Sashe 86
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shabiyu da rabi kowa yayi wanka mata na gidan Ummi maza na bangaren Mama wurin Raji suna ta hira. Mama ta koma wurin Ummi ta sallami duka yaran nan zuwa gidanta tace baki zasu yi zata kira su su gaishe su. Ya rage daga ita sai Mami da Ummi. Zahra ce karshen fitan tana tafiya Mami tace
"Wallahi Zainab mun gaji da wannan nuku nukun naki. Yanzu Daddy yace wai Excellency ma ya kirasu su dawo gida, suna hanya shi da Baba Hadir. Kin saka mu a duhu"
Kwalla ta share duk yadda taso daurewa "kuyi hakuri nan da mintuna kadan ne komai zai fito"
**********
Zayyan kallon kansa yayi yana karawa. Babu abinda ya kai tsafta da gyara dadi. Shi da mayar da jikinsa da yin kyau sosai sai an kwana biyu amma ko a haka sai dai ace Alhamdulillahi. Fuskarsa ta fito an gyare shi sosai. Wanka kuwa kamar bazai fito ba saboda jindadin ruwan da yayi da yadda yake cire dattin jikinsa. Lallausan yadi irin na masu hannu da shuni fari kal Awwab ya zaba masa a cikin kayan da aka siyo da bakar hula. Yau ya ga me ake kira turare designer da ko sunansa bai taba ji ba a da. Komai na shiryawa hatta links din hannu Awwab ne ya saka masa. Shima yayi wanka amma kayansa ya mayar suka fito duka aka dunguma motocin da suke jiransu. Yau mota biyu akayi saboda gwamna baya son a gane shine.
Tafiyar minti shabiyar suka shigo cikin estate din bangaren gidajen guda uku da suke gefe da gefe da juna.
Ana tsayawa Zayyan ya damki hannun Awwab.
"Tabani in tabbatar nine" yace muryarsa tana rawa da iyakar gaskiyarsa.
Awwab sai ya kara karfin rikon dake tsakanin hannuwansu. Gabansu duka faduwa yake Zayyan ya runtse ido ya kuma budewa a hankali yake cewa "Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba. Idan kuma mafarki ne Allah kasa na mutu a cikinsa"
Hannunsa Awwab ya sake rikewa suka fara takawa sannu a hankali bangaren Mairama Ali Gidado uwar Alheran da Muhammad Zayyan.
"Ba mafarki kake yi ba Daadaa. Ka tsaya a nan minti daya in fara shiga" yace lokacin da suka taka matattakala biyun da ake hawa kafin ya shiga gidan.
Da sallama ya shiga ya sami iyayen nasa duka a zazzaune sun saka Mama a gaba harda Major ana son jin bayaninta. Tana ganin Awwab ta mike sa sauri.
"Yauwa Awwab kun iso? Ina yake?"
Sai suka kara daurewa kowa kai da Awwab yace yana bakin kofa zai shigo dashi.
Komawa yayi da baya ya bude kofar ya riko hannuwan Zayyan suna tsaye da Excellency ya iso wurin.
Awwab ne ya daga labule yayin da muryar Zayyan ta karade falon a lokacin da yake cewa "Assalamu alaikum"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Gabadayansa ya bayyana a gabansu kafin muryar ta gama shiga kunnuwansu.
"Daddy, Baba...." Awwab ya soma cewa sai dai tuni Zayyan yayi gaba haka ma Daddy din da Baba sun taso daga wurin zamansu sun tare shi a tsakiyar falon.
"Zzzzayyyannn kaine?" Baba Hadir yace da karfinsa.
Manyan maza magidanta duniya ta sanyasu kuka tamkar yara. A wannan lokacin Hadir ne tsaye a gaban Zayyan dinsa. Hannuwansa yasa yana shafa shi kafin su kankame juna.
Major da ya tabbata ba mafarki ne ba ya ware hannuwansa ya rungume su su duka biyun a tare yana nasa hawayen. Excellency ma nasa yake yi a gefe yana jinjina karfin soyayyar wadannan mutane.
