Sashe 143
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba tare da kuskuren taku ko tangarda ba domin sun sha wahalar rehearsal da mai koyar da rawar da suka dauko suke miming wakar suna rawar da ko wadanda suka hau ta a film din bazasu nuna musu komai ba. Mamaki tukuru.a fuskar Radhiya da Arifah yayin da jama'a suke kallon wannan abin burgewa ana ta murmushi da dariyar farinciki.
Can gefen slideshow ake yi na hotunam da suka dauka rannan kowa yana bin baiti ana nuna amaryarsa. Saboda basu taba zato da tsammani ba shiyasa mamakinsu da farinciki yayi musu yawa.
Radhiya sai da taji kamar a wurin ta rungume Awwab ta kwana tana fada masa cewa shi kadai ne farincikinta a rayuwa.
Sai da wakar ta kare a daidai imda suke rawa a tsugunne suna kada hannuwansu su ma su Awwab hakan suka yi wuri kuwa ya kaure da tafi kamar zasu tsaga hall din. Gashi duk yadda manyan nan suka so yin liki an saka wani abu kamar ribbon alamun babu wucewa. Suna gamawa fita suka yi haske ya mamaye wurin MC yace za'a fara cin abinci. Ana ta hayaniya da zancen yadda abu ya kayatar Fauziyya tazo ta ja amaren zuwa dakin da zasu canja kaya. Lace suka saka coffee color da gold head da sauran accessories aka gyara musu kwalliya. Ana tambayarsu yaya suka ji game da babban surprise din su Awwab sai murmushi an rasa me cewa wani abu. To su ce me bayan amgwayen sun gama musu komai.
A wurin shiga suka hadu dasu Awwab da Radhiya na gaba su Arifah na bayansu. Wannan karon shadda suka saka golden babbar riga da hula. Sun shiga kafin su zauna aka canja waka zuwa ta Nura M Inuwa wato 'Yar amanar da Radhiya ke matukar so. Wannan karon kam iyayensu mata sai da suka fito Awwab da Yousuf basu bar komai na irin takun Zango da ya hau wakar ba suna faman baza babbar riga. Liki akeyi kamar ba'asan ciwon kudi ba Awwab ya makale matarsa a gefe ganin wurin babu masaka tsinke.
Taron ya tashi sa misalin shadaya da rabi na dare anyi hotuna anci an sha rayuka sun faranta. Ghazalatu kamar ta hadiyi tabarya haka bakinciki ya tsaya ya tokare mata wuya. Tana ta bin Awwab da ido bata san ta ina ba sai jin Nura tayi a bayanta ya rungumota a waje da suka fito ana tafiya gida. A fusace ta juyo tace masa bata son wulakanci meye haka zai tabata.
"Dazun nan na mayar dake Ghazy" yace yana shafa keya.
Ashar ta dankaro masa saboda tsabar bacin rai. Tana hangen yadda zatayi ta sami Awwab shine don rashin mutumci ya mayar da ita. Ko sauraronta baiyi ba ya jefata a motar da yazo da ita yace mata yau zasu fara angwanci.
Wuri ya watse saura mutane kadan Awwab ya karbi mota a wurin drebansu wadda yada ya kawo masa ya budewa Radhiya. Yau duk ya kashe mata baki da abubuwan mamaki. Babbar rigar ya cire da hula ya dora mata akan cinya kamshin turarensa ya mamaye hancinta ya shiga mazaunin dreba ya tada mota.
Shiru ta kasa magana sai murmushi ya kalleta yace "tunanin me kike yi Schatzi?"
Kafin ta bada amsa ya zame mata gwaggwaronta da ya zauna das a kanta ta ja mayafin da ta ce a saka mata a jakar kayan ta rufe kanta.
"Ke nake sauraro?"
Ido ta runtse ta soma magana a hankali "Hammana bani da wani buri da ya wuce faranta maka. Abinda kayi min tun farkon haduwarmu har zuwa yau bazan taba mantawa ba. I love you with all i've got. Alheran is never complete without Awwab. Nagode, nagode, nagode" ta daga hannunta mai zoben da ya saka mata ta sumbata.
Hannunta kawai ya kamo ya rike a haka ya kaisu gida suna kallon juna suyi murmushi. Ita kuwa harda sunkuyar da kai.
Kusan kowa ya dawo ga motoci nan birjik a ciki ya samu wuri yayi parking.
