Sashe 28
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mairama kwantar da hankalinki muje wajen don nan bazai daukemu ba. Ni da su duka dangin Mairo ne mahaifiyarki"
"Me? Da gaske?" Matsawa tayi daga jikin Radhiya hannuwanta suna neman kofa da sauri zata fita.
Innawuro jiki ya kama rawa ganin da yadda Mairama ta fita. Radhiya ta kalla hawaye suna wanke fuskarta.
"Bata gani ne?"
Radhiya tabi bayan Mairama don ta karasa da ita gabansu tana cewa "eh"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta iya fada tana kuka har wajen suna jin sautinta.
Duka idanunsu sun koma kan Mairama tana kuka take tambayar Radhiya da ta rike mata hannu su nawa ne?
Baffa Gide kamar yadda 'ya'yan 'yan uwa suke kiransa ji yayi kamar iska zata daga shi don tashin hankali da yaji me takw cewa kuma tamkar ya ga Mairo haka kamanin Mairama suke da na 'yar uwarta. Kyaunta ne yasa Malamijo zabarta da biyan bashi duk da a lokacin Innawuro ta girme mata kuma itama bata yi aure ba.
Tsakar gidan kamar gidan kallo ya koma. Ga dangin mahaifiyar Mairama ga ahalin gidan Malamijo kacokan.
Shi Baffa Habubakari kuka yake ma saboda rauninsa yafi na dan uwansa. 'Ya'yansu jiki yayi sanyi. Basu san Mairo ba don manyan ma suna kanana komai ya faru amma sun san wannan makauniyar da ta nufosu jininsu ce. Ga dai idanu a bude amma basa ganin komai.
Sai da suka zo tsakiya Radhiya taja hannunta don su gaishesu tunda ta ga akwai manya "ummi mu gaishesu"
Emzee sai ya baro gefe shima ya dawo ya durkusa tare da Umminsa da Addarsa.
"Ina wuninku, yaya hanya....Allah sarki ashe baku manta dani ba" shine abinda Mairama take cewa tana ta waige hagu da dama saboda rashin sanin a ina suke.
Su Radhiya ma gaishe su suka yi bakin Mairama kamar gonar auduga duk da bata san mutum nawa bane. Ganinsu su ukun nan ya ishi bawa tausayi. Ga uwa mai cike da kuruciya amma makauniya mai marayu biyu a gabanta. Ga kuma 'ya'yanta tamkar zakuna suna gadin farincikinsu, jigon rayuwarsu.
Sautin kuka Mairama ta fara ji daga yawancin matan da suke wurin ta rinka murmushi tana jiran taji wani cikinsu ya tabata taji dumin uwa. Kamar Innawuro ta sani ta durkusa a gabanta ta rungumeta suna sakin kuka a tare.
Ardo Barkindo ya kalli Malamijo ya fito a tsolon rakensa yace "a bamu wuri mu zauna ko"
Sai kuma ya farga ya dawo daga duniyar tunani "kai, kai ina kuke ne, ga baki a shimfada musu tabarmi daga jikin bangon can yafi inuwa."
Tabarmin aka kawo suka zazzauna ya sake dubansu "wace mai girki ne a kawo musu abinci"
Hajjo sarkin bakar magana ta tabe baki "Binta ce kuma yanzu ka dankara mata saki ko a kirawo ta ne?"
Kunya tamkar wanda aka watsawa ruwan kankara haka Malamijo yaji ya muzanta a gaban mutanen da ya taba wulakantawa yau suka taru suka yi masa kwarjini.
Allah Ya taimake shi Yadikko ta dawo yace "Uhmm, uhmmm....Yadikko fito da kwanuka aje gidan Tsahare ayi musu hadin wake da shinkafa amma da miya za'a siyo da salak. Idan akwai taliya 'yar gwamnati duka ta bada saboda ya ishesu. Sannan tasa nama a wadace do Allah"
Yau wace rana Malamijo zaiyi abin kai. Ya zura hannu zai zaro kudi yaji hankalinsa ya tashi...mutanen nan fa da yawa, anya ba duka rugarsu Gide ya kwaso ba?
