Sashe 75
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
An gama komai dreban Daddy ya tafi dauko masu fara sauka idan ya kaisu ya dawo daukar na biyun saboda motar tayi musu kadan kuma babu mai tuka ta Mama. Ibrahim sai laraba zai dawo shi kuma Emzee nasa zuwan sai kwana biyu kafin suna. Ya gama mita wai kiran me ake yi musu don za'ayi suna Ummi tace yaushe rabon da su taru lokaci guda duka. Kuma ma ana gama sunan Rugar Barkindo zasu je da Sumaila kafin Radhiya ta fara aikinta.
Su uku suka fito daga cikin airport din. Raji, Zahra da kuma Awwab da yake dauke da Femi. Mutan gida kowa yayi mamaki da murnar ganinsa. Yayi wani irin haske da kyau saboda kasar Ukraine akwai sanyi sosai. Ga girma da cika ido tamkar Major zamanin kuruciya. Dukkansu gidan Mama suka shiga ya mikawa Fauziyya Femi ya koma gefen Ummi da hannuwansa a mike yana jira ta ajiye masa baby Zayyan.
"Naki din, yanzu zaka zo Awwab sai dai in ganka kuma jiya ma munyi waya fa" tace tana bata rai.
"Ummi kin dena sona ne, a wayar ma fada kike yi min" yace yana dariya.
Sauran ma sai suka soma dariya ana tsokanar Ummi wai Mama tayi mata kwacen da.
"Ga sabo me zanyi da wannan katon nima. Na barwa Mama dama haka take so"
"Ke dai kawai don kinga munfi shiri yanzu shine zaki tashi hankalinki"
Sosai ta rinka zolayar Ummi ta kuwa hana shi baby din ya gama nacinsa ya hakura.
"Abincinku yana gidan Ummi. Zahra mijinki zai ci a can ko a kai masa dakin Awwab?" Mami ce tayi tambayar tana rike da Jawad da ya hanata zama yace wannan ya nuna wancan.
"Ni dai na koshi" Awwab yace ya tashi zai tafi daki.
Ummi ta tabe baki "kun gani irin halin nasa, mutum yaki cin abinci kullum koshi yake kira alhalin baici komai ba"
"Ummi ki rabu dashi yunwa ai ba kanwar uwa bace. Zata koro miki shi anjima"
Daga shi har su Zahran a gajiye suke. Dakinsa wanda aka gyara domin zuwan Raji suka shiga suyi wanka. Fauziyya ce ta yiwa Femi ya ware suna wasa da Jawad. Mami sai murmushi wadannan yaran jikokinta ne.
Sai karfe shida da rabi su Radhiya suka iso gidan suma a gajiye sai dai murna da doki bazasu bari taji da gajiyar jikin nata ba. Ita da Tante Nasara ne da Yousuf. Suna sauka daga mota tayi gidan Mama da sauri. Irin shigar da ta saba tayi na skirt mai fadi da riga iya cinya mai dogon hannu madaidaiciya wadda bata kamata ba bare ta fito da shape din jiki sai rolling din mayafi da tayi. Yousuf yana kallon yadda take sauri ya girgiza kai. Wani zubin kamar ta girma amma idan abin ya motsa sai tasa mutum dariyar dole. Yanzu ma saurin da take yi wai kada a gama rigata daukan baby ne.
Tunawa tayi da jan kunnen da Tante take yi mata akan rashin nutsuwa sai ta tsaya ta daidaita kanta sannan ta shiga da sallama. Mama tana zaune kasa hakuri tayi ta taso ta tarbi 'yar tata cike da farinciki.
"Radhiya kece kuwa? Bari dai maman taki tazo naji ko an baro min tawa a can ta kawo min ta bogi"
"Kai Mama" tace tana murmushi amma duk iya dauriyarta rashin ganin baby din yasa ta soma bata rai "Mama ina Daada?"
"Wai da gaske haka zaki rinka kiran sa?"
"Oui Maamon" Ta amsa da dariya tana mata salute suka sa dariya tare.
"Yana bayan Mami yanzu ta fita zata dawo am....."
