Sashe 57
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da rana tayi sosai aka miko musu plate da wani abu da Zayyan bai gane shinkafa ce, gero ko wake ba. Gashi nan dai a cure wuri guda. Col. Nasiruddeen yunwa ta galabaitar dashi ya rinka turawa kawai. Shima Zayyan sai ya ga bashi da zabin da ya wuce ya taya shi ci. Ba dadi ba dadadawa amma haka ake basu wannan abincin suna ci.
Sabo ne ya rinka shiga tsakanin wadannan bayin Allah da suke rayuwa a inda iyalansu da kowa nasu yake tunanin sun mutu. Kullum dare bayan 'yan tawayen nan sawunsu ya dauke daga dakin hirarsu sai ta karkata ga iyalansu. Dukkansu har jiran dare suke domin su saukewa juna nauyin zukatansu. Matsananciyar kewar iyalansu tana damunsu tana ci musu zukata. Yau ma bayan wata daya da kama Zayyan suna hira Col. Nasiruddeen yake cewa.
"Idan Allah Ya fitar dani daga wurin nan ina komawa abu na farko da zan fara yi shine yin ritaya. Zayyan na bar aikin soja har abada wallahi"
"Ka dena fadin haka Sir. Ni ka ga a duniya ban taba gani ko sha'awar wani aikin ba bayan shi."
"Da kuruciyarka ni kuwa girma ya soma zuwar min. Sa'annina da kannena suna kwance comfortably da iyalansa a wannan lokacin ina zaune a inda Allah kadai ya sani cikin wari da kazantar najasata. Babu wanka babu abinci mai kyau sannan duk abinda zamuyi sai dai mu yi shi a inda muke kuma mu kwana a ciki"
"Saboda abinda Allah Ya zaba maka kenan. Ya halicci mutane bayan kariyar da yake bamu da IkonSa kuma ya sanya mu garkuwa a garesu masu taimaka musu. I believe we soldiers are not made...we are born to protect (na yarda mu sojoji ba yinmu ake yi ba....haihuwar mu ake yi domin bada kariya)"
"We are special, nima na yarda...." Col. Nasiruddeen ya amsa da murmushi a fuskarsa "amma bazan cigaba da sacrificing rayuwata ga mutanen da basu san nayi musu ba. Ni da wannan aikin sai dai idan mutuwa nayi a wurin nan"
Dariya ya bawa Zayyan yadda ya hade rai da gaske ya gama da aikin soja "wannan magana fa kamar a kunnen Arifah. Nasan zata so ka cigaba da aiki muna biye daku"
Kafada ya noke kamar yaro "ko me zata yi sai dai tayi kuwa. Idan na mutu bakin aiki wa take dashi da zai kula min da ita? Burina kawai na koma gida na cigaba da bata kulawa. Shekara da shekaru ina neman haihuwa amma don ganganci ban tashi barin gida ba sai da na sami 'yar. Idan na mutu fa duka duka shekara hudu muka yi tare. Kila ma ta manta dani gabadaya"
Sai kuma ya bawa Zayyan tausayi. Col ya fada masa yadda ya kwashe shekaru shabiyar da aure tun da kuruciyarsa babu haihuwa sai akan Arifah. Yana son tilon 'yarsa kamar rai. Ranar da zai taho Liberia da kansa ya kaita makaranta nursery da take ta rinka kuka sai ta bishi. Zuciyarsa ta karye, ya baro mamanta tana nata kukan a gida itama tana yi kuma daga nan Lagos zasu wuce. Da kyar ya rarrasheta aka karbeta daga cikinsa tana ihu ya bar harabar makarantar.
Ranar da yaji labarin iyalin Zayyan ya tausaya masa matuka. Cewa yayi kada Zayyan ya kuma kiransa da wani abu da zai alakanta shi da soja sunana Baban Arifah shi kuma yana kiransa Baban Alheran.
Kwana uku a tsakani Zayyan ya soma tunanin hanyar guduwa. Sai da Col. Nasiruddeen yayi ta bashi shawarar kada ya fita ya fishi dadewa kuma shima ya gwada babu sa'a amma yaki hakura. Ta yaya zai hakura bayan kullum sai anzo an bashi wahala domin ya bada bayani shi kuma yaki. Sai ma zancen kashesu da aka fara wai zasu bar wurin an kusa gano su. Shiyasa yaga ya dace dole su nemi hanyar tsira.
Lallabawa yayi yana neman hanyar fita ya hango tawagar 'yan tawayen sun shigo wurin a guje. Masu gadin nasu da wasu kowa hankalinsa ya tashi. Cikin ikon Allah ya hango mutum biyu da kayan sojojin kasar amma umarni suke badawa a tabbatar babu wanda ya tsira a cikinsu. Su duka masu laifi.