Rigarsa da hular ya dauke daga cinyarta ya jefa baya inda ya cilla mata gwaggwaro sannan ya juyo da jikinsa yana fuskantarta ya jinginar da kansa gefe.
"Baby" taji yace a hankali sai da tsigar jikinta ta tashi.
"Uhmm"
"Na gaji sosai"
"Ai dole ka gasa jiki ko ka kasa tashi gobe" ta fada gabanta na faduwa.
Hannunsa ya mika mata duk lokacin yana kallonta tana jin idanuwansa a jikinta ta dukar da kai tana wasa da yatsunta da suka sha lalle. Sai da ta sake jin sabuwar faduwar gaba ta mika masa hannun damanta.
Tayi zaton rikewa kawai zaiyi ashe hanya ya nema ya janyota gabadaya jikinsa tana kan cinyarsa. Rungumeta yayi sosai yana sauke numfashi ta soma mutsu mutsun son tashi.
"Kinga" yace yana jan wani dan compartment a gaban motar tayi arba da mukullai "na gidanmu ne, ko dai ki nutsu ko na juya kan motar a biyoki da kayanki gobe"
Da sauri tace "Kai Hammana"
"I am serious baby na gaji sosai...mun kusa wata da aure da yanzu kin fara amai da tashin zuciya...."
Salati ta soma yi kunya kamar ta nutse a wurin "ni dai babu ruwana"
"Da nawa ni kam please ki bani janbakin nan na goge miki ko kuma mu tafi gidan"
A tsorace tace "idan wani ya ganmu fa?"
"Baki ji nace janbaki zan goge ba...haka zamu fada musu ai" ya sake yi mata wani irin riko.
"Wannan fa wayo ne"
"Ki bari nayi miki wayon mana" ya kyabe fuska shi a dole zaiyi mata shagwaba.
Dariyar da ta soma yi ya datse da bakinsa tun tana jin tsoro har ta biye masa suka manta a cikin gidan Daada suke.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Da kyar ta samu ya kyaleta ta fito daga motar ko ido ta kasa hadawa dashi. Shi kuwa ko a jikinsa sai ma murmushi da yake ta yi yana rike da hannunta.
Kashe mata ido yayi yace "yau ba zaki kara shafa wani ba don kada a gane?"
Motar ta nuna masa "shiga ka tafi ni dai"
Dariya yayi mata sannan ya dora hannunsa akan kirji ya ce "Kora ta kike yi? You are breaking my heart Schatzi, nayi zaton yau babu mai rabani dake"
"Ba korarka nake yi ba amma yanzu ina shiga ciki kunyar su Adda Zahra zanji. Sun san fa mun taho tun dazu amma kawai sai su ga na dade ban shigo ba?"
"Kin ma bani tausayi, idan kika tare Alheran na rinka baki kunyar nan kenan. Yadda nake so matata ta rinka kulawa dani haka nima zan rinka yi miki" ya janyota jikinsa ya zagaye kwankwasonta da hannuwansa.
Kunya sosai take ji gasu a waje kuma a gidan da yake da mutane tasan ko yaushe wani zai iya fitowa. Kukan shagwaba ta soma yi masa yace to ta shige ya rakata zuwa falo. Sun kusa shiga ta fara cewa ya juya ya tafi ita bata son su Fauziyya su ganshi.
Kai ya girgiza yana janyota ta hanyar dora hannunsa a kafadarta suna jerawa "indai Zahra da Fauziyya ne ina tabbatar miki kowacce tana wurin mijinta yau babu mai kwana a nan. Femi da Jawad suna wurin Zayyana da Rahima"
Baki Radhiya ta rike "a ina zasu kwana?"
Hancinta yaja a hankali ya juyo da ita gabansa ya rage tsayi tare da hada nasa hancin da nata yana magana a hankali "su na inda muka baro yayyen naki kowacce tasan abinda ya kamata. Wannan tsallen da muka sha sai da tausa..." kwantar da murya yayi mai kashe mata jiki "Allah Sarki Awwab tasa matar kunyar mutane tasa ko tunanin ciwon jikin da zai kwana yana y batayi ba. Dani da na biya sadaki da Ibrahim da Emzee babu maraba"
Hannuwanta ta ware kawai ta shige jikinsa ta kankame shi. Yau dinnan ya gama mata komai da performance dinsu. Hawaye take yi na tsabar son Awwab da kuma rashin son bata masa rai "Hammana kada kayi fushi dani"
"Kin wuce haka a wurina baby. Bazanyi fushi ba amma sai an rama min."