Radhiya har ta kofa tafiyar da bata kai minti guda ba ta kaita gidan Mamin. Tana iya jiyo muryoyinsu Zayyana ta fada da sauri tana murna. Su duka Mami ce tace su fita a bar Mama tayi bacci ko ta huta dai.
Kan kace meye wannan sun cika gidan ba babba ba yaro daga kan Zahra har Zayyana. Murnar ganin juna suke yi sosai. Kowa yayi mamakin Radhiya ta canja sosai ta zama wata rabin baturiya. Ta dauki Jawad da Femi duka lokaci guda tana juyi dasu.
"To dai ku rage hayaniya kunga mijin Zahra yana ciki kada ku hana shi hutawa" Mami ta fada tana ficewa da baby a bayanta don bazata yarda suna wannan hayaniyar ta damka musu dan amana ba. Suje can su karata da nasu 'ya'yan tunda su da kwarinsu.
Zahra ta dora hannu a baki tana kunshe dariya "Hamma Awwab kai Mami, shi yafi kowa gudun hayaniya yanzu."
Dif Radhiya tayi gabanta na faduwa. Hamma Awwab yana cikin gidan bata sani ba. Da yaran a hannu ta juya zata fita ta rasa murna ce ko tsoro ko kuma bacin rai na shareta da yayi. Suna zuwa kofa Femi ya bare baki yana mikawa Zahra hannu.
"Tafi can nima bana yi da kai mai kyuya kawai. Kuma zaka ganni na goya Jawad ne na bashi chocolate" tace tana mikawa Zayyana shi tunda tafi kusa.
Kukansa da Raji yaji yasa shi bude kofar dakin Awwab kuma a lokacin ne tayi wannan maganar a kunnuwan Awwab din. Comb ne mai brush mai laushi yake sake kwantar da sumar kansa duk da yayi aski saisaye amma gashin ya soma fitowa. Dena brushing kan nasa yayi ya kallo kofar yayi sa'ar ganinta tana hararar Femi da ganin babansa yasa shi dariya.
Murmushin da baiyi niyya bane ya kwace masa yana kallon yadda take hararar yaro a gaban iyayensa kuma wai nan fushi ne kawai don yaki binta "Silly girl" ya furta a hankali idanunsa a kanta har ta fita daga gidan.
Ko da ta isa gidan Tante da Yousuf suna tare da Ummi suna cin abinci. Dukkansu dama yunwa suke ji tun a hanya. Wurin Ummi taje ta rungumeta tana dariya.
"Umminaaaa"
"Meye haka, tashi ni ki dagani" Ummi tace tana jin kunyar Tante ba don bata murna ta ganin 'yarta ta ba.
"Alheran rabu da ita kinji. Zuba abinci ki ci"
"Wanka zan fara yi. Ummi yaushe Emzee da Ibrahim zasu zo?"
"Kafin ki fara aikin in sha Allahu. Kiyi wankan sai kuci tare da su Zahra su ma basu ci ba muna gidan Zainab tun dazu ana hira"
"Ai sai an dawo da komai baya bari na shirya dai."
Dakinta ta wuce akwatunan Fauziyya da Zahra suna gefen inda Ummi ta tura mata nata. Su ukun a nan zasu kwana. Yousuf a dakin Emzee ita da Nasara a dakin Ummin. A can gidan Mami kuma Zayyana ce kawai sai Awwab da Raji.
Tana wanka tana tunanin wai Awwab yazo. Yaushe rabon su da haduwa. Gabanta har wani faduwa yake ta koma shiryawa a hankali. Duk yadda yace yana sonta ko sau daya bai nemeta a waya ba tunda ta tafi wai shi fushi. Kwafa tayi ita kadai. Ranta taji ya baci tayi siririn tsaki tana tazar gashinta da ya zarce kafadunta. Dama ita kanta akwai cika ga santsi shiyasa duk gyaran da take masa bai wuce amfani da shampoo masu kyau ba sai steaming da Tante take mata a shafe shi da mayuka. Tana daure shi yake kwanciya a kanta sai tayi rolling dinsa a keya ko tsakiya da ribbon. Ita da kitso sai sunzo Nigeria ko Nijar.
