Sashe 44
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tabdi, yo ni malamin makaranta ba sai dai na zane shi da dorinarsa ba. Tsorona zai rinka ji"
Fauziyya da ta saka musu ido ita da Awwab tun jiya kuma take fatan hakan tace "ina jin zaki fi dacewa da dreban jirgin sama"
Mami da Zainab har Mairama sai su ka yi murmushi. Ko dai Fauziyyan ta ga wata alama ne take hasashen abinda suke shiryawa. Awwab da yake shan ruwa cire kofin yayi yana son jin amsarta. Abinka da 'Yar soja ta hade rai "ke kadai ce bakya sona Adda Fauziyya. Me zanyi da dreba sai kace ta kare min?"
Kowa yayi shiru yana kallon Awwab da ya zuba mata idanu harda Ghazalatu da misalin na Fauziyya ya kona mata rai. Bata san suna yi ba bare ta gyara zancen.
Zahra ce ta tace "mun ganku a rana ke da Hamma Awwab tunda shima dreban jirgin ne"
Ba arziki Radhiya ta tashi yana tsaye ya harde hannuwansa a kirji. Tayi zaton zaiyi fushi sai ta ga shi ya fara dariya kafin sauran "wato mu sai ta karewa mace za ta auremu ko"
"Wayo Adda Fauziyya tayi min ba haka nake nufi ba. Maimakon tace pilot yadda zan fahimta"
"Sannu Queen Elizabeth wato sai anyi turanci zaki fahimta" Ibrahim yace.
"Ka kiyayeni Surbajo" A dolensa yayi shiru da yaji abin zai dawo kansa.
Tsokanarta suka cigaba da yi tana karewa kanta. Awwab yana kallon Ghazalatu yace da Radhiya "ki shirya zata kare miki kwanannan kuwa don sai kin auri pilot. Kafin nan kuma ki zamarwa matata 'yar aiki"
Mama da Zainab suka kalli juna suna gyada kai da murmushi. Bakin mota suka firfito Mami da Ummi zasu bi karamar motar sauran kowa yace bus din da Awwab zai tuka zasu shiga. Radhiya da jikinta yayi sanyi tana jin babu dadi akan maganar da tayi tace ita ma motarsu zata shiga sai ta zauna a gaba.
"Koma cikin 'yan uwanki Radhiya" Zainab tace tana turata bakin daya motar.
Awwab ta kalla ko zaiyi magana sai ta kula hirarsa kawai yake yi da Ghazalatu. Juyowa yayi ya kalli Radhiya duk ta zama wata salihar karfi da yaji "ina zuwa" ya cewa Ghazalatu ya taho inda take tsaye a jikin motar.
"Zo in nuna miki wani abu"
"Wai ba fushi kayi da abinda nace ba kake yi min magana"
Murmushi yayi "Silly girl, kawai sai nayi fushi bayan nasan ta kusa kare miki kwanannan...auren dreba ba fashi"
"Shine ka barni inata damuwa, kuma a gaba zan zauna inyi ta ganinka tunda yau zaku dawo"
Wurin wata katuwar fulawa inda Ghazalatu ke tsaye suka nufa. Suna jiran iyayensu su gama maganar da suke yi su dau hanya ne shiyasa basu tafi ba.
"Dama babu mai zama wurinki ne nima inyi ta kallonki"
Dariya tayi fuskar Ghazalatu ta hade tsaf da kishi. Awwab yasan me yake bata mata rai don yanzu ta gama fada masa ita bata son yadda yake yiwa Alheran dinnan bayan ba karamar yarinya bace. Domin ya kwantar mata da hankali yaje ya kira ta.
"My G, ga Alheran kanwata. Alheran ga Ghazalatu kanwata kuma matar da zan aura"
Sai yanzu hankalin Ghazalatu ya kwanta sosai. Ta kurawa Radhiya ido sai ta ga yarinyar ko a jikinta sai ma dariyar ta take yi fuskarta ta tana wani annuri.
Dage girrarta duka biyun ta rinka yi yadda ta saba idan zata yi tsokana
" Eyye eyye Hamma shine kace zanyi aiki a gidanka? Naji zan rinka tayata indai itace matar"
"Bana bukatar house girl so kiyi zamanki" Ghazalatu tace tana shan kamshi.
Fuskar Awwab kadai zaka kalla kasan kalaman basuyi masa ba.
"House girl?" Yace yana kankance idanu.