Kai ta gyada da murmushinta "na yarda"
"Ranar da aka kawoki fa..." yace yana shafa fuskarta.
"Na amince" ta bashi amsa a dake.
"Baby kada fa ki chanja shawara ba kyaleki zanyi ba" yace da warning voice yana dariya.
Juya masa idanu ta shiga yi tana jijjiga kai "meye a cikin tausa da ba zan iya ba Chèri? Allah Ya kaimu"
Karamin yatsansa ya dago ya hada da nata "pinky swear?" yace yadda yara suke yi.
"Sealed and stamped" ta kuma bashi amsa da kwarin gwiwa duk da har kasan zuciyarta tasan kawai fada take yi. Tun yanzu ma kunyarsa take ji ga faduwar gaba idan su na su kadai bare kuma ace daga ita sai shi a gida.
"Yanzu zan tafi da kwarina..." sake kissing dinta yayi ya rakata har cikin falon da babu kowa sannan ya juya ya tafi yana mitar wannan kwanaki da ake ta cinye masa na kasancewa da matarsa. Zancen zuci yake yi yana tuki "Allah Ya kaimu dai ki haifa min baby girl. Idan ta girma ana daura aure zan bawa mijinta su tafi don ni dai kam wannan tsarin bazan yarda a sake yiwa kowa ba".
**********
Yamutsa fuska Zayyan ya kula Mairama tana yi tun da suka dawo tayi wanka ta gama shirin bacci ta kasa kwanciya. Kwalbar turaren hannunsa ya ajiye ya dawo kusa da ita akan wata kujerar cushion mai laushi sosai guda daya da take dakin.
"Fillo yaya ne?"
"Warin panadol dakin nan yake yi kuma na duba ban ga inda magani ya zube ba"
"Panadol kuma? Bana jin komai sai kamshin turaren wutar da kika saka"
Hancinta ta matse ta hanyar sake yamutsa fuska "yanzu baka jin kamar panadol ya rube?"
Zayyan bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba harda buga kafa "rubabban panadol ne dai kin tabbata ba nine na tube din ba ko?"
"Eh tayani dubawa ba wasa nake ba" ta tashi tana kokarin dukawa ya dawo da ita kusa dashi.
"Nace miki na tureki kinki yarda. Tunda kika kin taba jin panadol ya rube?"
Kunya taji tana murmushi "wurin dinner dinma fa haka ya rinka yi"
"Fillo wata nawa ne ki dena ja min rai" yace yana kallon saitin cikinta.
Can gefen slideshow ake yi na hotunam da suka dauka rannan kowa yana bin baiti ana nuna amaryarsa. Saboda basu taba zato da tsammani ba shiyasa mamakinsu da farinciki yayi musu yawa.
Radhiya sai da taji kamar a wurin ta rungume Awwab ta kwana tana fada masa cewa shi kadai ne farincikinta a rayuwa.
Sai da wakar ta kare a daidai imda suke rawa a tsugunne suna kada hannuwansu su ma su Awwab hakan suka yi wuri kuwa ya kaure da tafi kamar zasu tsaga hall din. Gashi duk yadda manyan nan suka so yin liki an saka wani abu kamar ribbon alamun babu wucewa. Suna gamawa fita suka yi haske ya mamaye wurin MC yace za'a fara cin abinci. Ana ta hayaniya da zancen yadda abu ya kayatar Fauziyya tazo ta ja amaren zuwa dakin da zasu canja kaya. Lace suka saka coffee color da gold head da sauran accessories aka gyara musu kwalliya. Ana tambayarsu yaya suka ji game da babban surprise din su Awwab sai murmushi an rasa me cewa wani abu. To su ce me bayan amgwayen sun gama musu komai.
A wurin shiga suka hadu dasu Awwab da Radhiya na gaba su Arifah na bayansu. Wannan karon shadda suka saka golden babbar riga da hula. Sun shiga kafin su zauna aka canja waka zuwa ta Nura M Inuwa wato 'Yar amanar da Radhiya ke matukar so. Wannan karon kam iyayensu mata sai da suka fito Awwab da Yousuf basu bar komai na irin takun Zango da ya hau wakar ba suna faman baza babbar riga. Liki akeyi kamar ba'asan ciwon kudi ba Awwab ya makale matarsa a gefe ganin wurin babu masaka tsinke.
