Sashe 33
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Badaru ya rike baki abin da daure kai "Yallabai gaskiya ka binciki mutumin da yayi maka karairayin nan tun wuri"
"Ban fahimceka ba"
Mami da Zainab har sun fara damuwa ganin yadda iyalan gidan su ka canja fuska su ma.
Badaru ya gyara zama ya soma yi musu bayani "zancen da nake muku Mairama tayi akalla shekara shida ko ma fi da makancewa, Radhiya da Zayyan kuma suna tare da ita a can wurin dangin babarta. Sai dai mutumci irin nata wallahi har ila yau tana turo mana yaran idan sun sami hutu"
Kuka wiwi Zainab da Mami suke yi. Zuwa yanzu sai dai su ce sun ga jiya sun ga yau a auren soja. Makanta, yanzu ace Mairama ta makance babu ido.
A sanyaye Major yace "ban tari numfashinka ba, wane Zayyan kake magana a kai?"
Jume tace "Zayyanu karami kanin Radhiya"
Mami ta zaro idanu "aka ce mana ta haihu jariri babu rai"
A fusace Jume tace "wai uban waye ne da wadannan karairayin? Yarinya tana fama da lalura da rashin miji anbi an dabaibayeta da karya. Rashin waiwayarta da kuka yi yafi komai damunta, bata da masaniyar inda kowa yake cikinku gashi dangin ita mahaifiyar Zayyanu suma shiru rabonmu dasu tun sunan 'Yar soja"
Zuciyar Major tuni ta kawo wuya ya daga waya zai kira dan sakon nasa sai ga Maikudi ikon Allah. Su Maikudi an karo wulakanci yana shiga yana fita duk wata yana jin 'yan chanjinsa a aljihu. Saboda son zuciya ma sai ya dena 'yar fafutukar da yake tunda dai albashin nan yana shigowa babu fashi.
"Yauwa Maikudi gara da Allah Ya dawo da kai da yanzu."
Idanunsa akan bakin ya kula akwai maiko a tare dasu "hee...hee baki muka yi a gidan ne. Sannunku da zuwa."
Matarsa ya shiga kwalawa kira "ya naga babu ko 'yar mantina dinnan a gabansu? Wannan ai halin karanta ne. Waye nan a cikin yaran azo a nemo musu abin sha mai sanyi"
Ran Jume ya fara baci tace "to dan ayi jikan na'isa, mu duk bamu iya ba sai kai. Ni zo ka jiye min baki ke neman Radhiya wai an fada musu a gidan nan take"
A take kuzarinsa ya fara raguwa "ki fada musu inda take su je mana"
"Mutanen nan fa abokan Marigayi ne, shi wannan yace ya dauki lokaci yana aiko da kudi kuma ance a gidannan ake karba" Badaru ya kara masa haske
Abinka da munafuki gumi ya soma yi kamar an kwara masa ruwa "indai don Allah suke yi sai abar tone tone su sake mata kyautar tunda sun dawo. Ni bari na shiga ciki na gaji"
Wani irin kallo Major da Hadir ke yi masa. Ashe Jume ma tasha jinin jizkinta. Ai kuwa bazata barshi ba indai haka ne. Kankace ido tayi ta kaurara murya
"Maikudi kada kace min kana da masaniya akan maganar da mutanen nan suke yi"
Ja da baya ya soma yi a tsorace "Ni kuma? Daga shigowata? Uhmm nayi nan akwai mai son ganina a waje" kafin su farga ya fice da sauri.
Yau da ace Hadir na da lafiya Maikudi sai ya yabawa aya zakinta. Major ma tashi ne dai baiyi ba amma ko ciki daya suka fito da Zayyan sai ya nuna masa yayi kuskure.
"Ku tashi mu tafi" yace dasu gabadaya.
Jume tana kuka matan gida da Badaru suna salati suke basu hakuri.