Ardo ya dakatar dashi don bai manta bayanan da yaji game da Malamijo ba.
"Kaga Malam Ali ba zama zamuyi ba a kan hanya muke. Ka zauna muyi magana"
A tsorace ya zauna daga gefen Baffa Gide don kallon da yake masa kamar zai wafto shi ya shiga dukansa ne. Bangaren matan kuwa Mairama sai dai taji wannan ta rike mata hannu ko an shafa bayanta suna fadin sunayensu.
Da addua ga marigayiya Mairo Ardo ya fara bude zaman nasu sannan ya ari bakin duka dangin nasu ya baiwa Mairama hakuri akan zumunci da suka yi sakaci dashi. Daga karshe ya gabatar da bukatarsu da cewa a yau dinnan ba gobe ba suke son daukarta da 'ya'yanta zasu koma da ita wurinsu.
"Don Allah da gaske?" Mairama ta sami kanta da fada cike da farinciki. Bata sansu ba kuma bata san halayensu ba amma ko don samun nutsuwarta tana so ace gata da dangin mahaifiyarta.
Matar Baffa Habubakari tace mata "Allah Yasa ki yarda ki bimu"
Ita kuwa me zai hanata yarda idan ba rashin sanin ciwon kai ba. Ardo ya umarci yaran nasu maza da su je su shigo da kayan da suka zo dasu. Malamijo ya baza ido ya ga wane shirgin suka kawo sai kukan tumaki ya ratsa kunnensa.
Raguna hudu ne da katoto kuma kosasshen sa guda daya. Kwanduna manya manya guda biyu cike da kwan zabi, buhun shinkafa daya 'yar gwamnati mai doki sai 'yar hausa daya da kuma buhun gero shima biyu.
"Tun daga haihuwar Mairama har aurenta, haihuwar jikokinmu da rasuwar mijinta da muka sami labari babu wani abu daya da muka halarta balle mu bada gudunmawa a matsayin iyayenta. Mal Ali ga wannan kayan, ba wai sakayya bace sai dai ihsani ne daga garemu kuma muna godiya a madadin marigayiya Mairo na kula da marainiyar Allah da kayi" Baffa Gide ya ce sauran suna gyada kai.
Innawuro ta riko hannun Emzee ya zauna a gefenta "ba rabaka zamuyi da ita ba. Mairama har abada 'yarka ce. Muna so ne dai ta bimu ta sanmu muma mu santa"
Yake Malamijo yake ya rasa dalilin da yasa suka yi masa kwarjini "bama zan hanaku tafiya da ita ba"
Kasa magana Malamijo yayi sai tarin kunya kamar ya tona rami ya binne kansa. Ba Mairama ba kadai kaf 'yayansa me zai bugi kirji yace yayi musu. Hajjo sai da ta magantu taji dadi ta fake da yi musu godiya "Allah Ya saka da alkhairi mungode. Ohh Malamijo baki sun zo gari -e- gari ko ruwa ba'a basu ba sai karbar kyauta daga hannunsu. Ke Radhiya tashi muje na tayaku hada kaya yau kakarku ta yanke saka"
Cike da zumudi Radhiya ta mike tana kallon yadda Mairama take ta fara'a a tsakanin mutane. Idan ma kuruciya tasa bata gane mahimmancin zumunci ba a iya hankalinta ta sani cewa Umminta tana cikin farinciki. Wannan kuma ya isheta komai.
Yadikko bata hakura ba sai da ta dafa musu dafadukan shinkafa da wake. Babu bama dai bare kifi amma tayi nata kokarin. Abin kunya ne ace wannan bakin sun zo sun tafi basu ci komai ba ga nisan hanya. Tasan tsiyar da suka tarar a gidan ita ta kara tunzura komawarsu a ranar.
