Sashe 145
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Falon bai kai girman dakin ba shi kuma royal chairs ne aka saka 3 sitter da one sitter guda biyu saboda wurin kada ya cushe. Ga katuwar wall tv da duk aka hada kayan kallo akan wani kayataccen tv stand. Centre table dinta da kananunsa na gefen kujeru duka masu kyau sai wani chest of drawer a karshen falon an jera plates da tarkacen kayan kitchen. Ana shigowa falon kofar dakin ce a farko daga dama sai kofar kitchen tana kallonsa daga hagu. Idan ka shiga kamar kada ka fita, gashi dai karami amma komai cikin girma da wadata akayi shi.
Zaman aikin karasa duk wani gyara da yayi saura su kayi. Emzee da Ibrahim ne a kitchen suka hada gas cooker da su fridge. Kafin isha bangaren amarya ya fito fes sai wani uban kamshi har bangaren Mami ana ji. Su Hajjo sunyi mamaki sosai ganin Mairama bata yi musu zancen akwai wani gidan a Katsina ba. Ba tayi kasa a gwiwa ba wurin nemanta inda ta ce musu bata da labari ko kadan itama. Zayyan ta fadawa yace shima bai sani ba. Sun tabbatar aikin su Mama ne wannan ta kirata kuwa ta ma kasa godiyar sai kuka tana cewa "Zainab Allah kada Ya taba bawa shaidan dama a kanmu. Kada Allah Ya bani ikon zama butulu a tsakaninki da Mami"
"Amin amma ki bar magana irin haka kada kisani kuka zan kira anjima" katse wayar tayi ta share kwalla. Me zasu cewa iyalin Zayyan. Gidansa da ya gida da guminsa da gadon mahaifiyarsa dungurugum ya baiwa DK kuma ya sayawa Ibrahim mota. Da shi da Daddy basu taba nuna wata alama da Hadir zai ji cewa bai kaisu arziki ba. Sun dauki kawunansu abu guda basa hangen komai sai soyayyar da suke yiwa juna.
Bayan sun koma ciki ne take fadawa Mami gobe ana gama budar kan bayan magariba sai a kai Radhiya.
Mami ta girgiza kai "a'a fa Zainab abinda biki bai kare ba, ko me za'ayi sai mun gama da Nijar dinnan kowa ya huta lokaci guda"
Mama ta kankance ido don bata da niyar chanza shawara "Mami kuji tsoron Allah, aure kwana nawa ana jawa yarona rai. Yo banda ma dai shi Awwab din anyi mai hakuri da tuni ba sai dai labari ya sha bamban ba. Kullum saka ido nake in ga tafiyar Radhiya ta sauya....."
Da sauri Mami ta mike "ba dai tariya kike so gobe ba? To a kaita dakinta gobe ba sai kin fara barambarama ba"
Shu'umar dariya Mama tayi "haka kawai don dai daga shi har ita ba wayis bane ta wannan fanin ga gabontar 'ya'yan fari da duk mun kwashi kunyarmu a hannu tun a Abuja"
Yousuf tun daga wurin dinner ya zarce da Arifah Nicon ya karbe wayarta sai gobe zasu tafi Nijar. Mom dinta tayi ta korafi Excellency kuwa yace yaro yayi masa daidai. Su basu yi lissafin halin da yaran zasu shiga ba kawai sunyi tsari yadda yayi musu.
Gidan tun safe aka tashi da aikace aikace saboda walima ce babba Mami ta shirya a farfajiyar gidan. 'Yan uwa na nesa da kusa sun taru. Daga shabiyu zuwa la'asar anyi kade-kade da raye-raye Rahima tun tana jin kunya da komawa baya har ta ware saboda Zayyana bata san bakunta ba. Duka kayan da Radhiya ke sakawa Mami ce ta tanada. Bayan la'asar atampa aka bata ta saka super exclusive dinkin sosai yayi mata kyau aka dora mata wata bakar alkyabba tasha ado sai sheki da daukar ido. Wurin zamanta daban an kawata shi ga kujeru a jere aka kira wata babbar malama tazo yin bayanai da nasiha game da zaman aure da hanyoyin samun kyakkyawan zama da miji. Radhiya jikin gabadaya yayi sanyi hawaye kawai take zubarwa don kalaman matar akwai shiga rai da tsoratarwa. Sai da magariba ta gabato sannan taron ya watse bayan addu'o'i daga bakin malamar.