Doguwar riga ta saka ta wani yadi mai laushi anyi mata free style da dogon hannu. Karamin mayafi ta yafa bayan ta shafa hoda, kwalli da wani lip gloss light brown. Sassanyan body spray ta feshi jikinta dashi ta kuma saka turarensa a kayanta. Kamshinsa bashi da karfi very cool daidai da mata.
Ta bata lokaci sosai sai da tayi sallar magariba da isha ta fito. Fauziyya da Zahra ta gani da yaransu su Ummi suna gidan Mama har Tante.
"Kunci abincin?"
"Au wai da baki ci ba Radhiya? Shine kika makale a daki" Inji Zahra
Hira suka dasa suna yiwa juna tambayoyin yaushe gamo ta durkusa gaban kwanukan abincin da aka sauke a tsakar falon ta debi dambun yadda take jin zai isheta da farfesun a karamin bowl. Kan dinning table ta ajiye komai ta karkata kujerarta yadda zata ji dadin hira dasu Zayyana ta shigo tana waya da Emzee. Wuri ta samu ta zauna a kujerar kusa da Radhiya suka ji wannan deep voice din ta Awwab yana sallama.
Kowa ya amsa sallamar harda Yousuf da ya fito daga daki a lokacin amma Radhiya ta kasa bude baki kamar wadda ta hadiyi kota. Ko dago kai ma ta kasa yi tana rike da cokali a hannu tayi kasa da kanta. Zuciyarta na tsananta bugu.
Fuskar Awwab a sake yaje ya mikawa Yousuf hannu suka gaisa tare da fadawa juna sunayensu. Zama Yousuf yayi a kan daya daga kujerun falon suka gaisa da su Zahra.
Shi kuma Awwab ya tako a nutse zuwa dinning table din da yake kusa da bango daga bayan kujerar da Yousuf ya zauna.
"Bani wuri" yace da Zayyana yana mata nuni da kujerar da take zaune a kai. Da sauri ta tashi ta koma wurin su Fauziyya shi kuma ya zauna. Gabadaya ji tayi falon yayi mata kadan tamkar cikin akurki aka kulleta tare dashi. Bai ce mata komai ba ya karbi cokalin hannunta ya zuba farfesun akan dambun ya diba yasa a baki sannan ya mika mata. Sai a lokacin ta dago kanta suka hada ido. Babu wanda zuciya da gangar jikinsa bai aika masa da sako mai girma a tattare da dan uwansa ba. Sun chanja sosai shekara kusan uku ba yau ba. Sauke nata idon tayi da sauri ya sake mika mata spoon din.
Su uku suka fito daga cikin airport din. Raji, Zahra da kuma Awwab da yake dauke da Femi. Mutan gida kowa yayi mamaki da murnar ganinsa. Yayi wani irin haske da kyau saboda kasar Ukraine akwai sanyi sosai. Ga girma da cika ido tamkar Major zamanin kuruciya. Dukkansu gidan Mama suka shiga ya mikawa Fauziyya Femi ya koma gefen Ummi da hannuwansa a mike yana jira ta ajiye masa baby Zayyan.
"Naki din, yanzu zaka zo Awwab sai dai in ganka kuma jiya ma munyi waya fa" tace tana bata rai.
"Ummi kin dena sona ne, a wayar ma fada kike yi min" yace yana dariya.
Sauran ma sai suka soma dariya ana tsokanar Ummi wai Mama tayi mata kwacen da.
"Ga sabo me zanyi da wannan katon nima. Na barwa Mama dama haka take so"
"Ke dai kawai don kinga munfi shiri yanzu shine zaki tashi hankalinki"
Sosai ta rinka zolayar Ummi ta kuwa hana shi baby din ya gama nacinsa ya hakura.
"Abincinku yana gidan Ummi. Zahra mijinki zai ci a can ko a kai masa dakin Awwab?" Mami ce tayi tambayar tana rike da Jawad da ya hanata zama yace wannan ya nuna wancan.
"Ni dai na koshi" Awwab yace ya tashi zai tafi daki.
Ummi ta tabe baki "kun gani irin halin nasa, mutum yaki cin abinci kullum koshi yake kira alhalin baici komai ba"
"Ummi ki rabu dashi yunwa ai ba kanwar uwa bace. Zata koro miki shi anjima"
Daga shi har su Zahran a gajiye suke. Dakinsa wanda aka gyara domin zuwan Raji suka shiga suyi wanka. Fauziyya ce ta yiwa Femi ya ware suna wasa da Jawad. Mami sai murmushi wadannan yaran jikokinta ne.