Ta fuskanci ransa ne ya baci sai ta wayance "naji kace za tayi min aiki ne dazu"
"Lallai wannan 'yar wulakanci ce" Radhiya tace a ranta. Ita bata san maganar wasa bane da zata yi tunanin da gaske aiki zata je yi mata. Hamma Awwab yafi karfin komai a wurinta tunda yake son Umminta da babanta da ita kanta. Kuma ba wani abu bane a wurinta ta taya matarsa aiki amma wallahi ba dai taje a house girl ba. Idan bata gwaba mata magana ko yaya bane tasan bazata ji dadi ba shiyasa ta ajiye katon murmushi a fuskarta tace "ko babu albashi zanyi miki aikin ma, kinsan mu 'yan kauye bamu san komai ba sai bautawa 'yan birni"
"No ki barshi fa bana bukata, idan ina so Yayana zai nemo min"
" Yes dai inzo inyi ko babu komai zan hutar da Hammana barnar kudi"
Hannuwansa ya zuba a aljihu yana kallon ikon Allah. Rigima ke neman tashi tsakaninsu daga su gaisa.
Daure fuska yayi yace "ku wuce ku shiga mu tafi"
Suna zuwa bakin motar Ibrahim zai bude gaba ya shiga saboda yana son Awwab ya koya masa tuki Ghazalatu ta riga shi budewa itama tana son zama kusa da masoyinta. Radhiya da ta fisu iyawa tayi sauri ta shige ta kofar bayan ta haura gaba. Awwab kansa sai ganinta yayi ta kusa fado masa garin sauri. Gyara zamanta tayi ta ballawa Ghazalatu da Ibrahim harara suna tsaye suna kallon abinda tayi.
"Ni dama ga wurina can kusa da Zeezee" Ibrahim yace yana shiga bayan inda Emzee ke yi masa dariya.
Ghazalatu ta kalli Awwab tana jira yayi magana "kace ta koma baya ina son muyi magana"
"Idan muna dawowa sai ki zauna a nan din kinji."
Tsabar bakinciki ji tayi kamar tasa ihu. Mami daga cikin tasu motar tace ta shiga su tafi rana tana kara yi. Hararar Radhiya tayi ita kuma tayi mata gwalo.
"Bansan mutum nayi ba sai naji a jikina"
"Alheran" taji yace muryarsa a dake sannan ya kalli Ghazalatu da take ta cika tana batsewa "ki shiga ki zauna mu tafi"
Daurewar da yayi yasa ta shige ba don ta hakura ba. Radhiya da take kusa dashi kuwa ji tayi kamar ta koma baya ita ma. Tukinsa kawai yake yi wanda baya masa dadi saboda bin bayan Abdallah da dole sai yayi tunda bai san hanya ba.
Motar duk sai tayi musu shiru mai bakin tsoro ya hanata magana Zayyana har ta soma gyangyadi a jikin Zahra. Su basu ma san me yake faruwa ba sai Ibrahim da yake tunanin saboda zaman gaba ne kawai.
Can dai taji shirun ya isheta ta dago a hankali ta saci kallonsa. Titi dai yake kallo har yanzu babu wannan sakin fuskar.
"Hamma" Radhiya ta kira sunansa a tausashe.
"Kar ki dameni please"
Shiru tayi ran sojoji ya baci. Ita kadai zaiyi fushi da ita bai ji masoyiyar tasa tana kiranta housegirl ba. Tura baki tayi ta juya duk jikinta tana kallon waje. Shima satar kallonta yayi yayi gajeren murmushi. Da gaske dai Alheran dinsa bata chanja ba sai ma abinda yayi gaba. Su mata abin rigima baya yi musu kadan ya kula. Su biyun kowa matsayinta daban to me ya kawo rigimar. Ko don Ghazalatu tace mata house girl? Shima kalmar bata yi masa dadi ba. Duka su biyun sai yayi aikin basu hakuri kenan. Haka kawai zasu tayar masa da hankali kamar wasu kishiyoyi. Ta mudubi ya hango Ghazalatu ita ma fuska babu wakwala kamar ma kuka take shirin yi. A take ya jinjinawa masu mata biyu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Sun isa Sumaila karfe biyu na rana a gajiye saboda tashin wuri da suka yi. Emzee ne ya koma jagora da suka shigo garin shiyasa tasu motar take gaba. Awwab ba tsayawa Emzee din ya fita da sauri saboda magana da yake son yi wa Ummin tasu. Gefe ya ja ta ana kokarin fitowa da kayan da ita kanta bata san da zamansu ba a boot.
"Ummi wai kuwa sun san zamu zo da baki?" Yace yana rage murya.
"Na fadawa Innawuro da ta kira nace ta sanar dasu tunda kaga ba waya gareni ba. Menene?"