"Shot on sight" (a harbe duk wanda aka gani) yaji ana bada umarni daga waje.
A guje ya koma ciki ya gano wani bari na katangar da ya dade yana tunanin haurawa sai kuma ya fasa ya shige inda suke ya tada Col. Nasiruddeen da yake bacci.
"Baban Arifah we need to run"
"Baban Alheran nace..."
Harbi suke ji da ihun maza da alamun guje guje. A gaggauce shima ya mike suka nufi wannan katanga. Zayyan ya haura saman ya miko hannu domin taimakawa Col. Nasiruddeen amma ya kasa saboda bashi da tsaho sosai. Ga tsira yana gani amma ya gaza. Idanunsa hawaye fal suna jin harbin yana kusanto inda suke yayi saluting Zayyan.
"It was nice meeting you Lieutenant. Take care"
Zukatansu sun karya su duka. Zayyan sai tuno Major Mustapha da dan uwansa Hadir yake yi. Soja shi kadai yasan ciwon soja. Durowa yayi kasa kafarsa tayi kara duk da haka ya kama Col. Nasiruddeen da mamaki mai tsanani ya kama shi na karamcin wannan yaro. A kafadarsa ya dora shi ya mike tsaye.
"Baban Arifah haura"
Col. Nasiruddeen ya mika hannu ya haye katangar bai sauka daya barin ba ya gano sojojin kasar da 'yan tawayen sun taho wurin gadan gadan. Su ma 'yan tawayen katangar suka zo haurawa. A gigice yace "yi sauri Zayyan"
Zayyan ya mika hannu ya hau katangar bai haura da kafafunsa ba bullet ya shiga kafadarsa. Col Nasiruddeen ya ga sanda aka yi harbin ya sa hannu zai janyo shi wani bullet din ya sami Zayyan a baya. Jikinsa ya saki duk yadda Col. Nasiruddeen yaso ko da gawarsa ce ya fitar daga wannan tsinannan gida bukata bata biya ba domin fadawa yayi baya aka cigaba da harbe harbe.
Col. Nasiruddeen ya sauka ta daya barin yasa gudu yayin da aka duba masu rai cikin 'yan tawaye harda Zayyan aka yi awon gaba dasu.
Taimako daya aka yi musu shi da sauran masu ran an cire musu bullets din jikinsu. Amma an gwada musu izaya da azaba nau'i daban daban domin su fadi inda sauran suke abu yaci tura. Sauran uban taurin kai ne yake damunsu shi kuwa Zayyan banda rashin sanin komai ya dage shi dan Nigeria ne. Da suka ga ya dage sai suka yi bincike akan unit da yace a cikinsu yake. Tashin farko akace wani mai suna Hadir Murtala ne kadai ya tsira a cikinsu tare da mutum daya daga wani unit din wato Major Mustapha.
Abu na ceton rai sauran ma kowa ya fara cewa shima wani ne baya cikin wadannan 'yan tawaye. Zasu fara dogon bincike aka kaiwa wani babban barikin sojojinsu mummunan hari wanda ya janyo gabadaya mutanen da aka kama harda 'yan wani kauye da tsautsayi ya ritsa dasu duka aka maka su a kurkuku.
Da fari Zayyan kusan hauka yayi a wurin. Tunanin iyalinsa yake yi. Mairama da Alheran da cikinta da yake tsammanin ta riga ta haife shi yanzu. A wane hali suke koma waye yake duba iyalansa? Yakan dauki tsahon lokaci yana zubar da hawaye masu zafi da kona zuciya. Uzurinsa na cewa shi ba dan tawaye bane bai karbo ba domin mutanen da ake kamowa sun hada da magidanta da matasa bisa tsautsayi. Kowa cikinsu kuma ya dage shima ba dan tawaye bane. Sai ake rasa gane waye mai gaskiya da makaryaci. Dadin matsakar kasar babu zaman lafiyar da zai bada damar a bata lokaci wurin sauraren korafinsu. A irin haka sojojin kasashe da dama suke riskar kawunansu a kurkuku daga zuwa kai dauki ga kasashen da suke cikin rikici.
