Sashe 82
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau da Radhiya akayi aikin breakfast ita da Ummi suna yi tana kara yi mata bayanin project dinta. Abin ya kayatar da Ummi matuka tace me zai hana tayi magana da Daddy sai a nema mata alfarmar samun adireshin wasu daga cikin matan da suka zauna tare a Sakkwato wadanda mazansu suka rasu ta saka su a sashen shirin nata da ta kira da (Hidden Heroes).
"Ummi kece ta farko a cikinsu sai dai bazan iya saka ki a ciki ba saboda kuka zamuyi ta yi" tace da kwalla a idanunta.
Da murmushinta mai ciwo tace "Allah Ya jikan Daadaa dinku. Halinku kadan ne da bambanci. Shi baya shagwaba irin wadda kika koyo wurin Nasara sai dai ya shagwaba wasu"
Dan tsalle tayi tana son hirar babanta "Ummi yana shagwabani?"
"Kamar ba gobe" ta amsa mata tana tuno rayuwarsu ta da murmushi na kufce mata.
"Kema yana shagwabaki ko?" Ta tsare Ummin da idanu tana daga gira daya da wani dan banzan murmushi.
"Kaniyarki, fita ki bani wuri" ta biyota da cokalin miya. Dariya ta saka ta gudu daki.
"Na fa zata ta kintsu ashe nutsuwar ta karya ce" Ummi ta cewa kanta ita kadai tana girgiza kai. Mai hali baya fasa halinsa.
Yau ma atampa ta saka amma riga da skirt. Ita kadai take juyi a gaban madubin bayan ta gama kwalliya ta karkata nan ta karkata can tana turo baki.
"Fita mana kije kiyi a gabansa sai ya fada miki inda yake bukatar gyara idan akwai"
Ta madubin ta harari Fauziyya kamar idanu zasu fado ta zagaya karbar Jawad zata shirya shi Fauziyyan tayi wanka sai ga Zahra kamar an korota ta shigo da sauri kana ganinta farkawarta kenan.
"Jama'a na shiga dubu a gidan nan yau"
"Me ya faru Adda?"
Kasa fada tayi wai saboda Radhiya ba aure gareta ba.
"Babu komai dai"
"Ina fa babu komai dazu Mami ta aiko Zayyana da Femi wai tana ta zuba ido jiya da daddare kije ki karbe shi taji shiru ko kinzo kin kwanta ne kin bar mata shi. Bai dade da komawa bacci ba yana dakin Ummi"
"Duk dad dinshi ya ja min" tace kamar tayi kuka.
Fauziyya ta zauna a gefen gadon kusa da ita harda rage murya za'ayi gulma "kwana kika yi a can tare dashi?"
Duka ta daka mata a cinya kafin tace "dawowa yayi fa duk cizon sauro yayi wani iri...daga hada masa ruwan wanka bacci ya daukeni"
"Allah Sarki...kinsan bacci babu ta yadda baya zuwa. Ina fata dai kinyi ya isheki" Fauziyya tace tana dariyar ta dago me ya sami yayartata.
Radhiya taji sun sakata a duhu ta kasa fahimtar me suke nufi ga son jin zancen na cinta tace "don Allah kuyi min bayani dalla dalla"
"Ke da wannan bayanin sai a gidan Hamma" Fauziyya ta sake yin dariya. Bakinta ya kara budewa ta zama mai tsokana sosai.
"Me? Aure zaiyi? To ni ina ruwana ai dai ba zuwa gidan zan rinka yi ba" tace tana bata rai.
"Nasan ba fahimta zakiyi ba dama. Shirya Jawad ga kayansa nan zanyi wanka."
Hannu ta mika zata dauki yaron ya zille ya koma wurin mamansa ta kuwa harare shi kamar sa'anta ta fice daga dakin tana mita.
"Yara ku cigaba da yi min kyuya sai na baku mamaki. 'Yan mata zan rinka haifa in hanaku aurensu"
"Allah Ya tashemu zaki fara ko, ke da wa kuma?" Ummi tace ta fito da Femi ya farka yana neman mamansa.
"Jawad mana Ummi. Wai ni suke yiwa kyuya shi da Femi."
"Baki iya yi musu yadda zasu sake dake bane. Harararsu fa take yi Ummi"
Faduwar gaba taji tun da ya fara magana. Tabbas taji wannan kamshin mai shiga ko ina a jikinta yana tasiri amma duk a zatonta ya shigo ya fita ne. Ashe yana tsaye ne a bayanta da kofin kunu a hannu. Diba yayi zai koma daki ta fito tana mita.