Sai karfe shida da rabi su Radhiya suka iso gidan suma a gajiye sai dai murna da doki bazasu bari taji da gajiyar jikin nata ba. Ita da Tante Nasara ne da Yousuf. Suna sauka daga mota tayi gidan Mama da sauri. Irin shigar da ta saba tayi na skirt mai fadi da riga iya cinya mai dogon hannu madaidaiciya wadda bata kamata ba bare ta fito da shape din jiki sai rolling din mayafi da tayi. Yousuf yana kallon yadda take sauri ya girgiza kai. Wani zubin kamar ta girma amma idan abin ya motsa sai tasa mutum dariyar dole. Yanzu ma saurin da take yi wai kada a gama rigata daukan baby ne.
Tunawa tayi da jan kunnen da Tante take yi mata akan rashin nutsuwa sai ta tsaya ta daidaita kanta sannan ta shiga da sallama. Mama tana zaune kasa hakuri tayi ta taso ta tarbi 'yar tata cike da farinciki.
"Radhiya kece kuwa? Bari dai maman taki tazo naji ko an baro min tawa a can ta kawo min ta bogi"
"Kai Mama" tace tana murmushi amma duk iya dauriyarta rashin ganin baby din yasa ta soma bata rai "Mama ina Daada?"
"Wai da gaske haka zaki rinka kiran sa?"
"Oui Maamon" Ta amsa da dariya tana mata salute suka sa dariya tare.
"Yana bayan Mami yanzu ta fita zata dawo am....."
Radhiya har ta kofa tafiyar da bata kai minti guda ba ta kaita gidan Mamin. Tana iya jiyo muryoyinsu Zayyana ta fada da sauri tana murna. Su duka Mami ce tace su fita a bar Mama tayi bacci ko ta huta dai.
Kan kace meye wannan sun cika gidan ba babba ba yaro daga kan Zahra har Zayyana. Murnar ganin juna suke yi sosai. Kowa yayi mamakin Radhiya ta canja sosai ta zama wata rabin baturiya. Ta dauki Jawad da Femi duka lokaci guda tana juyi dasu.
"To dai ku rage hayaniya kunga mijin Zahra yana ciki kada ku hana shi hutawa" Mami ta fada tana ficewa da baby a bayanta don bazata yarda suna wannan hayaniyar ta damka musu dan amana ba. Suje can su karata da nasu 'ya'yan tunda su da kwarinsu.
Zahra ta dora hannu a baki tana kunshe dariya "Hamma Awwab kai Mami, shi yafi kowa gudun hayaniya yanzu."
Dif Radhiya tayi gabanta na faduwa. Hamma Awwab yana cikin gidan bata sani ba. Da yaran a hannu ta juya zata fita ta rasa murna ce ko tsoro ko kuma bacin rai na shareta da yayi. Suna zuwa kofa Femi ya bare baki yana mikawa Zahra hannu.
"Tafi can nima bana yi da kai mai kyuya kawai. Kuma zaka ganni na goya Jawad ne na bashi chocolate" tace tana mikawa Zayyana shi tunda tafi kusa.
Kukansa da Raji yaji yasa shi bude kofar dakin Awwab kuma a lokacin ne tayi wannan maganar a kunnuwan Awwab din. Comb ne mai brush mai laushi yake sake kwantar da sumar kansa duk da yayi aski saisaye amma gashin ya soma fitowa. Dena brushing kan nasa yayi ya kallo kofar yayi sa'ar ganinta tana hararar Femi da ganin babansa yasa shi dariya.
Murmushin da baiyi niyya bane ya kwace masa yana kallon yadda take hararar yaro a gaban iyayensa kuma wai nan fushi ne kawai don yaki binta "Silly girl" ya furta a hankali idanunsa a kanta har ta fita daga gidan.
Ko da ta isa gidan Tante da Yousuf suna tare da Ummi suna cin abinci. Dukkansu dama yunwa suke ji tun a hanya. Wurin Ummi taje ta rungumeta tana dariya.