Duk abinda suke yi Mairama tana zaune kamar an dasata ta kasa motsi. Tana iya jiyo kukan Mami da Mama sama sama ita kuwa ta kasa. Wai shin ta cigaba da zama ne a wurin tana kallon Sojanta ko kuwa ta tashi itama taje ta rungume shi ko sau daya ne kafin ta farka daga wannan daddadan mafarki. Tunda take mafarkin Zayyan bata taba irin wannan da zata gansu a wuri daya duka tare ba. Ina ma Radhiya da Emzee zasu shigo suma su karasa cike mata mafarkin.
Tayi nisa a wannan tunani bata san Zayyan ya iso gabanta ya duka ba. Hannuwanta da ya rike masu laushi wani irin shock yaji na soyayya, tausayi da girmamawa a gareta da ta dauki shekaru ashirin da biyu tana dakon soyayyarsa bata yi aure ba. Runtse idanu tayi tana ayyana da gaske ne haka Zayyan zai dawo mata duk ya rame? Ashe kuwa zata dauki lokaci wurin ganin ta ciyar dashi duk abinda zai taimaka ya sake gina masa jiki.
Rikon da yayiwa hannunta da kakkarfan hannunsa sai kuma yatsansa da yasa yana kore mata hawayen dake gudana a fuskarta batare da ta sani ba shine ya sanyata dawo cikin hayyacinta daga tunanin da tayi zurfi tana yi. Tsigar jikinta ke tashi a lokacin da Zayyan ya mikar da ita tsaye ya dora hannuwansa akan kafadunta yana tayata kukan.
"Wai kuka zamuyi ta yi ne? Bazaki yiwa mijinki barka da dawowa ba?" Yayi maganar kamar baya so saboda shaukin dake dibarsa.
Wani hawayen ta matse ta hanyar runtse idanunta sannan ta budesu ta kalle shi da kyau wani abu yana sauka a kahon zuciyarta. A hankali ta daga hannunta daya ta shafa kumatunsa da wahala ta ramar.
"Ashe ba mafarki nake yi ba" tace lokaci guda ta sulale a jikinsa ta fadi sumammiya.
"Fillo" ya kira sunanta hankalinsa a tashe. Mama ta daure tace ya kwantar da hankalinsa abin ne yayi mata yawa. Ita kuma Mami ta samo ruwa a kitchen.
Ana shafa mata ta bude idanu suka sauka acikin na Zayyan.
"Da gaske ba mafarki nake yi ba?" Hawaye na gudana a idanunta take yi masa wannan tambaya.
"Nima tsoro nake kada a tasheni daga bacci"
"Ina ka tafi ka barni?" Tace tana fashewa da wani irin kuka.
"Wurin da ko makiyina bana fatan yaje. Kiyi hakuri Fillo na aureki na barki cikin..."
Kai ta shiga kadawa tana daga zaune akan kujerar da aka kwantar da ita da ta suma "kada kace komai sai godiyar Allah"
Sun bawa kowa na wurin tausayi. Major ya katse maganar tasu saboda kada aji kunya gasu a wurin ga Awwab da yake ta aikin share kwalla ya zama a koke.
Zayyan ya dago ya sake kallonsu yana fitar da murmushin mai karawa fuskarsa annuri. Ya tambayi Awwab "ina kannenka?"
Da sauri ya nemi nambar Zahra tana dauka yace su zo su duka falon Ummi anyi bako. Duka suka taho harda Raji. Baby Zayyan yana kafadar yayansa Ibrahim wanda Allah Ya sanyawa kaunarsa daga haduwarsu jiya.
Daya bayan daya suka shigo falon. Kowa na zaune banda Awwab da yake daga gefen kofa sai kuma wani dogon mutum da suna fara shigowa ya tashi yana murmushi.
Awwab yace da kannen nasa da dan karfi "introduce yourselves"
Radhiya ta juyo suka hada ido ta kawar da kai ita tana fushi kuma a ranta bata da niyar fadin nata sunan.