Ciki aka koma ana alwala da sallah. Radhiya ta fito daga toilet kenan Mama ta shiga dakin ta kirata. Dakin Mami ta kaita babu kowa a ciki ta bata wani abu a cikin kofi mai zaki da wani dandano da bata gane ba.
"Maza shanye kuma kada a sake baki wani abu ki sha kada kizo cikinki yayi ciwo sun isa haka. Sannan ki zama cikin shiri idan anyi sallah zamu kaiki kyayi wanka a can don nan ko ina a cike yake"
"Ina?" Tace a firgice murya na rawa.
"Bangarenku mana"
Wani abu taji ya tsirga mata a ciki ta daure tace "Mama wane bangaren kuma?"
Daure fuska tayi ganin Radhiya ta firgice lokaci guda kafin ta tara mata mutane "ina kinsan cewa akwai dakin Awwab a gidannan"
Idanu cike taf da hawaye tace "eh"
"To nan aka gyara miki idan kunzo kinga babu ruwanku da takurawa Mami kuna da komai a can" cewar Mama tausayin Radhiyan ya soma kama ta.
"Amma ba. Ance. Ance sai mun dawo daga Nijar ko Mama?" Tace da sigar roko.
Kafadarta Mama ta dafa tace "Radhiya, aure kika yi ba kwana kika zo yi gidan Mami ba kema yanzu nan gidanki ne. Ina so ki cire tsoro kamar yadda kika ji nasihar malamar nan dazu kada ki bani kunya kinji ko 'yar albarka. Jeki kiyi sallar zan zo mu tafi, kuma banda kuka ki tabbatar kin daure takalminki da kyau dai.." ta kare da zolayarta.
Kasa daurewa tayi tana sallah tana hawaye. Yanzu shikenan sai kowa ya kwana a cikin gidan ita kuma a kaita dakin Hamma Awwab? Da an fada mata da wuri da ta shirya zuciyarta amma wannan bazatan ya shammaceta da yawa.
Sukuku haka tayi sallah ta idar harda su sharar hawaye. Kukanta yasa Rahima rasa walwala tazo ta rungumeta itama tana yi batare da taji dalilinsa ba. Zahra da Fauziyya ne suka shigo Zayyana ta kira su akan kukan su Radhiyan.
Zahra tace "amaryar Hamma me ya faru?"
Kara sautin kukan tayi "wai kaini za'ayi"
Da ido Fauziyya ta yiwa Zayyana da Rahima alamun su fita sannan ta kwashe da dariya "wai, wai, wai....kice yau za'a kwana ana goge janbaki. Gara kisa 24hours shine baya fita da wuri"
Zahra ma dai dariyar tayi Radhiya na kuka tace "sai na fadawa Hamma"
"Tuba nake anti amarya. Tashi muje in baki karatu kinji kanwata yayata"
A dakin Mami kuma Mama ta kira Awwab tace masa shima ya taho da shiri yanzu za'a kai amarya jiya sha'afa tayi bata fada masa ba.
"Ina za'a kuma kaita Mama?"
"Bangarenku mana mun karasa jeren tun jiya"
Wata irin murna ta kama shi yace "Allah Mama?"
Sai da tayi dariya tace "idan ma kayi nisa ni dai yanzu zan rakata kasanta da son shiga jama'a kada taji ka shiru ta dawo cikinmu"
Takalmansa yake sakawa lokacin a gefen gidan Baban Biyu inda sukayi sallar magariba yace mata "gani nan Mama....Mama nagode sosai" ya cigaba da zuba mata godiya sannan ya ajiye wayar ya taso Bilal ya fada masa a ina zai siyo abubuwan da ango ke shiga gida dasu.
**********
Tsokanar Radhiya Fauziyya take tun tana kuka ta dena wani abun ma sai sunyi dariya ita da Zahra. Sallamar Mama taji wadda ta tsinke mata zuciya ta tashi da sauri.
"Taso mu tafi"
"Wayyo Mama banyi sallama dasu Adda Zahra ba" tace a rikice.
Mami taji wani irin tausayinta domin tana kusa da Maman. Duk bakin Radhiya da dakewar zuciya yau babu.
Mama ta rungume hannu a kirgi "to ina nan yi musu sallamar"
Rungumesu ta shiga yi sai ta basu tausayi bare ma Fauziyya kukan take tayata.