Sannu a hankali ya karbi kaddararsa da hannu bibbiyu ya fawwalawa Allah lamuransa. Baya shiga harkar kowa a wurin sai ma shi da akan sami masu shiga tasa. Sai ayi masa duka bai ko daga yatsa. Rayuwarsa ta kuntata komai ya fice masa a rai. Daga baya ne ya sake rungumar addini fiye da baya har kusan kowa ya sallama masa hadda wadanda ba musulman ba kuwa. Zaman lafiyarsa da yanayin mu'amala yasa ya shiga zukatan jama'ar wurin. Zayyan Muhammad Tureta tun asalinsa mutum ne mai shiga rai shiyasa a nan din ma ya zama na kowa. Babu wanda zai yi yunkurin taka Zayyan wasu basu saita masa zama ba.
Col. Nasiruddeen yayi nasarar komawa gida ga iyalinsa. Satinsa guda da komawa yasa aka binciko masa barikin su Zayyan. Daga can ya sami kwatancen gidan iyayensa. Da kansa yaje Sakkwato ba sako ba har kofar gidansu. Da yake wahala bata yankewa su Mairamu ba a wannan lokaci da yasa ayi masa sallama da dan uwan Zayyan ba wanda ya fito sai Maikudi. Ya ga mutum a fige saboda tsabar wahala sai hanci dan firit. Yanayinsa gabadaya kama yayi masa da mutanen Nijar yayi zaton aiko shi akayi saboda basu yarda da bayanin da yayi musu ba. Rufe ido yayi ya maimaita masa cewa Mairama ta haifi da ba rai, ita da 'yarta kuma sunyi hatsari sun mutu. Col. Nasiruddeen yaji babu dadi jikinsa yayi mugun sanyi ya koma Jos wurin iyalinsa cike da damuwa. Zayyan ya rasu a dalilin ceton ransa kuma iyalansa ma duka babu su. A satin yaje ya kai takardarsa ta barin aiki. A wurinsa rayuwar soja ba tasa bace. Asibiti ya koma neman aiki sai dai lokuta da dama idan ya ga yawaitar jini musamman idan hatsari ne jikinsa ya rinka rawa kenan. Likita da tsoron jini aiki bazai taba yiwuwa ba bisa dole ya hakura ya tsunduma cikin harkar siyasa ka'in da na'in.
***********
SABON SHAFI
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Asibitin Nasarawa aka tura su Awwab domin samun kwararren likitan ido. Da za'a basu daki yace dakin mutum daya yake bukata kada a hadata da kowa. Sunyi sa'a kuwa an samu. Dakin a gyare yake amma duk da haka ya dage sai an sake karkade shi an wanke toilet. Da ya ga matar zata yi masa gardama wai sai da safe zata sake zuwa ya bata dubu biyu. Kafin Mama ta iso da su Emzee da 'yan tarkacen bukata na kwana irinsu bargo da zanin gado an gyara dakin.
Sabo ne ya rinka shiga tsakanin wadannan bayin Allah da suke rayuwa a inda iyalansu da kowa nasu yake tunanin sun mutu. Kullum dare bayan 'yan tawayen nan sawunsu ya dauke daga dakin hirarsu sai ta karkata ga iyalansu. Dukkansu har jiran dare suke domin su saukewa juna nauyin zukatansu. Matsananciyar kewar iyalansu tana damunsu tana ci musu zukata. Yau ma bayan wata daya da kama Zayyan suna hira Col. Nasiruddeen yake cewa.
"Idan Allah Ya fitar dani daga wurin nan ina komawa abu na farko da zan fara yi shine yin ritaya. Zayyan na bar aikin soja har abada wallahi"
"Ka dena fadin haka Sir. Ni ka ga a duniya ban taba gani ko sha'awar wani aikin ba bayan shi."
"Da kuruciyarka ni kuwa girma ya soma zuwar min. Sa'annina da kannena suna kwance comfortably da iyalansa a wannan lokacin ina zaune a inda Allah kadai ya sani cikin wari da kazantar najasata. Babu wanka babu abinci mai kyau sannan duk abinda zamuyi sai dai mu yi shi a inda muke kuma mu kwana a ciki"
"Saboda abinda Allah Ya zaba maka kenan. Ya halicci mutane bayan kariyar da yake bamu da IkonSa kuma ya sanya mu garkuwa a garesu masu taimaka musu. I believe we soldiers are not made...we are born to protect (na yarda mu sojoji ba yinmu ake yi ba....haihuwar mu ake yi domin bada kariya)"
"We are special, nima na yarda...." Col. Nasiruddeen ya amsa da murmushi a fuskarsa "amma bazan cigaba da sacrificing rayuwata ga mutanen da basu san nayi musu ba. Ni da wannan aikin sai dai idan mutuwa nayi a wurin nan"
Dariya ya bawa Zayyan yadda ya hade rai da gaske ya gama da aikin soja "wannan magana fa kamar a kunnen Arifah. Nasan zata so ka cigaba da aiki muna biye daku"
Kafada ya noke kamar yaro "ko me zata yi sai dai tayi kuwa. Idan na mutu bakin aiki wa take dashi da zai kula min da ita? Burina kawai na koma gida na cigaba da bata kulawa. Shekara da shekaru ina neman haihuwa amma don ganganci ban tashi barin gida ba sai da na sami 'yar. Idan na mutu fa duka duka shekara hudu muka yi tare. Kila ma ta manta dani gabadaya"
Sai kuma ya bawa Zayyan tausayi. Col ya fada masa yadda ya kwashe shekaru shabiyar da aure tun da kuruciyarsa babu haihuwa sai akan Arifah. Yana son tilon 'yarsa kamar rai. Ranar da zai taho Liberia da kansa ya kaita makaranta nursery da take ta rinka kuka sai ta bishi. Zuciyarsa ta karye, ya baro mamanta tana nata kukan a gida itama tana yi kuma daga nan Lagos zasu wuce. Da kyar ya rarrasheta aka karbeta daga cikinsa tana ihu ya bar harabar makarantar.