Tayi matukar kyau kayan sun kara fito da ita. Rashin sanin yana wurin karamin mayafi ta yafa da ya dan zame baya yadda gaban gashinta da ta daure da ribbon ya kwanta ya bayyana.
"Kuma gara ta koya tun wuri don ni dai babu mai kawo min ajiyar 'ya'ya" Ummi ta fada tana kokarin barin wurin.
"Ummi kawo shi ki gani" ta zura hannu zata karbi Femi dan albarka sai ya yarda "kin gani ko..."
Zahra ce ta bude kofar dakin a lokacin yana ganinta ya soma kuka yana mika hannu da zillo. Radhiya taji kamar zai fadi ta mika mata shi. Tana karbarsa yayi shiru harda dora kansa a kafada ta shiga shafa masa baya.
"Nima dai inzo in haifi nawa su rinka like min ina muku yanga"
Ummi kada kai tayi ta fita tana murmushi da taji me take cewa. Sai yanzu Mama tayi mata wayar baby ya tashi don Ummi bata tashinsa yin wanka sai dai ta jira shi wai duk cikin 'ya'yan nasu shi tafi so dole ayi masa yadda yake so ba takura.
"Waye ya fada miki yara masu likewa iyaye dadi ne dasu?"
"Ba gashi kuna gayunku ba ke da Maman Jawad"
"Allah Ya baki muna gefe ai musha kallo. Wa yaga Radhiya da baby" Zahra tace tana komawa dakin domin bawa Femi abinci.
Satar kallon Awwab tayi da yake tsaye a bakin kofar dakin Emzee tun dazu ya tokare kafarsa da bango ya jingina. Hanyar fita tayi ya dakatar da ita.
"Kinyi breakfast ne?"
"Bana jin yunwa" tace a takaice.
"Realy? Kwaikwayona kika soma yi kenan" yace yana matsowa inda take tsaye. Yadda take ganin yayi matukar kyau haka shima yake ganinta.
"Kai ba gashi zaka sha kunu ba" ta dan tura baki tana lumshe idanu.
"Na Yousuf ne..nima bana jin yunwa" ya sami kansa da cewa.
Kawai don kada ya yarda shi take kwaikwayo har ya fassarata ta dauko kofi a cikin wata drawer mai kyan tsari dake gefen dinning table ta zuba kunu.
Gefenta ya tsaya ya rage murya tana jin wani abu na kwasarta "ki dena yi mana addu'ar yara masu kyuya don nima ina da son kulawa kada su rinka shiga lokacina"
Ta riga ta gama zuba kunun ta ajiye flask din da babu abinda zai hana ta sake shi yadda ta saki teaspoon din hannunta jiki na rawa saboda mamakin kalamansa.
"Careful and please kisa babban mayafi" yace yana kashe mata ido sannan ya ajiye mata kofin hannunsa ya dauki wanda ta zuba yayi gaba ya barta da bude baki.
Jiki a sake ta zauna zuciyarta da gangar jikinta suna neman karkata akalar tunaninta daga basarwa da jan aji zuwa sake fadawa cikin soyayyar Hammanta da bata taba fita a ranta ba. Ta dade da fahimtar manufar Yousuf a kanta amma sai tayi kamar bata sani ba saboda bata jin akwai wanda zata iya sakawa a gurbin da Awwab yake zaune cikin zuciyarta. Kwantar da kanta tayi akan table din tana bubbuga kafa "wai ni nake wahalar dashi ko shi yake wahalar dani...ahhhhhhh sai na rama nima"
Ta fuskanci da gangan ma ya fadi maganar don yasan me zata yi mata. Shikenan a tafi a haka zata sake dammara don so take taji ya fada da bakinsa yana sonta kafin ya koma aiki. Kai so take ya sota fiye da yadda a baya yayi ikirari. Yaji ta a ransa kamar yadda take jinsa a nata. Kwalla taji ta taru a idonta...soyayyar da take yiwa Awwab kamar tafi karfin kirjinta take ji lokuta da dama. Amma shine ya iya shareta duk tsahon lokacin nan kawai don tabi umarnin Ummi a abinda yake gyara ga zumuntar danginsu. Don dai yayi sa'a tana son shi ne amma ba hakura zata yi ba idan ba sai ta rama. Ta nanatawa kanta kafin ta dauki kunun da ya ajiye mata ta shanye duk da ya huce sai dumi kawai.
