya yu ba sai kalle kallen chanjin da aka samu. Kafin su karasa gidan Malamijo motar da su Radhiya suke ciki ta tsaya daga bakin wata kwana. Halifa ne ya sauka ya taho wurin motar su Ummi ya leka ta taga.
"Gwaggo Mairama nace bari naje wurin Umma na fada mata kunzo tazo ku gaisa kafin ku wuce Kanon"
Zayyan bai manta da wace Salame a baya ba kuma har yanzu ba wai yana dokin ganinta bane. Ya kula Halifa yaro ne mai nutsuwa daga jiya da suka kwana gashi uwa uba da ga Alh Salisu. Jiyan da Mairama taso sanar dashi cewa sun rabu da baban Halifa saboda kada yayi masa maganarta sharewa kawai yayi.
"Ta san da zuwan naka ne?" Ummi ta tambayeshi.
"Bata da waya amma nasan zata zo ko don ta tayamu murnar dawowar Daada" ya kare da murmushi.
Suna kallo ya gangara daga baya sai ka rantse wani babban Alhaji ne. Girman jikinsa da irin shaddodi da yadikan da yake sakawa suke kara masa cika ido.
Malamijo yau ko kofar gida bai leke ba yana jiraj zuwan bakinsa. Abinci biyu akeyi yanzu a gidan nasa. Nasu Yadikko daban na amarya da iyalinta daban. Kunya tasa bai iya fadawa Yadikko zuwan bakin da bai ma san suna da yawa ba kuma. Ita ranta ya dade Hajiyayye kuma babu dalilin da zaisa ya fada mata. Dirin mota yaji yana kashingide a tsakar gida daga shi sai dogon wando da 'yar shara duk sanyin nan ba ji yake sosai ba ya tashi da sauri kai baka ce tsoho bane mai shekarunsa sam baya jin jikinsa. Silifas dinsa ya saka yana washe bakin nan Hajiyayye ta fito daga kitchen da katuwar cooler shakare da farar shinkafa 'yar gomnati ta dafawa 'ya'ya zasu zo su ci banza.
"Ina kuma zaka je kake wannan saurin? Ga abinci ka jira in dan tsakura maka ladan ganin ido ko"
Bai ma jira masu tare masan sun shigo ba ya dora hannuwa a kugu ya daure fuska "a cikin gidan nawa kike zancen tsakura min abinci? Ashe baki da mutumci ban sani ba. To ki jira in dawo ciki zaki ga yadda zanyi dake mutuniyar banza"
Ta tsorata sosai amma sai ta dake kada tayi saurin nunawa "ni Hajiyayye kake yiwa wannan magana? Ko magagin baccin da ka soma ne bai sakeka ba?"
Kallon banza yayi mata harda su juya idanu yau take sallah fa a wurinsa ya fita a gaggauce. Kiris ya rage ya saki fitsari da ya ga 'ya'yan Hajiyayye ne ashe a akori kura manyan mazan su uku katti dasu tamkar ba daga cikinta suka fito ba. Dirowa suka yi daga bayan motar suka cewa dreban yaje gidan gonar ya jirasu. Zasu ci abinci ne su zo a dauko shanu ko hudu ne idan motar zata dauka. Idanun Malamijo sai suka kawo ruwa ya fara kokawa da kwalla. Samarin suka sauko kai cikin gidan suna muzurai su a dole mayu 'ya'yan mayya. Tsabar wulakanci basu duba tsufansa ba suka ringa bangazar kafadarsa suka shige cikin gidan. Jiki a sanyaye ya juya zai koma sai ga wasu galla gallan motoci guda biyu sun doso gidan.
Ihu ne kawai baiyi ba don tsananin murna ya koma daga soron ya tsaya yana jiransu. Jin kansa yake daidai da kowane maye da yake cikin gidansa.
Emzee da Ibrahim ne suka fara shigowa ya tarbesu cikin nishadi. Sai 'yan mata Hibbah da Zayyana sannan Radhiya ta biyo bayansu.