Taron ya tashi sa misalin shadaya da rabi na dare anyi hotuna anci an sha rayuka sun faranta. Ghazalatu kamar ta hadiyi tabarya haka bakinciki ya tsaya ya tokare mata wuya. Tana ta bin Awwab da ido bata san ta ina ba sai jin Nura tayi a bayanta ya rungumota a waje da suka fito ana tafiya gida. A fusace ta juyo tace masa bata son wulakanci meye haka zai tabata.
"Dazun nan na mayar dake Ghazy" yace yana shafa keya.
Ashar ta dankaro masa saboda tsabar bacin rai. Tana hangen yadda zatayi ta sami Awwab shine don rashin mutumci ya mayar da ita. Ko sauraronta baiyi ba ya jefata a motar da yazo da ita yace mata yau zasu fara angwanci.
Wuri ya watse saura mutane kadan Awwab ya karbi mota a wurin drebansu wadda yada ya kawo masa ya budewa Radhiya. Yau duk ya kashe mata baki da abubuwan mamaki. Babbar rigar ya cire da hula ya dora mata akan cinya kamshin turarensa ya mamaye hancinta ya shiga mazaunin dreba ya tada mota.
Shiru ta kasa magana sai murmushi ya kalleta yace "tunanin me kike yi Schatzi?"
Kafin ta bada amsa ya zame mata gwaggwaronta da ya zauna das a kanta ta ja mayafin da ta ce a saka mata a jakar kayan ta rufe kanta.
"Ke nake sauraro?"
Ido ta runtse ta soma magana a hankali "Hammana bani da wani buri da ya wuce faranta maka. Abinda kayi min tun farkon haduwarmu har zuwa yau bazan taba mantawa ba. I love you with all i've got. Alheran is never complete without Awwab. Nagode, nagode, nagode" ta daga hannunta mai zoben da ya saka mata ta sumbata.
Hannunta kawai ya kamo ya rike a haka ya kaisu gida suna kallon juna suyi murmushi. Ita kuwa harda sunkuyar da kai.
Kusan kowa ya dawo ga motoci nan birjik a ciki ya samu wuri yayi parking.
Rigarsa da hular ya dauke daga cinyarta ya jefa baya inda ya cilla mata gwaggwaro sannan ya juyo da jikinsa yana fuskantarta ya jinginar da kansa gefe.
"Baby" taji yace a hankali sai da tsigar jikinta ta tashi.
"Uhmm"
"Na gaji sosai"
"Ai dole ka gasa jiki ko ka kasa tashi gobe" ta fada gabanta na faduwa.
Hannunsa ya mika mata duk lokacin yana kallonta tana jin idanuwansa a jikinta ta dukar da kai tana wasa da yatsunta da suka sha lalle. Sai da ta sake jin sabuwar faduwar gaba ta mika masa hannun damanta.
Tayi zaton rikewa kawai zaiyi ashe hanya ya nema ya janyota gabadaya jikinsa tana kan cinyarsa. Rungumeta yayi sosai yana sauke numfashi ta soma mutsu mutsun son tashi.
"Kinga" yace yana jan wani dan compartment a gaban motar tayi arba da mukullai "na gidanmu ne, ko dai ki nutsu ko na juya kan motar a biyoki da kayanki gobe"
Da sauri tace "Kai Hammana"
"I am serious baby na gaji sosai...mun kusa wata da aure da yanzu kin fara amai da tashin zuciya...."
Salati ta soma yi kunya kamar ta nutse a wurin "ni dai babu ruwana"
"Da nawa ni kam please ki bani janbakin nan na goge miki ko kuma mu tafi gidan"
A tsorace tace "idan wani ya ganmu fa?"
"Baki ji nace janbaki zan goge ba...haka zamu fada musu ai" ya sake yi mata wani irin riko.
"Wannan fa wayo ne"
"Ki bari nayi miki wayon mana" ya kyabe fuska shi a dole zaiyi mata shagwaba.
Dariyar da ta soma yi ya datse da bakinsa tun tana jin tsoro har ta biye masa suka manta a cikin gidan Daada suke.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Da kyar ta samu ya kyaleta ta fito daga motar ko ido ta kasa hadawa dashi. Shi kuwa ko a jikinsa sai ma murmushi da yake ta yi yana rike da hannunta.
Kashe mata ido yayi yace "yau ba zaki kara shafa wani ba don kada a gane?"
Motar ta nuna masa "shiga ka tafi ni dai"
Dariya yayi mata sannan ya dora hannunsa akan kirji ya ce "Kora ta kike yi? You are breaking my heart Schatzi, nayi zaton yau babu mai rabani dake"
"Ba korarka nake yi ba amma yanzu ina shiga ciki kunyar su Adda Zahra zanji. Sun san fa mun taho tun dazu amma kawai sai su ga na dade ban shigo ba?"