Batare da bata lokaci ba suka fito an gama shiri. Wani dan akwati da take ajiyar mahimman abubuwa kamar khakin Zayyan, wasikarsa da kuma hotuna tace Radhiya ta tabbata ta dauko. Dariya tayi don ta gama haddace komai na ciki. Hotunan yawanci na bikin iyayenta ne da na sunanta.
Karfe biyar da kwata sun gama shiga mota. Baffa Gide yana tsaye a gefen mota kusa da Malamijo suka sake yin musabaha "yanzu da muka dena yawo idan kana nemanmu mun koma Giade can asalin garinmu amma rugarmu tana daga ciki da dan tafiya daga garin. Wannan da kake gani mijin Innawuro shine Ardo na biyu bayan kafuwar rugar"
Sallama Mairama tayi da kowa daga ita har su Radhiya ko digon hawaye irin na kewa dinnan. Rabuwa da Yadikko da Hajjo da kuma sauran 'yan uwa ya dan sa sunji wani iri to amma fa ko kadan bikin Magaji bazai hana na Magajiya ba.
**********
WAIWAYE....
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mairama ta ga gata da ya amsa sunan gata a Rugar Barkindo. 'Yan uwa ke tururuwar ganinta har ana fadan gidan wa zata zauna. Ardo yayi tsalle ya dire yace matarsa ce zata dauka ai ita ce mace. Dole sauran suka amince aka barwa Innawuro.
Idan manya ko dattijai cikin danginsu sunzo sai ayi ta kallonta ana cewa kaza dinta irin na Mairo ne. Murmushi kawai take yi don ko hoton mahaifiyarta bata taba gani ba. Sun tausaya mata da jin labarin rasuwar mijinta ga makanta.
Radhiya da Emzee sai gasu cikin 'yan uwa sa'anninsu ana ta nishadi. Abinci da nama anci an ture. Kafin sati ya zagayo jikinsu ya fara nuna kwanciyar hankali da koshi.
Mairama kullum cikin godiya take ga Allah da Ya dawo mata da dangin mahaifiyarta. Ba jimawa sabo ya kullu sosai a tsakaninsu baki daya. So da tausayawa suke nuna mata da 'ya 'yanta. Ardo ke cewa su duka marayu ne ababen dubawa.
Bata cuci kanta ba ta roki alfarmar su Radhiya su koma makaranta. Tare aka nema musu JSS 1 ita da Emzee da ya gama aji biyar. Ita a makarantar kwana ta gwamnatin jaha ta mata shi kuma jeka ka dawo ta maza. Ranar da dan gidan Baffa Habubakari ya kawo takardun tubure musu Radhiya tayi da kuka wai bata so.
"Karatun kike yiwa haka Radhiya?" Innawuro tace tana kokarin bata baki.
"Dama saboda bama cin abinci mu koshi ne fa Ummi ta kaini makaranta inyi kudi"
Mairama kunya ta isheta tasa hannu tana nemanta "haka muka yi dake? Kuji min yarinya"
"Da naga ko nama bama ci irin na gidan Baba Kallamu shine nayi zaton haka ne" ta mayar mata da amsa tana shure-shure.
"Idan bata yi ba ai ba'a kirata jikar Ali ba" Innawuro tace tana dariya.
Radhiya ta turo baki "Malamijo muke kiransa mu dai"
"Ina yaga malanta sai bakar rowa da mammakon tsiya"
"La la lahhhh baban Ummi ne fa"
Ardo yana jinsu yana rubutu a jikin allo yace "da kyau 'yar albarka ki kare masa kinji ko. Duk tsiyar naka ai naka ne Innawuro"
Dariya rigimar Radhiyan ke bata tace "kasan ni ba bakuwar zafi bace Allah Ya baki hakuri. Nima kizo na baki labarin 'yar uwata Mairo. Ga kyau ga kirki kamar wata dan daren goma sha hudu"
Idanu Radhiya ta bude sosai da mamaki "wata dai irin na sama Innawuro?"
"Akwai wata a kasa ne?" Mairama ta fada tana jin kamar ta mangareta.
"Tabdi, Ummi kenan Innar taki a mulmule take kamar wata. Ga Malamijo kamar tsolon rake. Mu dai Allah Ya taimakemu ke daidai kike."