"Malamijo nawa" tace tana murmushin da ta saba idan zata yi masa tsiya.
"Rahima? Tana can nasu gidan" yace da rashin damuwa.
"Ni kuwa da zaka gyara zumuncinku da ka burgeni. Dube ku duk bamu saba da juna ba haka su Ummi ma. Ita da Gwaggo Salame ban san yaushe suka hadu karshe ba"
"Ke Ummanmu ko gidan Malamijo bata zuwa in fada miki."
Yanayin zumuncin nasu baiyi mata dadi ba. Shi kuma da yake babba a nasu gidan sai taji ya kamata ta bashi shawarar gyara tsakaninsa da kannensa. Ko ba komai yana cikin rufin asiri zai kyautu ya rinka dan taimaka musu. Sunyi nisa suna tattaunawa Awwab ya shigo yaci karo dasu suna dariya hira tayi dadi. Tuni fuskarsa ta chanja ya koma ya kira wayarta. Tana dauka fito kawai yace ta tashi.
A bakin mota ta ganshi ya jingina bayansa ya harde kafafunsa da hannuwa a kirgi.
"Sannu da hira" yace fuska babu fara'a.
"Hira kuma?"
"Ba ita kike yi ba na taso ki"
Duka girarta biyu ta rinka dagewa tana wani juya masa ido da dariya "Chèri kishi kake yi? Oh my, my , my sai naji na koma wata sarauniya"
Sakin baki yayi ya kalleta kafin ya girgiza kai "mutum ma baza'a barshi ya nuna bacin ransa ba"
Kashe masa ido tayi tace "no chance baby" Wani irin kallo ya bita dashi ta tsure "kasan Allah subutar baki ne ba baby zan ce ba"
"Ah kawai kice kin girma. Daga fara saka min sunaye nan gaba ni din zaki dauke"
Kamar tayi masa kuka ta sake cewa fitowa yayi kawai.
"Saboda shine a ranki ko? Kinji me Daada yace dai ki fara hada kayanki"
Dagewa tayi bisa subutar baki ne shi kuma yayo ta zolayarta sai gashi sun koma hirarsu mai dadi.
"Please ni dai bana son yadda yaron nan yake shige miki. Nasan dan uwanki ne bazan rabaku amma ni dai a kula kinji ko. Ina kishinki sosai Schatzi"
"In sha Allah Cheri amma nima fa kada kaje kana yiwa 'yan matan jirgin nan masu dan skirt dariya wallahi. If not za ka ganni a mafarki muna fada"
"Naji...kuma banda zuwa rugar Barkindo ki rinka zuwa hira wurin Dr Zakari. Nasanki da likitoci ba sauki"
Dariya ya bata sosai. Ita sai yanzu ta gane ashe lab attendant ne ba likita ba "ka doke kowa fa ni sai dreba ko ba abin hawa"
Sunyi ta hira kamar kada su rabu don washegari karfe bakwai zai bar gida. Da safe da wuri ta tashi don suyi sallama duk da wayar da suka dade suna yi cikin dare don ma ya dage sai ta kwanta. Bayan tafiyarsa ba jimawa su Zahra su ma suka dauki hanya ita da Raji sai kuma tawagar su Ummi. Gidan sai yayiwa su Mami shiru don ma Fauziyya tana nan amma Ibrahim da Zayyana duk sun bisu. Shi Ibrahim zasu yi kwanaki kadan da Emzee a Sumaila su dawo Kano gidan nasa kakannin.
***********
Tun dare Malamijo yake ya da habaici a cikin gidansa wanda Hajiyayye bata fahimta ba.
"Gobe iwar haka watan tatse rashin mutumcin wasu zai tsaya."
Hajiyayye tana sakace hakori zazzaro masa idanu "me kenan kake nufi"
"Zancen zuci ne ya fito fili. Ko an hana magana ne ban sani ba?"