Da damuwa a fuskarsa yace "kada muje a rasa abinda za'a basu nasan bazaki ji dadi ba"
Murmushi Mairama tayi. Zayyan dinta akwai hankali da nutsuwa ga zurfin tunani. Rashin abin tarbar baki tabbas zai iya faruwa don tasan halin gidan nasu "to yanzu me ya kamata ayi?"
"Idan kina da kudi kawo naje na siyo gurasa da tsire kawai"
Karamar jakarta ta mika masa. Dubu uku ya cire cikin kudin da Ardo ya bata ne da zasu taho. Ya tafi tana ta masa addu'a a zuciyarta.
Radhiya kuma ta kama kofa za ta bude Awwab ya danna central lock. A zuciye ta juyo "bude min"
"Ko nima balotellin zaki yi min ne? Zai fi miki sauki akan wannan juya idanun" bayansa ya juya "Ghazalatu zauna magana zamuyi"
Murtuke fuska tayi itama ya kallesu ya tabe baki. Mata, mata halinku sai ku.
Su Zayyana duk sun fita sun bi bayan iyayensu cikin gidan. Basu san me yasa ya tsayar da su Radhiya ba amma ko ma meye tabbas basu ga alamun wasa a tare da yayan nasu ba.
"Kun gama fushin ko har yanzu da saura?"
Ghazalatu dama jira take yi "don na biyoka shine zaka wulakantani akan wannan yarinyar kamar wata kishiyata? Tunda muka zo sai kayi mata magana sau uku baka yi min daya ba. Sannan nazo shiga gaba ta shige duka ka kyaleta. Idan wani abu ne tsakaninku gara ka fada min da wuri na san matsayina. Amma bazai yiwu ta rinka jin kanta kamar wata a wurinka ba tana neman shiga tsakaninmu"
"Kin gama? To bari kiji in fada miki. Alheran wata ce a wurina Ghazalatu kuma bazan yarda kici mata mutumci ba. She is my sister kamar yadda na dauki su Zahra haka ita ma na dauketa. Idan ma kishi zakiyi ba da ita zakiyi ba. Ki bari sai kin hadu da wadda take da matsayi irin naki a wurina"
Dazu gani take wannan Ghazalatun take ko wa tayi mata rashin mutumci amma maganar Awwab ta yanzu tafi kona mata rai akan komai duk da cewa gaskiya ce ya fada. Ita din kanwa take a wurinsa amma meyasa kalaman nasa suka yi mata zafi haka.
Fauziyya da ta saka musu ido ita da Awwab tun jiya kuma take fatan hakan tace "ina jin zaki fi dacewa da dreban jirgin sama"
Mami da Zainab har Mairama sai su ka yi murmushi. Ko dai Fauziyyan ta ga wata alama ne take hasashen abinda suke shiryawa. Awwab da yake shan ruwa cire kofin yayi yana son jin amsarta. Abinka da 'Yar soja ta hade rai "ke kadai ce bakya sona Adda Fauziyya. Me zanyi da dreba sai kace ta kare min?"
Kowa yayi shiru yana kallon Awwab da ya zuba mata idanu harda Ghazalatu da misalin na Fauziyya ya kona mata rai. Bata san suna yi ba bare ta gyara zancen.
Zahra ce ta tace "mun ganku a rana ke da Hamma Awwab tunda shima dreban jirgin ne"
Ba arziki Radhiya ta tashi yana tsaye ya harde hannuwansa a kirji. Tayi zaton zaiyi fushi sai ta ga shi ya fara dariya kafin sauran "wato mu sai ta karewa mace za ta auremu ko"
"Wayo Adda Fauziyya tayi min ba haka nake nufi ba. Maimakon tace pilot yadda zan fahimta"
"Sannu Queen Elizabeth wato sai anyi turanci zaki fahimta" Ibrahim yace.
"Ka kiyayeni Surbajo" A dolensa yayi shiru da yaji abin zai dawo kansa.
Tsokanarta suka cigaba da yi tana karewa kanta. Awwab yana kallon Ghazalatu yace da Radhiya "ki shirya zata kare miki kwanannan kuwa don sai kin auri pilot. Kafin nan kuma ki zamarwa matata 'yar aiki"
Mama da Zainab suka kalli juna suna gyada kai da murmushi. Bakin mota suka firfito Mami da Ummi zasu bi karamar motar sauran kowa yace bus din da Awwab zai tuka zasu shiga. Radhiya da jikinta yayi sanyi tana jin babu dadi akan maganar da tayi tace ita ma motarsu zata shiga sai ta zauna a gaba.
"Koma cikin 'yan uwanki Radhiya" Zainab tace tana turata bakin daya motar.