Babu alamun wasa a fuskarsa yace "Ku bani nambar waya da zamu nemi kwatancen inda Ummin Awwab take. Shi kuma wancan kafin na turo masu kama shi a fada masa nasan iya abinda na turo saboda haka ina bukatar kudin nan...da gaggawa"
Ransa yayi matukar baci ne yaki amincewa da masaukin da Jume tace ayi musu a gidan. Giginya hotel suka yi masauki washegari sai ga Badaru da sassafe ya kira yace zaiyi musu rakiya har Rugar Barkindo.
**********
Saboda yanayin matsanancin zafi da ake fama dashi yau gidan har Ardo suna zazzaune a karkashin katuwar darbejiyar da ta yiwa tsakar gidan inuwa suna taba hira.
Yammaci ne na asabar Radhiya tasan cewa Zakari zai zo kawo wani sabon maganin ciwon ido da aka rubutawa Mairama a asibitin Bauchi inda yake aikin lab wato dakin gwaji. Gyaran nono ta gama wanda ta cire man shanu sannan ta je tayi wanka.
Shiryawa tayi cikin riga da skirt ta saka hijabinta iya gwiwa don zuciyarta tana raya mata yau kawun nata zai fada mata abinda idanunta suke ganin yana boyewa...soyayyarta.
Har kofar gidan Ardo aka rako su Major suka firfito kowa da nasa tunanin. A yayin da rayuwa tayi ta garasu ita Mairama kauye ta fado. Kauyen ma ruga da abubuwan cigaba suka yi mata karanci fiye da ko ina.
Fitowarsu ke da wuya sai ga Emzee nan da wani abokinsa sun dawo daga kiwon shanun Ardo. Sanda ce a wuyansa amma shirt da dogon wando ya saka suna ta hirarsu ta samari.
Ba Major da Hadir ba, hatta Mami da Zainab sai da gabansu ya fadi da ganinsa. Wannan banda haske babu ta inda zaka ce ya baro mahaifinsa.
Kawunsa ya hango ya yi saurin barin abokinsa ya taho "Kawu Badaru yaushe ka iso"
"Tare da bakin Umminku nake. Yi maza ka shiga kayi mana iso"
Gaishe su yayi cikin gurbatacciyar hausarsu ta tsantsar fulani ya shiga ya fada musu. Mairama ta auna ta auno ta kasa gane su waye zasu zo nemanta tare da Badaru.
Radhiya da ta tabbatar zuwan bakin zai hanata sakewa da Zakari ta shiga tura baki. Innawuro tace tayi shimfida sannan aka ce su shigo.
Zainab da Mairama kowacce wai dakewa take yi kada suyi abin kunya a gaban 'ya'yansu amma da sauri suka shiga gidan.
Mairama tana zaune akan tabarma ga sandarta a gefe ta yafa mayafi kalar kayanta. Daga bayanta kuwa babu tantama Alheran Radhiya ce wadda ganin 'yan gayu suna shigowa yasa ta manta da batun Zakari ta shiga washe baki.
Mairama tana ji Innawuro tana yi musu barka da zuwa amma yaran kadai ke amsawa. Manyan kuwa Mairama suke kallo da take ta murmushi a hankali a zatonta babu mai ji tace "Ke su waye ne sai kamshi nake ji"
Mami a gabanta ta zauna tana kuka ta kama hannunta da makanta bata hanata ayyuka irinsu yin fura ba da nata lallausan hannun. Zainab kuwa a gefenta ta zauna ta rungumo Mairama a jikinta. Rasa gane me yake faruwa ita da kowa na gidan suka yi.
Radhiya da ta kurawa Major da Hadir idanu ta saki ihu kamar an tsunguleta.
"Yasin Ummi na ganesu na hoton nan ne"
Mami tasa hannu ta shafa fuskar Mairama tace "Ummin Awwab"
Duk da bata gani sai da idanunta suka kara girma gabanta ya tsananta faduwa, baki na rawa tace "Mami??? Ke duba hotunan akwai wannan a ciki?" Ta fada tana kankame hannun Mami kamar zata kuma tafiya.