"Kayi abarka. A dai kula ne kada yawan surutun ya tasar min yara kasan halinsu. Yanzu duk naman da suka ci sai kaji suna neman kari"
Dauriya kawai yake a kai gobe amma yana cikin tashin hankalin rashin sanin ina shanunsa. Yau tun asuba yake gonar. Tsagerin yaron nata da yaje daukan wasu sai ya kasa saboda ganin idonsa da wasu bakin fuskoki dole ya tafi.
"Allah Ya hada fuskokinku da sarkin mayu dai amaryata" Malamijo yace harda hade hannuwa irin na mai addu"a.
Cikin Hajiyayye kuwa ya cure wuri guda a take kamar zata yi zawo "wannan wane irin mugun fata ne Malamijo?"
"Ban gane mugun fata ba. Yanzu kamar ni kinsan dadin da zanji duk ranar da na hadu da Mai Martaba Sarkin Kano Dan Lamido kuwa?"
Rai a bace tace "to meye hadin sarkin Kano da sarkin mayu?"
"Meye ne naga kin soma gumi? Namu sarkin shine sarkin Kano. Ke kuma naku Sarkin mayu. Yadda nake son ganin namu kuma nake kaunarki shine ne nake miki fatan haduwa da naku kema"
"To ba amin ba...kaga ni kudi nake so kamar dubu dari karshen wata yaran nan namu kowanne ana yi masa yanka shi kadai saboda rage karfin maitar"
Allah Yaso shi ba don abinda yaji da kunnuwansa ba da yanzu hankalinsa in yayi dubu ya tashi akan neman kudin. Amma yanzu sai cewa yayi tayi hakuri zai tanadar mata zuwa dare gobe.
Saboda samun wuri harda yi masa tsaki tace "to a hanzarta"
"To ranki ya dade"
Matsawa tayi akan katifar tana nuna masa wuri "taho mu kwanta ni bacci nake ji"
Hadiyar yawu yayi saboda sai yanzu da yake sansano tsira ya kara tabbatar da kazantarta da muguwar rama. Wa ya aike shi kwanciya kusa da ita karshe kasusuwan jikinta suje suyi masa sartse ko su soke shi.
Karfe takwas na safe ya soma kiran Ummi wai yana fata yaran sun taho tace masa tare zasu zo da ita harda Halifan Salame.
"In kin barni na ma manta da sunansa tunda uwarsa bata san mutumcina ba. Wannan yaro ina tsammani kamaninsa ma sun bace min. Kinga sai kun taho dai. A hanzarta do Allah"
Ta gama tabbatarwa lallai babu lafiya gidan nasu. Sun kimtsa kowa ya fito suka yi sallama dasu Mami da Mama.
Emzee da akace ya sako kayan makaranta sai ya sami irin shirt dinnan da ake yi da zane zanen khakin sojoji ya saka akan bakin wando. Radhiya kuma atampa ta saka da mayafi tayi kyau sosai. Umminta kuma wani lace ne dan ubansu mai tsada da kyau ta saka green da orange ta dora orange din mayafi da farin gilashinta tayi kyau sosai Zayyan ji yayi kamar a dage tafiyar ko na awa guda ne ya samu ya yaba mata yadda ya dace. Dadinsa ma mota guda Daddy ya bashi da dreba daga shi sai ita. Motar gidansu Halifa kuma mai wuri uku ce yaran suka duru a ciki.
Abinka da tafiyar sammako da kuma rashin tsaye tsaye a hanya karfe hudu suna cikin garin Sumaila. Shekarun baya ne suka rinka dawowa Zayyan. Zuwansa garin nan na karshe lokacin da Mairama tazo yawon arba'in din Alheran ne. Yanzu gashi Alheran dinsa aure yake shirin yi mata. Bacci ko na minti biyar bai iya yu ba sai kalle kallen chanjin da aka samu. Kafin su karasa gidan Malamijo motar da su Radhiya suke ciki ta tsaya daga bakin wata kwana. Halifa ne ya sauka ya taho wurin motar su Ummi ya leka ta taga.