"Umminaaaa"
"Meye haka, tashi ni ki dagani" Ummi tace tana jin kunyar Tante ba don bata murna ta ganin 'yarta ta ba.
"Alheran rabu da ita kinji. Zuba abinci ki ci"
"Wanka zan fara yi. Ummi yaushe Emzee da Ibrahim zasu zo?"
"Kafin ki fara aikin in sha Allahu. Kiyi wankan sai kuci tare da su Zahra su ma basu ci ba muna gidan Zainab tun dazu ana hira"
"Ai sai an dawo da komai baya bari na shirya dai."
Dakinta ta wuce akwatunan Fauziyya da Zahra suna gefen inda Ummi ta tura mata nata. Su ukun a nan zasu kwana. Yousuf a dakin Emzee ita da Nasara a dakin Ummin. A can gidan Mami kuma Zayyana ce kawai sai Awwab da Raji.
Tana wanka tana tunanin wai Awwab yazo. Yaushe rabon su da haduwa. Gabanta har wani faduwa yake ta koma shiryawa a hankali. Duk yadda yace yana sonta ko sau daya bai nemeta a waya ba tunda ta tafi wai shi fushi. Kwafa tayi ita kadai. Ranta taji ya baci tayi siririn tsaki tana tazar gashinta da ya zarce kafadunta. Dama ita kanta akwai cika ga santsi shiyasa duk gyaran da take masa bai wuce amfani da shampoo masu kyau ba sai steaming da Tante take mata a shafe shi da mayuka. Tana daure shi yake kwanciya a kanta sai tayi rolling dinsa a keya ko tsakiya da ribbon. Ita da kitso sai sunzo Nigeria ko Nijar.
Doguwar riga ta saka ta wani yadi mai laushi anyi mata free style da dogon hannu. Karamin mayafi ta yafa bayan ta shafa hoda, kwalli da wani lip gloss light brown. Sassanyan body spray ta feshi jikinta dashi ta kuma saka turarensa a kayanta. Kamshinsa bashi da karfi very cool daidai da mata.
Ta bata lokaci sosai sai da tayi sallar magariba da isha ta fito. Fauziyya da Zahra ta gani da yaransu su Ummi suna gidan Mama har Tante.
"Kunci abincin?"
"Au wai da baki ci ba Radhiya? Shine kika makale a daki" Inji Zahra
Hira suka dasa suna yiwa juna tambayoyin yaushe gamo ta durkusa gaban kwanukan abincin da aka sauke a tsakar falon ta debi dambun yadda take jin zai isheta da farfesun a karamin bowl. Kan dinning table ta ajiye komai ta karkata kujerarta yadda zata ji dadin hira dasu Zayyana ta shigo tana waya da Emzee. Wuri ta samu ta zauna a kujerar kusa da Radhiya suka ji wannan deep voice din ta Awwab yana sallama.
Kowa ya amsa sallamar harda Yousuf da ya fito daga daki a lokacin amma Radhiya ta kasa bude baki kamar wadda ta hadiyi kota. Ko dago kai ma ta kasa yi tana rike da cokali a hannu tayi kasa da kanta. Zuciyarta na tsananta bugu.
Fuskar Awwab a sake yaje ya mikawa Yousuf hannu suka gaisa tare da fadawa juna sunayensu. Zama Yousuf yayi a kan daya daga kujerun falon suka gaisa da su Zahra.
Shi kuma Awwab ya tako a nutse zuwa dinning table din da yake kusa da bango daga bayan kujerar da Yousuf ya zauna.
"Bani wuri" yace da Zayyana yana mata nuni da kujerar da take zaune a kai. Da sauri ta tashi ta koma wurin su Fauziyya shi kuma ya zauna. Gabadaya ji tayi falon yayi mata kadan tamkar cikin akurki aka kulleta tare dashi. Bai ce mata komai ba ya karbi cokalin hannunta ya zuba farfesun akan dambun ya diba yasa a baki sannan ya mika mata. Sai a lokacin ta dago kanta suka hada ido. Babu wanda zuciya da gangar jikinsa bai aika masa da sako mai girma a tattare da dan uwansa ba. Sun chanja sosai shekara kusan uku ba yau ba. Sauke nata idon tayi da sauri ya sake mika mata spoon din.