Ranar da yaji labarin iyalin Zayyan ya tausaya masa matuka. Cewa yayi kada Zayyan ya kuma kiransa da wani abu da zai alakanta shi da soja sunana Baban Arifah shi kuma yana kiransa Baban Alheran.
Kwana uku a tsakani Zayyan ya soma tunanin hanyar guduwa. Sai da Col. Nasiruddeen yayi ta bashi shawarar kada ya fita ya fishi dadewa kuma shima ya gwada babu sa'a amma yaki hakura. Ta yaya zai hakura bayan kullum sai anzo an bashi wahala domin ya bada bayani shi kuma yaki. Sai ma zancen kashesu da aka fara wai zasu bar wurin an kusa gano su. Shiyasa yaga ya dace dole su nemi hanyar tsira.
Lallabawa yayi yana neman hanyar fita ya hango tawagar 'yan tawayen sun shigo wurin a guje. Masu gadin nasu da wasu kowa hankalinsa ya tashi. Cikin ikon Allah ya hango mutum biyu da kayan sojojin kasar amma umarni suke badawa a tabbatar babu wanda ya tsira a cikinsu. Su duka masu laifi.
"Shot on sight" (a harbe duk wanda aka gani) yaji ana bada umarni daga waje.
A guje ya koma ciki ya gano wani bari na katangar da ya dade yana tunanin haurawa sai kuma ya fasa ya shige inda suke ya tada Col. Nasiruddeen da yake bacci.
"Baban Arifah we need to run"
"Baban Alheran nace..."
Harbi suke ji da ihun maza da alamun guje guje. A gaggauce shima ya mike suka nufi wannan katanga. Zayyan ya haura saman ya miko hannu domin taimakawa Col. Nasiruddeen amma ya kasa saboda bashi da tsaho sosai. Ga tsira yana gani amma ya gaza. Idanunsa hawaye fal suna jin harbin yana kusanto inda suke yayi saluting Zayyan.
"It was nice meeting you Lieutenant. Take care"
Zukatansu sun karya su duka. Zayyan sai tuno Major Mustapha da dan uwansa Hadir yake yi. Soja shi kadai yasan ciwon soja. Durowa yayi kasa kafarsa tayi kara duk da haka ya kama Col. Nasiruddeen da mamaki mai tsanani ya kama shi na karamcin wannan yaro. A kafadarsa ya dora shi ya mike tsaye.
"Baban Arifah haura"
Col. Nasiruddeen ya mika hannu ya haye katangar bai sauka daya barin ba ya gano sojojin kasar da 'yan tawayen sun taho wurin gadan gadan. Su ma 'yan tawayen katangar suka zo haurawa. A gigice yace "yi sauri Zayyan"
Zayyan ya mika hannu ya hau katangar bai haura da kafafunsa ba bullet ya shiga kafadarsa. Col Nasiruddeen ya ga sanda aka yi harbin ya sa hannu zai janyo shi wani bullet din ya sami Zayyan a baya. Jikinsa ya saki duk yadda Col. Nasiruddeen yaso ko da gawarsa ce ya fitar daga wannan tsinannan gida bukata bata biya ba domin fadawa yayi baya aka cigaba da harbe harbe.
Col. Nasiruddeen ya sauka ta daya barin yasa gudu yayin da aka duba masu rai cikin 'yan tawaye harda Zayyan aka yi awon gaba dasu.