Fauziyya ce ta farko ta matso gabansa zata gaishe shi ya mika hannu ya karbi Jawad "Fauziyya?"
Tayi mamaki har ya nuna a idanunta. Shi kuwa ya tuna ta ne kasancewar duka 'ya'yan Major ita kadai ya sani fara sauran duka wankan tawarda suke.
Yaronta ya bata saboda ganin wani da yayi a hannun ta kusa da ita ya karbe shi shima "Zahra?"
Duk da bata sanshi ba taji dadi ko waye wannan mutumin mai kwarjini itama ya santa.
Wani jaririn ya kuma gani a hannun wani matashi da babu tantama kamanni sun nuna dan Zainab da Hadir ne. Kafin ya ambaci sunansa Ibrahim yana murmushi tare da mika masa yaron yace cikin alfahari "Ibrahim Hadir da Zayyan Hadir"
Zayyan ya juya ya kalli Hadir ya yi murmushi sannan ya bashi yaron. Wata 'yar budurwa ya gani ta kusa da wadda yake kallo tun shigowarsu wato Radhiya ta turo ta gaba ita kuma sai kunya take ji ya dan rage tsayi "kema in daukeki ne?"
'Yan uwanta ta kalla ta dan marairaice a kunyace "a'a nima ka fadi sunana"
Ibrahim ya girgiza kai, ashe bata dena shagwaba ba. Ji yadda take tale baki ita da ta gama secondary.
"Kiyi hakuri ki fada min da kanki inyi miki babbar kyauta"
"Zayyanatu Mustapha" tace saboda taji Ibrahim ma ya fadi harda sunan babansu.
Baki bude Zayyan ya kalli Major da ya kafe shi da ido kamar idan ya rufe zai bude ya neme shi ya rasa.
Emzee ne ya rage a gabansa. Yaron tunda suka shigo yake ta kallon wannan mutumi yana tunanin a ina ya taba ganin fuska shigen wannan. Kallon kallo suke yi Zayyan yana jin kamar yana kallon younger version dinsa ne. Ashe Radhiya ma ta soma tunanin inda tasan fuskar ita da ta haddace kamanin mahaifinta a hoto.
Emzee ya bude baki kenan ta matso da sauri tana jin jikinta yana rawa. Tunda suka shigo ya gama gane wacece dinsa shiyasa ma ya bar yi mata magana sai a karshe.
"Kamar na san ka wallahi" tace muryarta a kasa kamar mai rada.
Hannu yasa ya janyota gabansa sosai ta tsare shi da manyan idanunta "Alheran Radhiya baki gane Daadaa ba?"
"Ya Allah" ta furta a gigice ta rungume shi tana kuka mai sauti. Bayanta kawai yake shafawa yana kokarin mayar da nasa hawayen.
"Ehemm..ni sunana..." Emzee yayi gyaran murya shima yau dauriya ta kare sai hawaye "Muhammad Zayyan Tureta"
Haba...koda yaji wannan yaro zuciyarsa ta bashi cewa jininsa ne. Sakin Radhiya yayi hawayen da yake kokarin kada ya zubar a gaban 'ya'ya suka fito suka rungume juna cikin farinciki suna kuka. Zayyan ya dago yana ta shafa fuskar Emzee wai wannan ma nasa ne.
"Kafi jindadin ganinsa a kaina ko?" Yaji Radhiya tace a raunane tana kara karyar masa da zuciya.
"A'a Alheran" yace yana sakin Emzee ya sake rungumeta.
"Kenan ni bakayi murnar ganina ba?" Shima Emzee yace yana jin haushin tayi masa kauron jin dumin babansa ya koma wurinta.
Zayyan sai ya rikice yana soma cewa "ba haka bane" ya ga Alheran ta kafe shi da ido shima Emzee ya tsaya yana jiran amsarsa.