"Me? Da gaske?" Matsawa tayi daga jikin Radhiya hannuwanta suna neman kofa da sauri zata fita.
Innawuro jiki ya kama rawa ganin da yadda Mairama ta fita. Radhiya ta kalla hawaye suna wanke fuskarta.
"Bata gani ne?"
Radhiya tabi bayan Mairama don ta karasa da ita gabansu tana cewa "eh"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta iya fada tana kuka har wajen suna jin sautinta.
Duka idanunsu sun koma kan Mairama tana kuka take tambayar Radhiya da ta rike mata hannu su nawa ne?
Baffa Gide kamar yadda 'ya'yan 'yan uwa suke kiransa ji yayi kamar iska zata daga shi don tashin hankali da yaji me takw cewa kuma tamkar ya ga Mairo haka kamanin Mairama suke da na 'yar uwarta. Kyaunta ne yasa Malamijo zabarta da biyan bashi duk da a lokacin Innawuro ta girme mata kuma itama bata yi aure ba.
Tsakar gidan kamar gidan kallo ya koma. Ga dangin mahaifiyar Mairama ga ahalin gidan Malamijo kacokan.
Shi Baffa Habubakari kuka yake ma saboda rauninsa yafi na dan uwansa. 'Ya'yansu jiki yayi sanyi. Basu san Mairo ba don manyan ma suna kanana komai ya faru amma sun san wannan makauniyar da ta nufosu jininsu ce. Ga dai idanu a bude amma basa ganin komai.
Sai da suka zo tsakiya Radhiya taja hannunta don su gaishesu tunda ta ga akwai manya "ummi mu gaishesu"
Emzee sai ya baro gefe shima ya dawo ya durkusa tare da Umminsa da Addarsa.
"Ina wuninku, yaya hanya....Allah sarki ashe baku manta dani ba" shine abinda Mairama take cewa tana ta waige hagu da dama saboda rashin sanin a ina suke.
Su Radhiya ma gaishe su suka yi bakin Mairama kamar gonar auduga duk da bata san mutum nawa bane. Ganinsu su ukun nan ya ishi bawa tausayi. Ga uwa mai cike da kuruciya amma makauniya mai marayu biyu a gabanta. Ga kuma 'ya'yanta tamkar zakuna suna gadin farincikinsu, jigon rayuwarsu.
Sautin kuka Mairama ta fara ji daga yawancin matan da suke wurin ta rinka murmushi tana jiran taji wani cikinsu ya tabata taji dumin uwa. Kamar Innawuro ta sani ta durkusa a gabanta ta rungumeta suna sakin kuka a tare.
Ardo Barkindo ya kalli Malamijo ya fito a tsolon rakensa yace "a bamu wuri mu zauna ko"
Sai kuma ya farga ya dawo daga duniyar tunani "kai, kai ina kuke ne, ga baki a shimfada musu tabarmi daga jikin bangon can yafi inuwa."
Tabarmin aka kawo suka zazzauna ya sake dubansu "wace mai girki ne a kawo musu abinci"
Hajjo sarkin bakar magana ta tabe baki "Binta ce kuma yanzu ka dankara mata saki ko a kirawo ta ne?"
Kunya tamkar wanda aka watsawa ruwan kankara haka Malamijo yaji ya muzanta a gaban mutanen da ya taba wulakantawa yau suka taru suka yi masa kwarjini.
Allah Ya taimake shi Yadikko ta dawo yace "Uhmm, uhmmm....Yadikko fito da kwanuka aje gidan Tsahare ayi musu hadin wake da shinkafa amma da miya za'a siyo da salak. Idan akwai taliya 'yar gwamnati duka ta bada saboda ya ishesu. Sannan tasa nama a wadace do Allah"
Yau wace rana Malamijo zaiyi abin kai. Ya zura hannu zai zaro kudi yaji hankalinsa ya tashi...mutanen nan fa da yawa, anya ba duka rugarsu Gide ya kwaso ba?