"Ai shikenan tunda baki ce a duba dani ba" Zainab tayi maganar da wasa cikin kukan da yaci karfinta.
Mairama fashewa kawai tayi da kuka su ukun suka rungume juna suna hawaye sauran jama'ar wurin suna tayasu mazansu da matansu.[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Duk dauriya irin ta Ardo sai da ya matse kwalla ganin yadda hatta mazan kowanne ido yayi jajir.
Mairama ce ta fara magana cikinsu "ina Awwab dan Ummi? Nasan ya girma yanzu? Anyi masa aure ne?"
Zahra tace "Mami ashe da gaske dai Ummin Hamma Awwab mu bata sonmu"
Mairama sai dariya ta kufce mata ta daga hannuwa ta tashi tsaye tana cewa "Zahra, kece ko? Ina Fauziyya da Ibrahim abokin fadan wannan yarinyar?"
Fauziyya da Zahra suka matso suna rike hannuwanta tace "kuji min yara yaushe zan ganeku da hannu kawai, haka ake yi" ta fada tana rungumesu.
Muryar wata shagwababbiya da hausarta ke fita kamar mai waka saboda yadda yaren Germany da turanci ya kama mata baki taji tana cewa "Daddy ni kowa baya sona, she even asked for Hamma that is not here"
Ibrahim kallonta yayi ya tabe baki, yarinya yar shekara sha hudu kamar yadda yaji Mami ta fada sai ta dage tana zuba tabara Daddynta yana biye mata.
Emzee kuwa murmushi yayi bai ce mata komai ba. A gidan Ardo shine karami bai saba ganin haka ba shiyasa yadda tayi ya burge shi.
Mairama sai ta sake dariya ta rasa ina zata kai farincikin da yake cikin zuciyarta.
"Such a sweet voice, wace ce wannan?"
Zayyana dadi ya mamayeta ance muryarta da dadi ta tafi da sauri ta ture Fauziyya da Zahra ta shige jikin Mairama tana cewa cikin tsantsar mamakin wannan 'yar kauyen "Daddy she speaks English too"
Ibrahim ya kwalo idanu a hankali yace "ji min rainin wayo."
Sai kuma suka tsinkayi Radhiya muryar tayi kicin-kicin da fuska tana kallon Zayyana "ke yarinya iya bakinki wallahi, Ummina ma 'yar boko ce har secondary ta gama ehe"
"Zaki fara ko?" Mairama tace tana zaunawa har lokacin Zayyana na jikinta ba ta fahimci dogon zancen Radhiyan ba.
"Ai gara na fada mata gaskiya tun wuri kada ganinki a kauye yasa ayi miki kallon wata local"
Haba wuri sai ya kaure da dariya harda Major. Sai lokacin Mairama ta gama gane su waye a wurin kunya ta kamata. Halin Radhiya sai ita.
Zainab tana cewa ta zo Mami ma tana kiranta sai ta rasa wurin wa zata je. Zainab tace "jeki dai dama ita ce mamanki, ni Zayyan zan dauka nafi kama da maman maza"
Rufe fuska tayi da hannuwanta tana kallonsu a fakaice sai wani blushing take "wallahi kun sani jin kunya...duk sona kuke yi"
Wata dariyar ta basu Mami ta janyo hannunta ta zauna a kusa da ita "haka kika koma Alheran din Awwab? Wannan idan na wuni dake cikina sai ya kulle"
"Indai wannan ce baki ga komai ba" cewar Innawuro.
Kowa a cikinsu yana cike da tsananin farinciki. 'Ya'yansu ma ko da basu gama sanin mahimmancin iyayen nasu a wurin juna ba sun amince wannan haduwa ta faranta ran iyayensu su ma dole su ji dadi.
"Idan kun gama kukan da dariyar ya kamata a gaisa kuma haka" Ardo yace dasu don ya dakatar da zubar hawayen matan.
Sai kuma aka soma gaisawa ana tambayar yaya bayan saduwa. Mairama ta fuskanci bangaren da take jin a nan su Major suke ta saki fuska.