"Kin ma bani tausayi, idan kika tare Alheran na rinka baki kunyar nan kenan. Yadda nake so matata ta rinka kulawa dani haka nima zan rinka yi miki" ya janyota jikinsa ya zagaye kwankwasonta da hannuwansa.
Kunya sosai take ji gasu a waje kuma a gidan da yake da mutane tasan ko yaushe wani zai iya fitowa. Kukan shagwaba ta soma yi masa yace to ta shige ya rakata zuwa falo. Sun kusa shiga ta fara cewa ya juya ya tafi ita bata son su Fauziyya su ganshi.
Kai ya girgiza yana janyota ta hanyar dora hannunsa a kafadarta suna jerawa "indai Zahra da Fauziyya ne ina tabbatar miki kowacce tana wurin mijinta yau babu mai kwana a nan. Femi da Jawad suna wurin Zayyana da Rahima"
Baki Radhiya ta rike "a ina zasu kwana?"
Hancinta yaja a hankali ya juyo da ita gabansa ya rage tsayi tare da hada nasa hancin da nata yana magana a hankali "su na inda muka baro yayyen naki kowacce tasan abinda ya kamata. Wannan tsallen da muka sha sai da tausa..." kwantar da murya yayi mai kashe mata jiki "Allah Sarki Awwab tasa matar kunyar mutane tasa ko tunanin ciwon jikin da zai kwana yana y batayi ba. Dani da na biya sadaki da Ibrahim da Emzee babu maraba"
Hannuwanta ta ware kawai ta shige jikinsa ta kankame shi. Yau dinnan ya gama mata komai da performance dinsu. Hawaye take yi na tsabar son Awwab da kuma rashin son bata masa rai "Hammana kada kayi fushi dani"
"Kin wuce haka a wurina baby. Bazanyi fushi ba amma sai an rama min."
Kai ta gyada da murmushinta "na yarda"
"Ranar da aka kawoki fa..." yace yana shafa fuskarta.
"Na amince" ta bashi amsa a dake.
"Baby kada fa ki chanja shawara ba kyaleki zanyi ba" yace da warning voice yana dariya.
Juya masa idanu ta shiga yi tana jijjiga kai "meye a cikin tausa da ba zan iya ba Chèri? Allah Ya kaimu"
Karamin yatsansa ya dago ya hada da nata "pinky swear?" yace yadda yara suke yi.
"Sealed and stamped" ta kuma bashi amsa da kwarin gwiwa duk da har kasan zuciyarta tasan kawai fada take yi. Tun yanzu ma kunyarsa take ji ga faduwar gaba idan su na su kadai bare kuma ace daga ita sai shi a gida.
"Yanzu zan tafi da kwarina..." sake kissing dinta yayi ya rakata har cikin falon da babu kowa sannan ya juya ya tafi yana mitar wannan kwanaki da ake ta cinye masa na kasancewa da matarsa. Zancen zuci yake yi yana tuki "Allah Ya kaimu dai ki haifa min baby girl. Idan ta girma ana daura aure zan bawa mijinta su tafi don ni dai kam wannan tsarin bazan yarda a sake yiwa kowa ba".
**********
Yamutsa fuska Zayyan ya kula Mairama tana yi tun da suka dawo tayi wanka ta gama shirin bacci ta kasa kwanciya. Kwalbar turaren hannunsa ya ajiye ya dawo kusa da ita akan wata kujerar cushion mai laushi sosai guda daya da take dakin.
"Fillo yaya ne?"
"Warin panadol dakin nan yake yi kuma na duba ban ga inda magani ya zube ba"
"Panadol kuma? Bana jin komai sai kamshin turaren wutar da kika saka"
Hancinta ta matse ta hanyar sake yamutsa fuska "yanzu baka jin kamar panadol ya rube?"
Zayyan bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba harda buga kafa "rubabban panadol ne dai kin tabbata ba nine na tube din ba ko?"
"Eh tayani dubawa ba wasa nake ba" ta tashi tana kokarin dukawa ya dawo da ita kusa dashi.
"Nace miki na tureki kinki yarda. Tunda kika kin taba jin panadol ya rube?"
Kunya taji tana murmushi "wurin dinner dinma fa haka ya rinka yi"
"Fillo wata nawa ne ki dena ja min rai" yace yana kallon saitin cikinta.