Sashe 42
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zamowa yayi daga kan kujerar yana janyo plate din gabansa bayan ya tankwashe kafafunsa.
"Babu ruwana da wasanninku, Alheran matso mu ci yunwa nake ji"
Bude baki su kayi cike da mamaki harda ita Radhiyan.
Kifta mata ido Awwab yayi a kunyace ta matso ya dauki fork a kan tray din da aka kawo kwanukan abincin.
"Muyi kama-kama irin na yara?" Yayi magana yana kallon idanunta. Tsabar kunya tashi tayi zata gudu.
"Ba fa ki isa ba, wannan abincin na mutum biyu ne so just sit mu cinye"
"Kaci ka rage min Hamma Awwab" tace tana kallon su Zahra tana neman taimako.
"Tare zamu ci kada a barki da gyaran akwati"
"Babu komai zan iya"
Hade rai yayi "ina wasa dake ne?"
Ba shiri ta zauna tana bashi hakuri sai kuma ta waiga tana kallon kowa an zuba musu ido "don Allah ka bari su gama duka su tafi kunyarsu nake ji"
"Kin tabbata zaki zauna muci idan sun tafi?"
"Eh mana"
"Kamar gaske"
Bude baki tayi za ta sake magana kawai ya tura mata fork din da ya ciko da abinci tun dazu. Ibrahim ya dora hannu ya rufewa Emzee idanun da ya zaro sun ga abinda basu saba ba. Zahra ma sai ta rufe nata ta sakalo hannuwanta akan idanun Fauziyya da Zayyana suna faman dariya.
Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab yayi murmushi duk da yayi ne kawai saboda kannensa amma abin ya tsaya masa a rai dakewa kawai yayi ya dauko kofin da aka cika da juice ya miko saitin bakinta.
"Sorry na cika miki baki, hadiye ki sha wannan"
A guje Radhiya ta bar falon kafin ta kasa numfashi. Yau ta gamu da gamonta. Ita bata taba kunyar wani mahaluki ba kamar yadda taji Awwab ya gama da ita ba yau.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Bata tsaya ko ina ba sai daki ta cire hijabin da dankwali ta fada kan gado. Wani tunani ne ya shigeta haka kawai kada a sake tsautsayi ta dauki dankwalinta ta daura.
Awwab kamar bai san me yayi ba ya shiga cin abinci hankali kwance yana jin matan suna kuskus a junansu. To meye ma a ciki daga bata abinci. Da ace sun tashi tare baya jin akwai abinda zai kasa yi mata sai dai a taka masa birki tunda mace ce. Allah ne Ya hada jininsa da na iyayenta sai Ya sanya masa matukar kaunarta tun tana tsumman goyo.
Emzee yaso dauke kai amma ya kasa. Karshe ya dauko wani littafi a kusa dashi ya bude shi ya kifa akan fuskarsa yana dariyar da ba sauti. Gaskiya yaji kunya kamar shi aka bawa abincin. Ibrahim ne ya fara tsokanarsa sai kawai ya tashi da plate dinsa a hannu zai koma daki.
"Dawo ka zauna ka gama cin abincin nan" Awwab yace ko kallonsa baiyi ba.
"Na koshi"
"Kira min Alheran"
Ba musu yaje ya fadi sakon, maimakon amsa sai ta kara dukunkune kanta ta tura a karkashin filo. Murmushi yayi kawai ya fita ya dawo ya fadawa Awwab taki tashi.
Sai da yaci rabin abincin ya mika masa plate din "ka kai mata nata, sai da safen ku"
Tashi yayi zai tafi dakin Ibrahim inda aka yi masa masauki Zayyana da ta kasa hakuri ta fara shagwabe fuska "Hamma ni baka taba yi min irin haka ba, harda bata a baki"
"Ba kiji ta fada muku cewa a rashinta nake kulaki ba" ya fada da wasa.
Kukan shagwabar da ta saba ta fara "kuma sai na...."
"....fadawa Daddy" Ibrahim ya karashe mata yana kyabe fuska yadda take yi.
Awwab ya kusa kofa don idan ya biye mata karshenta a daren sai ya ga wayar Daddy. Juye juye ta soma yi Emzee ya dawo daga ajiyewa Radhiya abinci ya ganta.
"Wa kike nema?"
"Kai mana"
"Inyi miki me?"
"Ba Hamma Ibrahim bane yake tsokanata"
"In fada miki sunan Fulatancinsa ki rama?"
Cikin sauri Ibrahim yazo ya tura shi daki yana magiya da yayi shiru. Tun da Radhiya ta fassara masa ma'anar Surbajo yake gudun sunan kuma dashi Emzee yake samu ya dan kashe bakin idan ya dame su.