Dariya suka ji daga bayansu. Falon da ake ta kuka ma'abota cikinsa sun koma dariyar wannan haduwa ta uba da 'ya'yansa. Hadasu yayi kowanne a bari daya ya rungumesu kamar za'a kwace masa su
**********
"Wallahi Zainab mun gaji da wannan nuku nukun naki. Yanzu Daddy yace wai Excellency ma ya kirasu su dawo gida, suna hanya shi da Baba Hadir. Kin saka mu a duhu"
Kwalla ta share duk yadda taso daurewa "kuyi hakuri nan da mintuna kadan ne komai zai fito"
**********
Zayyan kallon kansa yayi yana karawa. Babu abinda ya kai tsafta da gyara dadi. Shi da mayar da jikinsa da yin kyau sosai sai an kwana biyu amma ko a haka sai dai ace Alhamdulillahi. Fuskarsa ta fito an gyare shi sosai. Wanka kuwa kamar bazai fito ba saboda jindadin ruwan da yayi da yadda yake cire dattin jikinsa. Lallausan yadi irin na masu hannu da shuni fari kal Awwab ya zaba masa a cikin kayan da aka siyo da bakar hula. Yau ya ga me ake kira turare designer da ko sunansa bai taba ji ba a da. Komai na shiryawa hatta links din hannu Awwab ne ya saka masa. Shima yayi wanka amma kayansa ya mayar suka fito duka aka dunguma motocin da suke jiransu. Yau mota biyu akayi saboda gwamna baya son a gane shine.
Tafiyar minti shabiyar suka shigo cikin estate din bangaren gidajen guda uku da suke gefe da gefe da juna.
Ana tsayawa Zayyan ya damki hannun Awwab.
"Tabani in tabbatar nine" yace muryarsa tana rawa da iyakar gaskiyarsa.
Awwab sai ya kara karfin rikon dake tsakanin hannuwansu. Gabansu duka faduwa yake Zayyan ya runtse ido ya kuma budewa a hankali yake cewa "Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba. Idan kuma mafarki ne Allah kasa na mutu a cikinsa"
Hannunsa Awwab ya sake rikewa suka fara takawa sannu a hankali bangaren Mairama Ali Gidado uwar Alheran da Muhammad Zayyan.
"Ba mafarki kake yi ba Daadaa. Ka tsaya a nan minti daya in fara shiga" yace lokacin da suka taka matattakala biyun da ake hawa kafin ya shiga gidan.
Da sallama ya shiga ya sami iyayen nasa duka a zazzaune sun saka Mama a gaba harda Major ana son jin bayaninta. Tana ganin Awwab ta mike sa sauri.
"Yauwa Awwab kun iso? Ina yake?"
Sai suka kara daurewa kowa kai da Awwab yace yana bakin kofa zai shigo dashi.
Komawa yayi da baya ya bude kofar ya riko hannuwan Zayyan suna tsaye da Excellency ya iso wurin.
Awwab ne ya daga labule yayin da muryar Zayyan ta karade falon a lokacin da yake cewa "Assalamu alaikum"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Gabadayansa ya bayyana a gabansu kafin muryar ta gama shiga kunnuwansu.
"Daddy, Baba...." Awwab ya soma cewa sai dai tuni Zayyan yayi gaba haka ma Daddy din da Baba sun taso daga wurin zamansu sun tare shi a tsakiyar falon.
"Zzzzayyyannn kaine?" Baba Hadir yace da karfinsa.
Manyan maza magidanta duniya ta sanyasu kuka tamkar yara. A wannan lokacin Hadir ne tsaye a gaban Zayyan dinsa. Hannuwansa yasa yana shafa shi kafin su kankame juna.
Major da ya tabbata ba mafarki ne ba ya ware hannuwansa ya rungume su su duka biyun a tare yana nasa hawayen. Excellency ma nasa yake yi a gefe yana jinjina karfin soyayyar wadannan mutane.