"Gwaggo Mairama nace bari naje wurin Umma na fada mata kunzo tazo ku gaisa kafin ku wuce Kanon"
Zayyan bai manta da wace Salame a baya ba kuma har yanzu ba wai yana dokin ganinta bane. Ya kula Halifa yaro ne mai nutsuwa daga jiya da suka kwana gashi uwa uba da ga Alh Salisu. Jiyan da Mairama taso sanar dashi cewa sun rabu da baban Halifa saboda kada yayi masa maganarta sharewa kawai yayi.
"Ta san da zuwan naka ne?" Ummi ta tambayeshi.
"Bata da waya amma nasan zata zo ko don ta tayamu murnar dawowar Daada" ya kare da murmushi.
Suna kallo ya gangara daga baya sai ka rantse wani babban Alhaji ne. Girman jikinsa da irin shaddodi da yadikan da yake sakawa suke kara masa cika ido.
Malamijo yau ko kofar gida bai leke ba yana jiraj zuwan bakinsa. Abinci biyu akeyi yanzu a gidan nasa. Nasu Yadikko daban na amarya da iyalinta daban. Kunya tasa bai iya fadawa Yadikko zuwan bakin da bai ma san suna da yawa ba kuma. Ita ranta ya dade Hajiyayye kuma babu dalilin da zaisa ya fada mata. Dirin mota yaji yana kashingide a tsakar gida daga shi sai dogon wando da 'yar shara duk sanyin nan ba ji yake sosai ba ya tashi da sauri kai baka ce tsoho bane mai shekarunsa sam baya jin jikinsa. Silifas dinsa ya saka yana washe bakin nan Hajiyayye ta fito daga kitchen da katuwar cooler shakare da farar shinkafa 'yar gomnati ta dafawa 'ya'ya zasu zo su ci banza.
"Ina kuma zaka je kake wannan saurin? Ga abinci ka jira in dan tsakura maka ladan ganin ido ko"
Bai ma jira masu tare masan sun shigo ba ya dora hannuwa a kugu ya daure fuska "a cikin gidan nawa kike zancen tsakura min abinci? Ashe baki da mutumci ban sani ba. To ki jira in dawo ciki zaki ga yadda zanyi dake mutuniyar banza"
Ta tsorata sosai amma sai ta dake kada tayi saurin nunawa "ni Hajiyayye kake yiwa wannan magana? Ko magagin baccin da ka soma ne bai sakeka ba?"
Kallon banza yayi mata harda su juya idanu yau take sallah fa a wurinsa ya fita a gaggauce. Kiris ya rage ya saki fitsari da ya ga 'ya'yan Hajiyayye ne ashe a akori kura manyan mazan su uku katti dasu tamkar ba daga cikinta suka fito ba. Dirowa suka yi daga bayan motar suka cewa dreban yaje gidan gonar ya jirasu. Zasu ci abinci ne su zo a dauko shanu ko hudu ne idan motar zata dauka. Idanun Malamijo sai suka kawo ruwa ya fara kokawa da kwalla. Samarin suka sauko kai cikin gidan suna muzurai su a dole mayu 'ya'yan mayya. Tsabar wulakanci basu duba tsufansa ba suka ringa bangazar kafadarsa suka shige cikin gidan. Jiki a sanyaye ya juya zai koma sai ga wasu galla gallan motoci guda biyu sun doso gidan.
Ihu ne kawai baiyi ba don tsananin murna ya koma daga soron ya tsaya yana jiransu. Jin kansa yake daidai da kowane maye da yake cikin gidansa.
Emzee da Ibrahim ne suka fara shigowa ya tarbesu cikin nishadi. Sai 'yan mata Hibbah da Zayyana sannan Radhiya ta biyo bayansu.
"Malamijo nawa" tace tana murmushin da ta saba idan zata yi masa tsiya.