"Ban fahimceka ba"
Mami da Zainab har sun fara damuwa ganin yadda iyalan gidan su ka canja fuska su ma.
Badaru ya gyara zama ya soma yi musu bayani "zancen da nake muku Mairama tayi akalla shekara shida ko ma fi da makancewa, Radhiya da Zayyan kuma suna tare da ita a can wurin dangin babarta. Sai dai mutumci irin nata wallahi har ila yau tana turo mana yaran idan sun sami hutu"
Kuka wiwi Zainab da Mami suke yi. Zuwa yanzu sai dai su ce sun ga jiya sun ga yau a auren soja. Makanta, yanzu ace Mairama ta makance babu ido.
A sanyaye Major yace "ban tari numfashinka ba, wane Zayyan kake magana a kai?"
Jume tace "Zayyanu karami kanin Radhiya"
Mami ta zaro idanu "aka ce mana ta haihu jariri babu rai"
A fusace Jume tace "wai uban waye ne da wadannan karairayin? Yarinya tana fama da lalura da rashin miji anbi an dabaibayeta da karya. Rashin waiwayarta da kuka yi yafi komai damunta, bata da masaniyar inda kowa yake cikinku gashi dangin ita mahaifiyar Zayyanu suma shiru rabonmu dasu tun sunan 'Yar soja"
Zuciyar Major tuni ta kawo wuya ya daga waya zai kira dan sakon nasa sai ga Maikudi ikon Allah. Su Maikudi an karo wulakanci yana shiga yana fita duk wata yana jin 'yan chanjinsa a aljihu. Saboda son zuciya ma sai ya dena 'yar fafutukar da yake tunda dai albashin nan yana shigowa babu fashi.
"Yauwa Maikudi gara da Allah Ya dawo da kai da yanzu."
Idanunsa akan bakin ya kula akwai maiko a tare dasu "hee...hee baki muka yi a gidan ne. Sannunku da zuwa."
Matarsa ya shiga kwalawa kira "ya naga babu ko 'yar mantina dinnan a gabansu? Wannan ai halin karanta ne. Waye nan a cikin yaran azo a nemo musu abin sha mai sanyi"
Ran Jume ya fara baci tace "to dan ayi jikan na'isa, mu duk bamu iya ba sai kai. Ni zo ka jiye min baki ke neman Radhiya wai an fada musu a gidan nan take"
A take kuzarinsa ya fara raguwa "ki fada musu inda take su je mana"
"Mutanen nan fa abokan Marigayi ne, shi wannan yace ya dauki lokaci yana aiko da kudi kuma ance a gidannan ake karba" Badaru ya kara masa haske
Abinka da munafuki gumi ya soma yi kamar an kwara masa ruwa "indai don Allah suke yi sai abar tone tone su sake mata kyautar tunda sun dawo. Ni bari na shiga ciki na gaji"
Wani irin kallo Major da Hadir ke yi masa. Ashe Jume ma tasha jinin jizkinta. Ai kuwa bazata barshi ba indai haka ne. Kankace ido tayi ta kaurara murya
"Maikudi kada kace min kana da masaniya akan maganar da mutanen nan suke yi"
Ja da baya ya soma yi a tsorace "Ni kuma? Daga shigowata? Uhmm nayi nan akwai mai son ganina a waje" kafin su farga ya fice da sauri.
Yau da ace Hadir na da lafiya Maikudi sai ya yabawa aya zakinta. Major ma tashi ne dai baiyi ba amma ko ciki daya suka fito da Zayyan sai ya nuna masa yayi kuskure.
"Ku tashi mu tafi" yace dasu gabadaya.
Jume tana kuka matan gida da Badaru suna salati suke basu hakuri.