Ardo ya dakatar dashi don bai manta bayanan da yaji game da Malamijo ba.
"Kaga Malam Ali ba zama zamuyi ba a kan hanya muke. Ka zauna muyi magana"
A tsorace ya zauna daga gefen Baffa Gide don kallon da yake masa kamar zai wafto shi ya shiga dukansa ne. Bangaren matan kuwa Mairama sai dai taji wannan ta rike mata hannu ko an shafa bayanta suna fadin sunayensu.
Da addua ga marigayiya Mairo Ardo ya fara bude zaman nasu sannan ya ari bakin duka dangin nasu ya baiwa Mairama hakuri akan zumunci da suka yi sakaci dashi. Daga karshe ya gabatar da bukatarsu da cewa a yau dinnan ba gobe ba suke son daukarta da 'ya'yanta zasu koma da ita wurinsu.
"Don Allah da gaske?" Mairama ta sami kanta da fada cike da farinciki. Bata sansu ba kuma bata san halayensu ba amma ko don samun nutsuwarta tana so ace gata da dangin mahaifiyarta.
Matar Baffa Habubakari tace mata "Allah Yasa ki yarda ki bimu"
Ita kuwa me zai hanata yarda idan ba rashin sanin ciwon kai ba. Ardo ya umarci yaran nasu maza da su je su shigo da kayan da suka zo dasu. Malamijo ya baza ido ya ga wane shirgin suka kawo sai kukan tumaki ya ratsa kunnensa.
Raguna hudu ne da katoto kuma kosasshen sa guda daya. Kwanduna manya manya guda biyu cike da kwan zabi, buhun shinkafa daya 'yar gwamnati mai doki sai 'yar hausa daya da kuma buhun gero shima biyu.
"Tun daga haihuwar Mairama har aurenta, haihuwar jikokinmu da rasuwar mijinta da muka sami labari babu wani abu daya da muka halarta balle mu bada gudunmawa a matsayin iyayenta. Mal Ali ga wannan kayan, ba wai sakayya bace sai dai ihsani ne daga garemu kuma muna godiya a madadin marigayiya Mairo na kula da marainiyar Allah da kayi" Baffa Gide ya ce sauran suna gyada kai.
Innawuro ta riko hannun Emzee ya zauna a gefenta "ba rabaka zamuyi da ita ba. Mairama har abada 'yarka ce. Muna so ne dai ta bimu ta sanmu muma mu santa"
Yake Malamijo yake ya rasa dalilin da yasa suka yi masa kwarjini "bama zan hanaku tafiya da ita ba"
Kasa magana Malamijo yayi sai tarin kunya kamar ya tona rami ya binne kansa. Ba Mairama ba kadai kaf 'yayansa me zai bugi kirji yace yayi musu. Hajjo sai da ta magantu taji dadi ta fake da yi musu godiya "Allah Ya saka da alkhairi mungode. Ohh Malamijo baki sun zo gari -e- gari ko ruwa ba'a basu ba sai karbar kyauta daga hannunsu. Ke Radhiya tashi muje na tayaku hada kaya yau kakarku ta yanke saka"
Cike da zumudi Radhiya ta mike tana kallon yadda Mairama take ta fara'a a tsakanin mutane. Idan ma kuruciya tasa bata gane mahimmancin zumunci ba a iya hankalinta ta sani cewa Umminta tana cikin farinciki. Wannan kuma ya isheta komai.
Yadikko bata hakura ba sai da ta dafa musu dafadukan shinkafa da wake. Babu bama dai bare kifi amma tayi nata kokarin. Abin kunya ne ace wannan bakin sun zo sun tafi basu ci komai ba ga nisan hanya. Tasan tsiyar da suka tarar a gidan ita ta kara tunzura komawarsu a ranar.
Batare da bata lokaci ba suka fito an gama shiri. Wani dan akwati da take ajiyar mahimman abubuwa kamar khakin Zayyan, wasikarsa da kuma hotuna tace Radhiya ta tabbata ta dauko. Dariya tayi don ta gama haddace komai na ciki. Hotunan yawanci na bikin iyayenta ne da na sunanta.