Karfe uku suka firfito Daddy yace su biya har Asokoro gidan Plateau state government house su gaishe da maman Arifah da take ta cigiyarsu. Taron matan gwamnoni ta taho Arifah tayi mata rakiya.
Dakin Ummi taje shiryawa ta samu ta sanar da Tante gidan wa zasu je fa.
"Kada kice min tsoronsu kike ji saboda abinda ya taba hadaku"
"Ni bana son zuwa ne kawai" tace a sanyaye da gaske tana jin karayar zuciya.
"Ina sojan 'yata ta shiga ta bar min wannan mai tsoron? Sunyi zaton suna da abinda zai kaiki kwadayi ne ina ga tun farko shiyasa suka kara rainaki."
"Duk fa akan Ghazalatun nan ne"
"Ai da baifi da ba amma Mairama tayi musu kawaici don a zauna lafiya. Ki saki jikinki in kunje idan ba haka ba za'ayi aurenku ne kina kin shiga dangin miji?"
Shagwabar ce ta motsa tace "Ni nace zan aure shi ne Tante?"
"Baki ce ba shiyasa tunda na kula Yousuf dina na sonki zan fadawa Papa"
Tashi tayi da sauri zata gudu Nasara ta rinka dariya tace ta saka kayanta ta gani. Tana taimaka mata ta shirya tana bata sirrikan sake janyo Awwab gareta "idan na gaji da gulmar taku zaki wayi gari watarana kawai a kaiki gidansa an daura aure kuna bacci"
"Kamar wata 'yar tsana"
"Yi sauri kafin Mairama ta shigo ta fara mana fada daga ni har ke"
Abaya ce ta gani a fada kalar lilac mai ado ruwan madara. Duwatsun jikinta kadan ne ba irin mai daukar ido daga nesa ba an jera su sunyi zagaye zagaye daga wuya har kasa a tsaye ta tsakiya. Gefen mayafin ma haka yake sai dai kafin tayi rolling sai da daura wani karamin dankwali saboda wancan yana da santsi kada ya zame ga maikon kanta. Kayan kwaliyar Laura Mercier take amfani dasu. Tayi light make up dinta tasa janbaki nude bayan tayi lining lebenta da lip liner purple. Sai ya tashi ya bada wata kala mai kyau. Wani killer smile ta saki tana kallon Tante tana gode mata a ranta. Matar nan ba karamin kulawa da gyara take bata ba. 'Ya take yi da ita da zuciya daya shiyasa itama ta bata matsayin da ya kamaceta na uwa.
"Ummi kece ta farko a cikinsu sai dai bazan iya saka ki a ciki ba saboda kuka zamuyi ta yi" tace da kwalla a idanunta.
Da murmushinta mai ciwo tace "Allah Ya jikan Daadaa dinku. Halinku kadan ne da bambanci. Shi baya shagwaba irin wadda kika koyo wurin Nasara sai dai ya shagwaba wasu"
Dan tsalle tayi tana son hirar babanta "Ummi yana shagwabani?"
"Kamar ba gobe" ta amsa mata tana tuno rayuwarsu ta da murmushi na kufce mata.
"Kema yana shagwabaki ko?" Ta tsare Ummin da idanu tana daga gira daya da wani dan banzan murmushi.
"Kaniyarki, fita ki bani wuri" ta biyota da cokalin miya. Dariya ta saka ta gudu daki.
"Na fa zata ta kintsu ashe nutsuwar ta karya ce" Ummi ta cewa kanta ita kadai tana girgiza kai. Mai hali baya fasa halinsa.
Yau ma atampa ta saka amma riga da skirt. Ita kadai take juyi a gaban madubin bayan ta gama kwalliya ta karkata nan ta karkata can tana turo baki.
"Fita mana kije kiyi a gabansa sai ya fada miki inda yake bukatar gyara idan akwai"
Ta madubin ta harari Fauziyya kamar idanu zasu fado ta zagaya karbar Jawad zata shirya shi Fauziyyan tayi wanka sai ga Zahra kamar an korota ta shigo da sauri kana ganinta farkawarta kenan.
"Jama'a na shiga dubu a gidan nan yau"
"Me ya faru Adda?"
Kasa fada tayi wai saboda Radhiya ba aure gareta ba.
"Babu komai dai"
"Ina fa babu komai dazu Mami ta aiko Zayyana da Femi wai tana ta zuba ido jiya da daddare kije ki karbe shi taji shiru ko kinzo kin kwanta ne kin bar mata shi. Bai dade da komawa bacci ba yana dakin Ummi"
"Duk dad dinshi ya ja min" tace kamar tayi kuka.