Babu alamun wasa a fuskarsa yace "Ku bani nambar waya da zamu nemi kwatancen inda Ummin Awwab take. Shi kuma wancan kafin na turo masu kama shi a fada masa nasan iya abinda na turo saboda haka ina bukatar kudin nan...da gaggawa"
Ransa yayi matukar baci ne yaki amincewa da masaukin da Jume tace ayi musu a gidan. Giginya hotel suka yi masauki washegari sai ga Badaru da sassafe ya kira yace zaiyi musu rakiya har Rugar Barkindo.
**********
Saboda yanayin matsanancin zafi da ake fama dashi yau gidan har Ardo suna zazzaune a karkashin katuwar darbejiyar da ta yiwa tsakar gidan inuwa suna taba hira.
Yammaci ne na asabar Radhiya tasan cewa Zakari zai zo kawo wani sabon maganin ciwon ido da aka rubutawa Mairama a asibitin Bauchi inda yake aikin lab wato dakin gwaji. Gyaran nono ta gama wanda ta cire man shanu sannan ta je tayi wanka.
Shiryawa tayi cikin riga da skirt ta saka hijabinta iya gwiwa don zuciyarta tana raya mata yau kawun nata zai fada mata abinda idanunta suke ganin yana boyewa...soyayyarta.
Har kofar gidan Ardo aka rako su Major suka firfito kowa da nasa tunanin. A yayin da rayuwa tayi ta garasu ita Mairama kauye ta fado. Kauyen ma ruga da abubuwan cigaba suka yi mata karanci fiye da ko ina.
Fitowarsu ke da wuya sai ga Emzee nan da wani abokinsa sun dawo daga kiwon shanun Ardo. Sanda ce a wuyansa amma shirt da dogon wando ya saka suna ta hirarsu ta samari.
Ba Major da Hadir ba, hatta Mami da Zainab sai da gabansu ya fadi da ganinsa. Wannan banda haske babu ta inda zaka ce ya baro mahaifinsa.
Kawunsa ya hango ya yi saurin barin abokinsa ya taho "Kawu Badaru yaushe ka iso"
"Tare da bakin Umminku nake. Yi maza ka shiga kayi mana iso"
Gaishe su yayi cikin gurbatacciyar hausarsu ta tsantsar fulani ya shiga ya fada musu. Mairama ta auna ta auno ta kasa gane su waye zasu zo nemanta tare da Badaru.
Radhiya da ta tabbatar zuwan bakin zai hanata sakewa da Zakari ta shiga tura baki. Innawuro tace tayi shimfida sannan aka ce su shigo.
Zainab da Mairama kowacce wai dakewa take yi kada suyi abin kunya a gaban 'ya'yansu amma da sauri suka shiga gidan.
Mairama tana zaune akan tabarma ga sandarta a gefe ta yafa mayafi kalar kayanta. Daga bayanta kuwa babu tantama Alheran Radhiya ce wadda ganin 'yan gayu suna shigowa yasa ta manta da batun Zakari ta shiga washe baki.
Mairama tana ji Innawuro tana yi musu barka da zuwa amma yaran kadai ke amsawa. Manyan kuwa Mairama suke kallo da take ta murmushi a hankali a zatonta babu mai ji tace "Ke su waye ne sai kamshi nake ji"
Mami a gabanta ta zauna tana kuka ta kama hannunta da makanta bata hanata ayyuka irinsu yin fura ba da nata lallausan hannun. Zainab kuwa a gefenta ta zauna ta rungumo Mairama a jikinta. Rasa gane me yake faruwa ita da kowa na gidan suka yi.
Radhiya da ta kurawa Major da Hadir idanu ta saki ihu kamar an tsunguleta.
"Yasin Ummi na ganesu na hoton nan ne"
Mami tasa hannu ta shafa fuskar Mairama tace "Ummin Awwab"
Duk da bata gani sai da idanunta suka kara girma gabanta ya tsananta faduwa, baki na rawa tace "Mami??? Ke duba hotunan akwai wannan a ciki?" Ta fada tana kankame hannun Mami kamar zata kuma tafiya.
"Ai shikenan tunda baki ce a duba dani ba" Zainab tayi maganar da wasa cikin kukan da yaci karfinta.