Duk abinda suke yi Mairama tana zaune kamar an dasata ta kasa motsi. Tana iya jiyo kukan Mami da Mama sama sama ita kuwa ta kasa. Wai shin ta cigaba da zama ne a wurin tana kallon Sojanta ko kuwa ta tashi itama taje ta rungume shi ko sau daya ne kafin ta farka daga wannan daddadan mafarki. Tunda take mafarkin Zayyan bata taba irin wannan da zata gansu a wuri daya duka tare ba. Ina ma Radhiya da Emzee zasu shigo suma su karasa cike mata mafarkin.
Tayi nisa a wannan tunani bata san Zayyan ya iso gabanta ya duka ba. Hannuwanta da ya rike masu laushi wani irin shock yaji na soyayya, tausayi da girmamawa a gareta da ta dauki shekaru ashirin da biyu tana dakon soyayyarsa bata yi aure ba. Runtse idanu tayi tana ayyana da gaske ne haka Zayyan zai dawo mata duk ya rame? Ashe kuwa zata dauki lokaci wurin ganin ta ciyar dashi duk abinda zai taimaka ya sake gina masa jiki.
Rikon da yayiwa hannunta da kakkarfan hannunsa sai kuma yatsansa da yasa yana kore mata hawayen dake gudana a fuskarta batare da ta sani ba shine ya sanyata dawo cikin hayyacinta daga tunanin da tayi zurfi tana yi. Tsigar jikinta ke tashi a lokacin da Zayyan ya mikar da ita tsaye ya dora hannuwansa akan kafadunta yana tayata kukan.
"Wai kuka zamuyi ta yi ne? Bazaki yiwa mijinki barka da dawowa ba?" Yayi maganar kamar baya so saboda shaukin dake dibarsa.
Wani hawayen ta matse ta hanyar runtse idanunta sannan ta budesu ta kalle shi da kyau wani abu yana sauka a kahon zuciyarta. A hankali ta daga hannunta daya ta shafa kumatunsa da wahala ta ramar.
"Ashe ba mafarki nake yi ba" tace lokaci guda ta sulale a jikinsa ta fadi sumammiya.
"Fillo" ya kira sunanta hankalinsa a tashe. Mama ta daure tace ya kwantar da hankalinsa abin ne yayi mata yawa. Ita kuma Mami ta samo ruwa a kitchen.
Ana shafa mata ta bude idanu suka sauka acikin na Zayyan.
"Da gaske ba mafarki nake yi ba?" Hawaye na gudana a idanunta take yi masa wannan tambaya.
"Nima tsoro nake kada a tasheni daga bacci"
"Ina ka tafi ka barni?" Tace tana fashewa da wani irin kuka.
"Wurin da ko makiyina bana fatan yaje. Kiyi hakuri Fillo na aureki na barki cikin..."
Kai ta shiga kadawa tana daga zaune akan kujerar da aka kwantar da ita da ta suma "kada kace komai sai godiyar Allah"
Sun bawa kowa na wurin tausayi. Major ya katse maganar tasu saboda kada aji kunya gasu a wurin ga Awwab da yake ta aikin share kwalla ya zama a koke.
Zayyan ya dago ya sake kallonsu yana fitar da murmushin mai karawa fuskarsa annuri. Ya tambayi Awwab "ina kannenka?"
Da sauri ya nemi nambar Zahra tana dauka yace su zo su duka falon Ummi anyi bako. Duka suka taho harda Raji. Baby Zayyan yana kafadar yayansa Ibrahim wanda Allah Ya sanyawa kaunarsa daga haduwarsu jiya.
Daya bayan daya suka shigo falon. Kowa na zaune banda Awwab da yake daga gefen kofa sai kuma wani dogon mutum da suna fara shigowa ya tashi yana murmushi.
Awwab yace da kannen nasa da dan karfi "introduce yourselves"
Radhiya ta juyo suka hada ido ta kawar da kai ita tana fushi kuma a ranta bata da niyar fadin nata sunan.
Fauziyya ce ta farko ta matso gabansa zata gaishe shi ya mika hannu ya karbi Jawad "Fauziyya?"