Awwab ta kalla ko zaiyi magana sai ta kula hirarsa kawai yake yi da Ghazalatu. Juyowa yayi ya kalli Radhiya duk ta zama wata salihar karfi da yaji "ina zuwa" ya cewa Ghazalatu ya taho inda take tsaye a jikin motar.
"Zo in nuna miki wani abu"
"Wai ba fushi kayi da abinda nace ba kake yi min magana"
Murmushi yayi "Silly girl, kawai sai nayi fushi bayan nasan ta kusa kare miki kwanannan...auren dreba ba fashi"
"Shine ka barni inata damuwa, kuma a gaba zan zauna inyi ta ganinka tunda yau zaku dawo"
Wurin wata katuwar fulawa inda Ghazalatu ke tsaye suka nufa. Suna jiran iyayensu su gama maganar da suke yi su dau hanya ne shiyasa basu tafi ba.
"Dama babu mai zama wurinki ne nima inyi ta kallonki"
Dariya tayi fuskar Ghazalatu ta hade tsaf da kishi. Awwab yasan me yake bata mata rai don yanzu ta gama fada masa ita bata son yadda yake yiwa Alheran dinnan bayan ba karamar yarinya bace. Domin ya kwantar mata da hankali yaje ya kira ta.
"My G, ga Alheran kanwata. Alheran ga Ghazalatu kanwata kuma matar da zan aura"
Sai yanzu hankalin Ghazalatu ya kwanta sosai. Ta kurawa Radhiya ido sai ta ga yarinyar ko a jikinta sai ma dariyar ta take yi fuskarta ta tana wani annuri.
Dage girrarta duka biyun ta rinka yi yadda ta saba idan zata yi tsokana
" Eyye eyye Hamma shine kace zanyi aiki a gidanka? Naji zan rinka tayata indai itace matar"
"Bana bukatar house girl so kiyi zamanki" Ghazalatu tace tana shan kamshi.
Fuskar Awwab kadai zaka kalla kasan kalaman basuyi masa ba.
"House girl?" Yace yana kankance idanu.
Ta fuskanci ransa ne ya baci sai ta wayance "naji kace za tayi min aiki ne dazu"
"Lallai wannan 'yar wulakanci ce" Radhiya tace a ranta. Ita bata san maganar wasa bane da zata yi tunanin da gaske aiki zata je yi mata. Hamma Awwab yafi karfin komai a wurinta tunda yake son Umminta da babanta da ita kanta. Kuma ba wani abu bane a wurinta ta taya matarsa aiki amma wallahi ba dai taje a house girl ba. Idan bata gwaba mata magana ko yaya bane tasan bazata ji dadi ba shiyasa ta ajiye katon murmushi a fuskarta tace "ko babu albashi zanyi miki aikin ma, kinsan mu 'yan kauye bamu san komai ba sai bautawa 'yan birni"
"No ki barshi fa bana bukata, idan ina so Yayana zai nemo min"
" Yes dai inzo inyi ko babu komai zan hutar da Hammana barnar kudi"
Hannuwansa ya zuba a aljihu yana kallon ikon Allah. Rigima ke neman tashi tsakaninsu daga su gaisa.
Daure fuska yayi yace "ku wuce ku shiga mu tafi"
Suna zuwa bakin motar Ibrahim zai bude gaba ya shiga saboda yana son Awwab ya koya masa tuki Ghazalatu ta riga shi budewa itama tana son zama kusa da masoyinta. Radhiya da ta fisu iyawa tayi sauri ta shige ta kofar bayan ta haura gaba. Awwab kansa sai ganinta yayi ta kusa fado masa garin sauri. Gyara zamanta tayi ta ballawa Ghazalatu da Ibrahim harara suna tsaye suna kallon abinda tayi.
"Ni dama ga wurina can kusa da Zeezee" Ibrahim yace yana shiga bayan inda Emzee ke yi masa dariya.
Ghazalatu ta kalli Awwab tana jira yayi magana "kace ta koma baya ina son muyi magana"
"Idan muna dawowa sai ki zauna a nan din kinji."
Tsabar bakinciki ji tayi kamar tasa ihu. Mami daga cikin tasu motar tace ta shiga su tafi rana tana kara yi. Hararar Radhiya tayi ita kuma tayi mata gwalo.
"Bansan mutum nayi ba sai naji a jikina"
"Alheran" taji yace muryarsa a dake sannan ya kalli Ghazalatu da take ta cika tana batsewa "ki shiga ki zauna mu tafi"
Daurewar da yayi yasa ta shige ba don ta hakura ba. Radhiya da take kusa dashi kuwa ji tayi kamar ta koma baya ita ma. Tukinsa kawai yake yi wanda baya masa dadi saboda bin bayan Abdallah da dole sai yayi tunda bai san hanya ba.