Mairama fashewa kawai tayi da kuka su ukun suka rungume juna suna hawaye sauran jama'ar wurin suna tayasu mazansu da matansu.[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Duk dauriya irin ta Ardo sai da ya matse kwalla ganin yadda hatta mazan kowanne ido yayi jajir.
Mairama ce ta fara magana cikinsu "ina Awwab dan Ummi? Nasan ya girma yanzu? Anyi masa aure ne?"
Zahra tace "Mami ashe da gaske dai Ummin Hamma Awwab mu bata sonmu"
Mairama sai dariya ta kufce mata ta daga hannuwa ta tashi tsaye tana cewa "Zahra, kece ko? Ina Fauziyya da Ibrahim abokin fadan wannan yarinyar?"
Fauziyya da Zahra suka matso suna rike hannuwanta tace "kuji min yara yaushe zan ganeku da hannu kawai, haka ake yi" ta fada tana rungumesu.
Muryar wata shagwababbiya da hausarta ke fita kamar mai waka saboda yadda yaren Germany da turanci ya kama mata baki taji tana cewa "Daddy ni kowa baya sona, she even asked for Hamma that is not here"
Ibrahim kallonta yayi ya tabe baki, yarinya yar shekara sha hudu kamar yadda yaji Mami ta fada sai ta dage tana zuba tabara Daddynta yana biye mata.
Emzee kuwa murmushi yayi bai ce mata komai ba. A gidan Ardo shine karami bai saba ganin haka ba shiyasa yadda tayi ya burge shi.
Mairama sai ta sake dariya ta rasa ina zata kai farincikin da yake cikin zuciyarta.
"Such a sweet voice, wace ce wannan?"
Zayyana dadi ya mamayeta ance muryarta da dadi ta tafi da sauri ta ture Fauziyya da Zahra ta shige jikin Mairama tana cewa cikin tsantsar mamakin wannan 'yar kauyen "Daddy she speaks English too"
Ibrahim ya kwalo idanu a hankali yace "ji min rainin wayo."
Sai kuma suka tsinkayi Radhiya muryar tayi kicin-kicin da fuska tana kallon Zayyana "ke yarinya iya bakinki wallahi, Ummina ma 'yar boko ce har secondary ta gama ehe"
"Zaki fara ko?" Mairama tace tana zaunawa har lokacin Zayyana na jikinta ba ta fahimci dogon zancen Radhiyan ba.
"Ai gara na fada mata gaskiya tun wuri kada ganinki a kauye yasa ayi miki kallon wata local"
Haba wuri sai ya kaure da dariya harda Major. Sai lokacin Mairama ta gama gane su waye a wurin kunya ta kamata. Halin Radhiya sai ita.
Zainab tana cewa ta zo Mami ma tana kiranta sai ta rasa wurin wa zata je. Zainab tace "jeki dai dama ita ce mamanki, ni Zayyan zan dauka nafi kama da maman maza"
Rufe fuska tayi da hannuwanta tana kallonsu a fakaice sai wani blushing take "wallahi kun sani jin kunya...duk sona kuke yi"
Wata dariyar ta basu Mami ta janyo hannunta ta zauna a kusa da ita "haka kika koma Alheran din Awwab? Wannan idan na wuni dake cikina sai ya kulle"
"Indai wannan ce baki ga komai ba" cewar Innawuro.
Kowa a cikinsu yana cike da tsananin farinciki. 'Ya'yansu ma ko da basu gama sanin mahimmancin iyayen nasu a wurin juna ba sun amince wannan haduwa ta faranta ran iyayensu su ma dole su ji dadi.
"Idan kun gama kukan da dariyar ya kamata a gaisa kuma haka" Ardo yace dasu don ya dakatar da zubar hawayen matan.
Sai kuma aka soma gaisawa ana tambayar yaya bayan saduwa. Mairama ta fuskanci bangaren da take jin a nan su Major suke ta saki fuska.