Hannunta Mama ta janyo "muje kinji gobe da safe zan turo miki su ayi ta rungume-rungumen"
Mayafi kawai ta yafa ta saka wasu flat shoes masu dan uban kyau suka fito. Wata kanwar Ummi ce ta dauko akwatinta wanda bata san da zamansa ba duk cikin aikin Mami ne wannan kayan da ta dinka mata kala goma. Kayan kwalliya da underware daga cikin wanda ta taho dasu ne aka dibar mata aka zuba.
Suna fitowa bakin kofa Emzee na danno kai zai shigo. Ai yana ganin tana kuka ya fara tambaya hankali a tashe. Kanwarsu ta bangaren Badaru ce ta fada masa kaita za'ayi. Ya bata rai kuwa.
"Yanzu Mama ana kai kowa a mota amma Adda a kafa"
Hajjo ta kamo kunnensa "To sannu me taya bera bari ina zamu kaita da mota"
"Ni gaskiya ban yarda ba Mama don Allah bari na kaita a mota" yace yana turo musu baki.
Rahima murmushi kawai tayi ganin halayen Emzee mabambanta. Ta dai tabbatar baya hada kowa da yayarsa kuma baya boyewa ma.
Iyaye na masa fada ya kama hannunta ya rike "da so nayi na zagaye gidannan sai biyar dake a mota sannan a kaiki amma tunda sun ki muje na rakaki Addata"
Dariya ya basu ya fuske abinsa wai ai bata da kawaye shine dai babban abokin. Haka ya shige cikin mata abinsa har falonta aka wuce dakin da ita ana musu fatan alkhairi. Ko minti shabiyar basuyi ba suka tafi Mama tace mata tayi wanka akwai kaya a ciki ta nemi wanda bazai takurata ba ta saka.
**********
Tana jiyo hayaniyar mutane sama-sama daga main house din tayi kuri tana tunani wai yau ita ce a gidan nan a matsayin matar aure-matar Awwab. Ita ma bata da masaniya akan za'a ware musu wuri a gidan nan shiyasa take ta mamaki. Kanta ta bude ta karewa dakin kallo a take ya shiga ranta komai ya burgeta matuka. Ta tashi a hankali ta leka toilet, falo da kitchen zuciyarta fes.
Tunowa tayi da gargadin Mama akan tayi wanka ga turaruka da ta nuna mata na humra a showglass da kuma wasu a cikin akwatin da aka zuba mata kaya. Mikewa tayi ta cire kaya tayi sa'a akwai tawul biyu a bandakin kuma akwai heater ta bango a kunne. Wanka tayi kafin ta gama taji ana kiran isha ta dauro alwala ta fito.
Zaman aikin karasa duk wani gyara da yayi saura su kayi. Emzee da Ibrahim ne a kitchen suka hada gas cooker da su fridge. Kafin isha bangaren amarya ya fito fes sai wani uban kamshi har bangaren Mami ana ji. Su Hajjo sunyi mamaki sosai ganin Mairama bata yi musu zancen akwai wani gidan a Katsina ba. Ba tayi kasa a gwiwa ba wurin nemanta inda ta ce musu bata da labari ko kadan itama. Zayyan ta fadawa yace shima bai sani ba. Sun tabbatar aikin su Mama ne wannan ta kirata kuwa ta ma kasa godiyar sai kuka tana cewa "Zainab Allah kada Ya taba bawa shaidan dama a kanmu. Kada Allah Ya bani ikon zama butulu a tsakaninki da Mami"
"Amin amma ki bar magana irin haka kada kisani kuka zan kira anjima" katse wayar tayi ta share kwalla. Me zasu cewa iyalin Zayyan. Gidansa da ya gida da guminsa da gadon mahaifiyarsa dungurugum ya baiwa DK kuma ya sayawa Ibrahim mota. Da shi da Daddy basu taba nuna wata alama da Hadir zai ji cewa bai kaisu arziki ba. Sun dauki kawunansu abu guda basa hangen komai sai soyayyar da suke yiwa juna.
Bayan sun koma ciki ne take fadawa Mami gobe ana gama budar kan bayan magariba sai a kai Radhiya.
Mami ta girgiza kai "a'a fa Zainab abinda biki bai kare ba, ko me za'ayi sai mun gama da Nijar dinnan kowa ya huta lokaci guda"
Mama ta kankance ido don bata da niyar chanza shawara "Mami kuji tsoron Allah, aure kwana nawa ana jawa yarona rai. Yo banda ma dai shi Awwab din anyi mai hakuri da tuni ba sai dai labari ya sha bamban ba. Kullum saka ido nake in ga tafiyar Radhiya ta sauya....."