Fauziyya ta zauna a gefen gadon kusa da ita harda rage murya za'ayi gulma "kwana kika yi a can tare dashi?"
Duka ta daka mata a cinya kafin tace "dawowa yayi fa duk cizon sauro yayi wani iri...daga hada masa ruwan wanka bacci ya daukeni"
"Allah Sarki...kinsan bacci babu ta yadda baya zuwa. Ina fata dai kinyi ya isheki" Fauziyya tace tana dariyar ta dago me ya sami yayartata.
Radhiya taji sun sakata a duhu ta kasa fahimtar me suke nufi ga son jin zancen na cinta tace "don Allah kuyi min bayani dalla dalla"
"Ke da wannan bayanin sai a gidan Hamma" Fauziyya ta sake yin dariya. Bakinta ya kara budewa ta zama mai tsokana sosai.
"Me? Aure zaiyi? To ni ina ruwana ai dai ba zuwa gidan zan rinka yi ba" tace tana bata rai.
"Nasan ba fahimta zakiyi ba dama. Shirya Jawad ga kayansa nan zanyi wanka."
Hannu ta mika zata dauki yaron ya zille ya koma wurin mamansa ta kuwa harare shi kamar sa'anta ta fice daga dakin tana mita.
"Yara ku cigaba da yi min kyuya sai na baku mamaki. 'Yan mata zan rinka haifa in hanaku aurensu"
"Allah Ya tashemu zaki fara ko, ke da wa kuma?" Ummi tace ta fito da Femi ya farka yana neman mamansa.
"Jawad mana Ummi. Wai ni suke yiwa kyuya shi da Femi."
"Baki iya yi musu yadda zasu sake dake bane. Harararsu fa take yi Ummi"
Faduwar gaba taji tun da ya fara magana. Tabbas taji wannan kamshin mai shiga ko ina a jikinta yana tasiri amma duk a zatonta ya shigo ya fita ne. Ashe yana tsaye ne a bayanta da kofin kunu a hannu. Diba yayi zai koma daki ta fito tana mita.
Tayi matukar kyau kayan sun kara fito da ita. Rashin sanin yana wurin karamin mayafi ta yafa da ya dan zame baya yadda gaban gashinta da ta daure da ribbon ya kwanta ya bayyana.
"Kuma gara ta koya tun wuri don ni dai babu mai kawo min ajiyar 'ya'ya" Ummi ta fada tana kokarin barin wurin.
"Ummi kawo shi ki gani" ta zura hannu zata karbi Femi dan albarka sai ya yarda "kin gani ko..."
Zahra ce ta bude kofar dakin a lokacin yana ganinta ya soma kuka yana mika hannu da zillo. Radhiya taji kamar zai fadi ta mika mata shi. Tana karbarsa yayi shiru harda dora kansa a kafada ta shiga shafa masa baya.
"Nima dai inzo in haifi nawa su rinka like min ina muku yanga"
Ummi kada kai tayi ta fita tana murmushi da taji me take cewa. Sai yanzu Mama tayi mata wayar baby ya tashi don Ummi bata tashinsa yin wanka sai dai ta jira shi wai duk cikin 'ya'yan nasu shi tafi so dole ayi masa yadda yake so ba takura.
"Waye ya fada miki yara masu likewa iyaye dadi ne dasu?"
"Ba gashi kuna gayunku ba ke da Maman Jawad"
"Allah Ya baki muna gefe ai musha kallo. Wa yaga Radhiya da baby" Zahra tace tana komawa dakin domin bawa Femi abinci.
Satar kallon Awwab tayi da yake tsaye a bakin kofar dakin Emzee tun dazu ya tokare kafarsa da bango ya jingina. Hanyar fita tayi ya dakatar da ita.
"Kinyi breakfast ne?"
"Bana jin yunwa" tace a takaice.
"Realy? Kwaikwayona kika soma yi kenan" yace yana matsowa inda take tsaye. Yadda take ganin yayi matukar kyau haka shima yake ganinta.
"Kai ba gashi zaka sha kunu ba" ta dan tura baki tana lumshe idanu.
"Na Yousuf ne..nima bana jin yunwa" ya sami kansa da cewa.
Kawai don kada ya yarda shi take kwaikwayo har ya fassarata ta dauko kofi a cikin wata drawer mai kyan tsari dake gefen dinning table ta zuba kunu.