Motar duk sai tayi musu shiru mai bakin tsoro ya hanata magana Zayyana har ta soma gyangyadi a jikin Zahra. Su basu ma san me yake faruwa ba sai Ibrahim da yake tunanin saboda zaman gaba ne kawai.
Can dai taji shirun ya isheta ta dago a hankali ta saci kallonsa. Titi dai yake kallo har yanzu babu wannan sakin fuskar.
"Hamma" Radhiya ta kira sunansa a tausashe.
"Kar ki dameni please"
Shiru tayi ran sojoji ya baci. Ita kadai zaiyi fushi da ita bai ji masoyiyar tasa tana kiranta housegirl ba. Tura baki tayi ta juya duk jikinta tana kallon waje. Shima satar kallonta yayi yayi gajeren murmushi. Da gaske dai Alheran dinsa bata chanja ba sai ma abinda yayi gaba. Su mata abin rigima baya yi musu kadan ya kula. Su biyun kowa matsayinta daban to me ya kawo rigimar. Ko don Ghazalatu tace mata house girl? Shima kalmar bata yi masa dadi ba. Duka su biyun sai yayi aikin basu hakuri kenan. Haka kawai zasu tayar masa da hankali kamar wasu kishiyoyi. Ta mudubi ya hango Ghazalatu ita ma fuska babu wakwala kamar ma kuka take shirin yi. A take ya jinjinawa masu mata biyu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Sun isa Sumaila karfe biyu na rana a gajiye saboda tashin wuri da suka yi. Emzee ne ya koma jagora da suka shigo garin shiyasa tasu motar take gaba. Awwab ba tsayawa Emzee din ya fita da sauri saboda magana da yake son yi wa Ummin tasu. Gefe ya ja ta ana kokarin fitowa da kayan da ita kanta bata san da zamansu ba a boot.
"Ummi wai kuwa sun san zamu zo da baki?" Yace yana rage murya.
"Na fadawa Innawuro da ta kira nace ta sanar dasu tunda kaga ba waya gareni ba. Menene?"
Da damuwa a fuskarsa yace "kada muje a rasa abinda za'a basu nasan bazaki ji dadi ba"
Murmushi Mairama tayi. Zayyan dinta akwai hankali da nutsuwa ga zurfin tunani. Rashin abin tarbar baki tabbas zai iya faruwa don tasan halin gidan nasu "to yanzu me ya kamata ayi?"
"Idan kina da kudi kawo naje na siyo gurasa da tsire kawai"
Karamar jakarta ta mika masa. Dubu uku ya cire cikin kudin da Ardo ya bata ne da zasu taho. Ya tafi tana ta masa addu'a a zuciyarta.
Radhiya kuma ta kama kofa za ta bude Awwab ya danna central lock. A zuciye ta juyo "bude min"
"Ko nima balotellin zaki yi min ne? Zai fi miki sauki akan wannan juya idanun" bayansa ya juya "Ghazalatu zauna magana zamuyi"
Murtuke fuska tayi itama ya kallesu ya tabe baki. Mata, mata halinku sai ku.
Su Zayyana duk sun fita sun bi bayan iyayensu cikin gidan. Basu san me yasa ya tsayar da su Radhiya ba amma ko ma meye tabbas basu ga alamun wasa a tare da yayan nasu ba.
"Kun gama fushin ko har yanzu da saura?"
Ghazalatu dama jira take yi "don na biyoka shine zaka wulakantani akan wannan yarinyar kamar wata kishiyata? Tunda muka zo sai kayi mata magana sau uku baka yi min daya ba. Sannan nazo shiga gaba ta shige duka ka kyaleta. Idan wani abu ne tsakaninku gara ka fada min da wuri na san matsayina. Amma bazai yiwu ta rinka jin kanta kamar wata a wurinka ba tana neman shiga tsakaninmu"
"Kin gama? To bari kiji in fada miki. Alheran wata ce a wurina Ghazalatu kuma bazan yarda kici mata mutumci ba. She is my sister kamar yadda na dauki su Zahra haka ita ma na dauketa. Idan ma kishi zakiyi ba da ita zakiyi ba. Ki bari sai kin hadu da wadda take da matsayi irin naki a wurina"
Dazu gani take wannan Ghazalatun take ko wa tayi mata rashin mutumci amma maganar Awwab ta yanzu tafi kona mata rai akan komai duk da cewa gaskiya ce ya fada. Ita din kanwa take a wurinsa amma meyasa kalaman nasa suka yi mata zafi haka.