Tayi mamaki har ya nuna a idanunta. Shi kuwa ya tuna ta ne kasancewar duka 'ya'yan Major ita kadai ya sani fara sauran duka wankan tawarda suke.
Yaronta ya bata saboda ganin wani da yayi a hannun ta kusa da ita ya karbe shi shima "Zahra?"
Duk da bata sanshi ba taji dadi ko waye wannan mutumin mai kwarjini itama ya santa.
Wani jaririn ya kuma gani a hannun wani matashi da babu tantama kamanni sun nuna dan Zainab da Hadir ne. Kafin ya ambaci sunansa Ibrahim yana murmushi tare da mika masa yaron yace cikin alfahari "Ibrahim Hadir da Zayyan Hadir"
Zayyan ya juya ya kalli Hadir ya yi murmushi sannan ya bashi yaron. Wata 'yar budurwa ya gani ta kusa da wadda yake kallo tun shigowarsu wato Radhiya ta turo ta gaba ita kuma sai kunya take ji ya dan rage tsayi "kema in daukeki ne?"
'Yan uwanta ta kalla ta dan marairaice a kunyace "a'a nima ka fadi sunana"
Ibrahim ya girgiza kai, ashe bata dena shagwaba ba. Ji yadda take tale baki ita da ta gama secondary.
"Kiyi hakuri ki fada min da kanki inyi miki babbar kyauta"
"Zayyanatu Mustapha" tace saboda taji Ibrahim ma ya fadi harda sunan babansu.
Baki bude Zayyan ya kalli Major da ya kafe shi da ido kamar idan ya rufe zai bude ya neme shi ya rasa.
Emzee ne ya rage a gabansa. Yaron tunda suka shigo yake ta kallon wannan mutumi yana tunanin a ina ya taba ganin fuska shigen wannan. Kallon kallo suke yi Zayyan yana jin kamar yana kallon younger version dinsa ne. Ashe Radhiya ma ta soma tunanin inda tasan fuskar ita da ta haddace kamanin mahaifinta a hoto.
Emzee ya bude baki kenan ta matso da sauri tana jin jikinta yana rawa. Tunda suka shigo ya gama gane wacece dinsa shiyasa ma ya bar yi mata magana sai a karshe.
"Kamar na san ka wallahi" tace muryarta a kasa kamar mai rada.
Hannu yasa ya janyota gabansa sosai ta tsare shi da manyan idanunta "Alheran Radhiya baki gane Daadaa ba?"
"Ya Allah" ta furta a gigice ta rungume shi tana kuka mai sauti. Bayanta kawai yake shafawa yana kokarin mayar da nasa hawayen.
"Ehemm..ni sunana..." Emzee yayi gyaran murya shima yau dauriya ta kare sai hawaye "Muhammad Zayyan Tureta"
Haba...koda yaji wannan yaro zuciyarsa ta bashi cewa jininsa ne. Sakin Radhiya yayi hawayen da yake kokarin kada ya zubar a gaban 'ya'ya suka fito suka rungume juna cikin farinciki suna kuka. Zayyan ya dago yana ta shafa fuskar Emzee wai wannan ma nasa ne.
"Kafi jindadin ganinsa a kaina ko?" Yaji Radhiya tace a raunane tana kara karyar masa da zuciya.
"A'a Alheran" yace yana sakin Emzee ya sake rungumeta.
"Kenan ni bakayi murnar ganina ba?" Shima Emzee yace yana jin haushin tayi masa kauron jin dumin babansa ya koma wurinta.
Zayyan sai ya rikice yana soma cewa "ba haka bane" ya ga Alheran ta kafe shi da ido shima Emzee ya tsaya yana jiran amsarsa.
Dariya suka ji daga bayansu. Falon da ake ta kuka ma'abota cikinsa sun koma dariyar wannan haduwa ta uba da 'ya'yansa. Hadasu yayi kowanne a bari daya ya rungumesu kamar za'a kwace masa su
**********