Da sauri Mami ta mike "ba dai tariya kike so gobe ba? To a kaita dakinta gobe ba sai kin fara barambarama ba"
Shu'umar dariya Mama tayi "haka kawai don dai daga shi har ita ba wayis bane ta wannan fanin ga gabontar 'ya'yan fari da duk mun kwashi kunyarmu a hannu tun a Abuja"
Yousuf tun daga wurin dinner ya zarce da Arifah Nicon ya karbe wayarta sai gobe zasu tafi Nijar. Mom dinta tayi ta korafi Excellency kuwa yace yaro yayi masa daidai. Su basu yi lissafin halin da yaran zasu shiga ba kawai sunyi tsari yadda yayi musu.
Gidan tun safe aka tashi da aikace aikace saboda walima ce babba Mami ta shirya a farfajiyar gidan. 'Yan uwa na nesa da kusa sun taru. Daga shabiyu zuwa la'asar anyi kade-kade da raye-raye Rahima tun tana jin kunya da komawa baya har ta ware saboda Zayyana bata san bakunta ba. Duka kayan da Radhiya ke sakawa Mami ce ta tanada. Bayan la'asar atampa aka bata ta saka super exclusive dinkin sosai yayi mata kyau aka dora mata wata bakar alkyabba tasha ado sai sheki da daukar ido. Wurin zamanta daban an kawata shi ga kujeru a jere aka kira wata babbar malama tazo yin bayanai da nasiha game da zaman aure da hanyoyin samun kyakkyawan zama da miji. Radhiya jikin gabadaya yayi sanyi hawaye kawai take zubarwa don kalaman matar akwai shiga rai da tsoratarwa. Sai da magariba ta gabato sannan taron ya watse bayan addu'o'i daga bakin malamar.
Ciki aka koma ana alwala da sallah. Radhiya ta fito daga toilet kenan Mama ta shiga dakin ta kirata. Dakin Mami ta kaita babu kowa a ciki ta bata wani abu a cikin kofi mai zaki da wani dandano da bata gane ba.
"Maza shanye kuma kada a sake baki wani abu ki sha kada kizo cikinki yayi ciwo sun isa haka. Sannan ki zama cikin shiri idan anyi sallah zamu kaiki kyayi wanka a can don nan ko ina a cike yake"
"Ina?" Tace a firgice murya na rawa.
"Bangarenku mana"
Wani abu taji ya tsirga mata a ciki ta daure tace "Mama wane bangaren kuma?"
Daure fuska tayi ganin Radhiya ta firgice lokaci guda kafin ta tara mata mutane "ina kinsan cewa akwai dakin Awwab a gidannan"
Idanu cike taf da hawaye tace "eh"
"To nan aka gyara miki idan kunzo kinga babu ruwanku da takurawa Mami kuna da komai a can" cewar Mama tausayin Radhiyan ya soma kama ta.
"Amma ba. Ance. Ance sai mun dawo daga Nijar ko Mama?" Tace da sigar roko.
Kafadarta Mama ta dafa tace "Radhiya, aure kika yi ba kwana kika zo yi gidan Mami ba kema yanzu nan gidanki ne. Ina so ki cire tsoro kamar yadda kika ji nasihar malamar nan dazu kada ki bani kunya kinji ko 'yar albarka. Jeki kiyi sallar zan zo mu tafi, kuma banda kuka ki tabbatar kin daure takalminki da kyau dai.." ta kare da zolayarta.
Kasa daurewa tayi tana sallah tana hawaye. Yanzu shikenan sai kowa ya kwana a cikin gidan ita kuma a kaita dakin Hamma Awwab? Da an fada mata da wuri da ta shirya zuciyarta amma wannan bazatan ya shammaceta da yawa.
Sukuku haka tayi sallah ta idar harda su sharar hawaye. Kukanta yasa Rahima rasa walwala tazo ta rungumeta itama tana yi batare da taji dalilinsa ba. Zahra da Fauziyya ne suka shigo Zayyana ta kira su akan kukan su Radhiyan.
Zahra tace "amaryar Hamma me ya faru?"