Gefenta ya tsaya ya rage murya tana jin wani abu na kwasarta "ki dena yi mana addu'ar yara masu kyuya don nima ina da son kulawa kada su rinka shiga lokacina"
Ta riga ta gama zuba kunun ta ajiye flask din da babu abinda zai hana ta sake shi yadda ta saki teaspoon din hannunta jiki na rawa saboda mamakin kalamansa.
"Careful and please kisa babban mayafi" yace yana kashe mata ido sannan ya ajiye mata kofin hannunsa ya dauki wanda ta zuba yayi gaba ya barta da bude baki.
Jiki a sake ta zauna zuciyarta da gangar jikinta suna neman karkata akalar tunaninta daga basarwa da jan aji zuwa sake fadawa cikin soyayyar Hammanta da bata taba fita a ranta ba. Ta dade da fahimtar manufar Yousuf a kanta amma sai tayi kamar bata sani ba saboda bata jin akwai wanda zata iya sakawa a gurbin da Awwab yake zaune cikin zuciyarta. Kwantar da kanta tayi akan table din tana bubbuga kafa "wai ni nake wahalar dashi ko shi yake wahalar dani...ahhhhhhh sai na rama nima"
Ta fuskanci da gangan ma ya fadi maganar don yasan me zata yi mata. Shikenan a tafi a haka zata sake dammara don so take taji ya fada da bakinsa yana sonta kafin ya koma aiki. Kai so take ya sota fiye da yadda a baya yayi ikirari. Yaji ta a ransa kamar yadda take jinsa a nata. Kwalla taji ta taru a idonta...soyayyar da take yiwa Awwab kamar tafi karfin kirjinta take ji lokuta da dama. Amma shine ya iya shareta duk tsahon lokacin nan kawai don tabi umarnin Ummi a abinda yake gyara ga zumuntar danginsu. Don dai yayi sa'a tana son shi ne amma ba hakura zata yi ba idan ba sai ta rama. Ta nanatawa kanta kafin ta dauki kunun da ya ajiye mata ta shanye duk da ya huce sai dumi kawai.
Karfe uku suka firfito Daddy yace su biya har Asokoro gidan Plateau state government house su gaishe da maman Arifah da take ta cigiyarsu. Taron matan gwamnoni ta taho Arifah tayi mata rakiya.
Dakin Ummi taje shiryawa ta samu ta sanar da Tante gidan wa zasu je fa.
"Kada kice min tsoronsu kike ji saboda abinda ya taba hadaku"
"Ni bana son zuwa ne kawai" tace a sanyaye da gaske tana jin karayar zuciya.
"Ina sojan 'yata ta shiga ta bar min wannan mai tsoron? Sunyi zaton suna da abinda zai kaiki kwadayi ne ina ga tun farko shiyasa suka kara rainaki."
"Duk fa akan Ghazalatun nan ne"
"Ai da baifi da ba amma Mairama tayi musu kawaici don a zauna lafiya. Ki saki jikinki in kunje idan ba haka ba za'ayi aurenku ne kina kin shiga dangin miji?"
Shagwabar ce ta motsa tace "Ni nace zan aure shi ne Tante?"
"Baki ce ba shiyasa tunda na kula Yousuf dina na sonki zan fadawa Papa"
Tashi tayi da sauri zata gudu Nasara ta rinka dariya tace ta saka kayanta ta gani. Tana taimaka mata ta shirya tana bata sirrikan sake janyo Awwab gareta "idan na gaji da gulmar taku zaki wayi gari watarana kawai a kaiki gidansa an daura aure kuna bacci"
"Kamar wata 'yar tsana"
"Yi sauri kafin Mairama ta shigo ta fara mana fada daga ni har ke"
Abaya ce ta gani a fada kalar lilac mai ado ruwan madara. Duwatsun jikinta kadan ne ba irin mai daukar ido daga nesa ba an jera su sunyi zagaye zagaye daga wuya har kasa a tsaye ta tsakiya. Gefen mayafin ma haka yake sai dai kafin tayi rolling sai da daura wani karamin dankwali saboda wancan yana da santsi kada ya zame ga maikon kanta. Kayan kwaliyar Laura Mercier take amfani dasu. Tayi light make up dinta tasa janbaki nude bayan tayi lining lebenta da lip liner purple. Sai ya tashi ya bada wata kala mai kyau. Wani killer smile ta saki tana kallon Tante tana gode mata a ranta. Matar nan ba karamin kulawa da gyara take bata ba. 'Ya take yi da ita da zuciya daya shiyasa itama ta bata matsayin da ya kamaceta na uwa.