Taimako daya aka yi musu shi da sauran masu ran an cire musu bullets din jikinsu. Amma an gwada musu izaya da azaba nau'i daban daban domin su fadi inda sauran suke abu yaci tura. Sauran uban taurin kai ne yake damunsu shi kuwa Zayyan banda rashin sanin komai ya dage shi dan Nigeria ne. Da suka ga ya dage sai suka yi bincike akan unit da yace a cikinsu yake. Tashin farko akace wani mai suna Hadir Murtala ne kadai ya tsira a cikinsu tare da mutum daya daga wani unit din wato Major Mustapha.
Abu na ceton rai sauran ma kowa ya fara cewa shima wani ne baya cikin wadannan 'yan tawaye. Zasu fara dogon bincike aka kaiwa wani babban barikin sojojinsu mummunan hari wanda ya janyo gabadaya mutanen da aka kama harda 'yan wani kauye da tsautsayi ya ritsa dasu duka aka maka su a kurkuku.
Da fari Zayyan kusan hauka yayi a wurin. Tunanin iyalinsa yake yi. Mairama da Alheran da cikinta da yake tsammanin ta riga ta haife shi yanzu. A wane hali suke koma waye yake duba iyalansa? Yakan dauki tsahon lokaci yana zubar da hawaye masu zafi da kona zuciya. Uzurinsa na cewa shi ba dan tawaye bane bai karbo ba domin mutanen da ake kamowa sun hada da magidanta da matasa bisa tsautsayi. Kowa cikinsu kuma ya dage shima ba dan tawaye bane. Sai ake rasa gane waye mai gaskiya da makaryaci. Dadin matsakar kasar babu zaman lafiyar da zai bada damar a bata lokaci wurin sauraren korafinsu. A irin haka sojojin kasashe da dama suke riskar kawunansu a kurkuku daga zuwa kai dauki ga kasashen da suke cikin rikici.
Sannu a hankali ya karbi kaddararsa da hannu bibbiyu ya fawwalawa Allah lamuransa. Baya shiga harkar kowa a wurin sai ma shi da akan sami masu shiga tasa. Sai ayi masa duka bai ko daga yatsa. Rayuwarsa ta kuntata komai ya fice masa a rai. Daga baya ne ya sake rungumar addini fiye da baya har kusan kowa ya sallama masa hadda wadanda ba musulman ba kuwa. Zaman lafiyarsa da yanayin mu'amala yasa ya shiga zukatan jama'ar wurin. Zayyan Muhammad Tureta tun asalinsa mutum ne mai shiga rai shiyasa a nan din ma ya zama na kowa. Babu wanda zai yi yunkurin taka Zayyan wasu basu saita masa zama ba.
Col. Nasiruddeen yayi nasarar komawa gida ga iyalinsa. Satinsa guda da komawa yasa aka binciko masa barikin su Zayyan. Daga can ya sami kwatancen gidan iyayensa. Da kansa yaje Sakkwato ba sako ba har kofar gidansu. Da yake wahala bata yankewa su Mairamu ba a wannan lokaci da yasa ayi masa sallama da dan uwan Zayyan ba wanda ya fito sai Maikudi. Ya ga mutum a fige saboda tsabar wahala sai hanci dan firit. Yanayinsa gabadaya kama yayi masa da mutanen Nijar yayi zaton aiko shi akayi saboda basu yarda da bayanin da yayi musu ba. Rufe ido yayi ya maimaita masa cewa Mairama ta haifi da ba rai, ita da 'yarta kuma sunyi hatsari sun mutu. Col. Nasiruddeen yaji babu dadi jikinsa yayi mugun sanyi ya koma Jos wurin iyalinsa cike da damuwa. Zayyan ya rasu a dalilin ceton ransa kuma iyalansa ma duka babu su. A satin yaje ya kai takardarsa ta barin aiki. A wurinsa rayuwar soja ba tasa bace. Asibiti ya koma neman aiki sai dai lokuta da dama idan ya ga yawaitar jini musamman idan hatsari ne jikinsa ya rinka rawa kenan. Likita da tsoron jini aiki bazai taba yiwuwa ba bisa dole ya hakura ya tsunduma cikin harkar siyasa ka'in da na'in.
***********
SABON SHAFI
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Asibitin Nasarawa aka tura su Awwab domin samun kwararren likitan ido. Da za'a basu daki yace dakin mutum daya yake bukata kada a hadata da kowa. Sunyi sa'a kuwa an samu. Dakin a gyare yake amma duk da haka ya dage sai an sake karkade shi an wanke toilet. Da ya ga matar zata yi masa gardama wai sai da safe zata sake zuwa ya bata dubu biyu. Kafin Mama ta iso da su Emzee da 'yan tarkacen bukata na kwana irinsu bargo da zanin gado an gyara dakin.