Karfe biyar da kwata sun gama shiga mota. Baffa Gide yana tsaye a gefen mota kusa da Malamijo suka sake yin musabaha "yanzu da muka dena yawo idan kana nemanmu mun koma Giade can asalin garinmu amma rugarmu tana daga ciki da dan tafiya daga garin. Wannan da kake gani mijin Innawuro shine Ardo na biyu bayan kafuwar rugar"
Sallama Mairama tayi da kowa daga ita har su Radhiya ko digon hawaye irin na kewa dinnan. Rabuwa da Yadikko da Hajjo da kuma sauran 'yan uwa ya dan sa sunji wani iri to amma fa ko kadan bikin Magaji bazai hana na Magajiya ba.
**********
WAIWAYE....
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mairama ta ga gata da ya amsa sunan gata a Rugar Barkindo. 'Yan uwa ke tururuwar ganinta har ana fadan gidan wa zata zauna. Ardo yayi tsalle ya dire yace matarsa ce zata dauka ai ita ce mace. Dole sauran suka amince aka barwa Innawuro.
Idan manya ko dattijai cikin danginsu sunzo sai ayi ta kallonta ana cewa kaza dinta irin na Mairo ne. Murmushi kawai take yi don ko hoton mahaifiyarta bata taba gani ba. Sun tausaya mata da jin labarin rasuwar mijinta ga makanta.
Radhiya da Emzee sai gasu cikin 'yan uwa sa'anninsu ana ta nishadi. Abinci da nama anci an ture. Kafin sati ya zagayo jikinsu ya fara nuna kwanciyar hankali da koshi.
Mairama kullum cikin godiya take ga Allah da Ya dawo mata da dangin mahaifiyarta. Ba jimawa sabo ya kullu sosai a tsakaninsu baki daya. So da tausayawa suke nuna mata da 'ya 'yanta. Ardo ke cewa su duka marayu ne ababen dubawa.
Bata cuci kanta ba ta roki alfarmar su Radhiya su koma makaranta. Tare aka nema musu JSS 1 ita da Emzee da ya gama aji biyar. Ita a makarantar kwana ta gwamnatin jaha ta mata shi kuma jeka ka dawo ta maza. Ranar da dan gidan Baffa Habubakari ya kawo takardun tubure musu Radhiya tayi da kuka wai bata so.
"Karatun kike yiwa haka Radhiya?" Innawuro tace tana kokarin bata baki.
"Dama saboda bama cin abinci mu koshi ne fa Ummi ta kaini makaranta inyi kudi"
Mairama kunya ta isheta tasa hannu tana nemanta "haka muka yi dake? Kuji min yarinya"
"Da naga ko nama bama ci irin na gidan Baba Kallamu shine nayi zaton haka ne" ta mayar mata da amsa tana shure-shure.
"Idan bata yi ba ai ba'a kirata jikar Ali ba" Innawuro tace tana dariya.
Radhiya ta turo baki "Malamijo muke kiransa mu dai"
"Ina yaga malanta sai bakar rowa da mammakon tsiya"
"La la lahhhh baban Ummi ne fa"
Ardo yana jinsu yana rubutu a jikin allo yace "da kyau 'yar albarka ki kare masa kinji ko. Duk tsiyar naka ai naka ne Innawuro"
Dariya rigimar Radhiyan ke bata tace "kasan ni ba bakuwar zafi bace Allah Ya baki hakuri. Nima kizo na baki labarin 'yar uwata Mairo. Ga kyau ga kirki kamar wata dan daren goma sha hudu"
Idanu Radhiya ta bude sosai da mamaki "wata dai irin na sama Innawuro?"
"Akwai wata a kasa ne?" Mairama ta fada tana jin kamar ta mangareta.
"Tabdi, Ummi kenan Innar taki a mulmule take kamar wata. Ga Malamijo kamar tsolon rake. Mu dai Allah Ya taimakemu ke daidai kike."