Kara sautin kukan tayi "wai kaini za'ayi"
Da ido Fauziyya ta yiwa Zayyana da Rahima alamun su fita sannan ta kwashe da dariya "wai, wai, wai....kice yau za'a kwana ana goge janbaki. Gara kisa 24hours shine baya fita da wuri"
Zahra ma dai dariyar tayi Radhiya na kuka tace "sai na fadawa Hamma"
"Tuba nake anti amarya. Tashi muje in baki karatu kinji kanwata yayata"
A dakin Mami kuma Mama ta kira Awwab tace masa shima ya taho da shiri yanzu za'a kai amarya jiya sha'afa tayi bata fada masa ba.
"Ina za'a kuma kaita Mama?"
"Bangarenku mana mun karasa jeren tun jiya"
Wata irin murna ta kama shi yace "Allah Mama?"
Sai da tayi dariya tace "idan ma kayi nisa ni dai yanzu zan rakata kasanta da son shiga jama'a kada taji ka shiru ta dawo cikinmu"
Takalmansa yake sakawa lokacin a gefen gidan Baban Biyu inda sukayi sallar magariba yace mata "gani nan Mama....Mama nagode sosai" ya cigaba da zuba mata godiya sannan ya ajiye wayar ya taso Bilal ya fada masa a ina zai siyo abubuwan da ango ke shiga gida dasu.
**********
Tsokanar Radhiya Fauziyya take tun tana kuka ta dena wani abun ma sai sunyi dariya ita da Zahra. Sallamar Mama taji wadda ta tsinke mata zuciya ta tashi da sauri.
"Taso mu tafi"
"Wayyo Mama banyi sallama dasu Adda Zahra ba" tace a rikice.
Mami taji wani irin tausayinta domin tana kusa da Maman. Duk bakin Radhiya da dakewar zuciya yau babu.
Mama ta rungume hannu a kirgi "to ina nan yi musu sallamar"
Rungumesu ta shiga yi sai ta basu tausayi bare ma Fauziyya kukan take tayata.
Hannunta Mama ta janyo "muje kinji gobe da safe zan turo miki su ayi ta rungume-rungumen"
Mayafi kawai ta yafa ta saka wasu flat shoes masu dan uban kyau suka fito. Wata kanwar Ummi ce ta dauko akwatinta wanda bata san da zamansa ba duk cikin aikin Mami ne wannan kayan da ta dinka mata kala goma. Kayan kwalliya da underware daga cikin wanda ta taho dasu ne aka dibar mata aka zuba.
Suna fitowa bakin kofa Emzee na danno kai zai shigo. Ai yana ganin tana kuka ya fara tambaya hankali a tashe. Kanwarsu ta bangaren Badaru ce ta fada masa kaita za'ayi. Ya bata rai kuwa.
"Yanzu Mama ana kai kowa a mota amma Adda a kafa"
Hajjo ta kamo kunnensa "To sannu me taya bera bari ina zamu kaita da mota"
"Ni gaskiya ban yarda ba Mama don Allah bari na kaita a mota" yace yana turo musu baki.
Rahima murmushi kawai tayi ganin halayen Emzee mabambanta. Ta dai tabbatar baya hada kowa da yayarsa kuma baya boyewa ma.
Iyaye na masa fada ya kama hannunta ya rike "da so nayi na zagaye gidannan sai biyar dake a mota sannan a kaiki amma tunda sun ki muje na rakaki Addata"
Dariya ya basu ya fuske abinsa wai ai bata da kawaye shine dai babban abokin. Haka ya shige cikin mata abinsa har falonta aka wuce dakin da ita ana musu fatan alkhairi. Ko minti shabiyar basuyi ba suka tafi Mama tace mata tayi wanka akwai kaya a ciki ta nemi wanda bazai takurata ba ta saka.
**********
Tana jiyo hayaniyar mutane sama-sama daga main house din tayi kuri tana tunani wai yau ita ce a gidan nan a matsayin matar aure-matar Awwab. Ita ma bata da masaniya akan za'a ware musu wuri a gidan nan shiyasa take ta mamaki. Kanta ta bude ta karewa dakin kallo a take ya shiga ranta komai ya burgeta matuka. Ta tashi a hankali ta leka toilet, falo da kitchen zuciyarta fes.
Tunowa tayi da gargadin Mama akan tayi wanka ga turaruka da ta nuna mata na humra a showglass da kuma wasu a cikin akwatin da aka zuba mata kaya. Mikewa tayi ta cire kaya tayi sa'a akwai tawul biyu a bandakin kuma akwai heater ta bango a kunne. Wanka tayi kafin ta gama taji ana kiran isha ta dauro alwala ta fito.