Da yake Mami ta fada musu cewa sammako zasuyi su baro Katsina su ma basu yi sanya ba wurin tashi da wuri. Zuwan 'yan matan ba karamin dadi ya yiwa Zainab ba. Su tayata hira ayi ta barkwanci sannan basa bari tayi komai. Zahra da Fauziyya sun jima da gogewa wurin aikin gida da girki. Saboda Mami taran safe zuwa taran dare tana gidan aikinta. Su ne suke komai. Shiyasa Zayyana ta shaku dasu sosai wani zubin bazaka ce yayyenta bane da suka girme mata da yawa.
Kowa ya shirya cikin kayan kirki Radhiya ta bude jakarta kenan bayan ta gama shafa mai Zainab ta leko tayi kiranta. Dakinta ta bar musu dama. Yanzu kuwa da ta kai Hadir falo bayan ya gama breakfast sai ta kirata dakinsa. Ledoji uku ne a gabanta manya ta tura mata daya.
"Ga naki kafin ku tashi daga bacci telan ya kawo"
Radhiya ta bude baki tana kallon kayan da Zainab din take zarowa. Atampa guda uku, material daya, shadda daya da wasu yadika combination biyu. Kwalkwal tayi ta idanu zata yi kuka. Duk wannan ita kadai.
"Bana son kuka fa kin sani ko yanzu naje na fada a hanaki yin sojan."
"Mama nagode" tace hawayen yana fitowa. Yarinya ce mai rike abu a rai shiyasa bata manta alkhairi ko sharri. Da yake dai wasa da shirme sunyi mata yawa a ka shiyasa sai ka ga kamar bata da damuwar komai.
Banda kaddara da Zayyan yana raye Zainab ta sani da yanzu sun kai wani mataki a aikinsu. Yadda yake da kwazo da himma tasan 'ya'yansa sai dai wani yaci arzikinsu. Babban dalilin kiran dama so take ta shirya Radhiya da kanta. Mama Zainab 'yar kwalliya ce ajin karshe. Idan ka ganta a yanzu da take cikin farincikin kasancewa da Hadir duk da a zahiri za'a iya cewa nauyi ne shi a gareta amma fes take kullum. Gogewarta a soyayya duba da tarihin rayuwarta yasa tun jiya ta daukarwa kanta nauyin sake hada Awwab da Alheran domin su cimma burinsu cikin sauki akan yaran.
Kallo daya zaka yi musu kasan sun dace da juna amma idan ka san kowannensu ta fannin zamantakewar rayuwa dole ka chanja shawara. Awwab dan boko ne tashin turai. Yana da ilimi, wayewa da kudi domin kuwa pilots masu aiki da kamfanin KLM suna cikin mafiya samun kudi cikin tsararrakinsu. Alheran Radhiya kuwa yarinya ce da ta tashi a rugar fulani a cikin wata karamar hukuma. Wannan kadai ya isa zama wawakeken bambamci tsakaninsu indai zaman aure zasuyi wanda babu soyayya. Abubuwan da ya sani ko yake so bata sansu ba bare ta so su. Wayewarsu ba iri daya bace. Tayi nata karatun daidai gwargwado amma baza'a taba hada shi da nasa ba tunda iyakarta secondary. Shiyasa indai ana so zaman aurensu yayi karko to a samu soyayya mai karfi da za ta zama igiyar dauresu.
Wani kaya Zainab ta ciro daga ledar ta mika mata "jeki ki saka wadannan gani nan zuwa. Ko hoda kada ki shafa sai nazo"
"To Mama" tace ta fita da murnarta taje ta nunawa su Zahra su ka tayata murna.
Yadi ne mai kala biyu. Mara adon light purple ne anyi mata skirt dogo da dankwali. Rigar kuwa yadinta duka zanen filawoyi ne manya pink da light light purple kamar skirt din. Tsayinta ya wuce gwiwa da kadan anyi mata dogon hannu mai dan fadi daga kasansa. Kadan akayi mata shape don kada ta kama jiki ba wani ado a jikinta sai maballai guda hudu na wuya amma tayi kyau musamman a jikin Radhiya. Wani juyi ta rinka yi tana jindadi su Zahra na zuga ta har Zainab ta shigo tace suyi sauri wanda basu ci abinci ba su je su ci nan da awa daya ko kasa da haka su Mami zasu iso. Duka su ukun su ka fita aka barsu su kadai.
Hoda, kwalli da janbaki pink mara duhu ta shafawa Radhiya a fuska bayan tayi mata lining da jagira pink mai duhu a leben. Simple make up ne amma fuskarta tayi kyau. Cikas din kawai kanta ne. Zainab ta daura mata dankwalin da kanta ya danyi tudu daga keya sannan ta mika mata hijab mai kyau da kananun duwatsu a kasansa pink irin kayan. Iyakarsa ya sauko kirjinta da kadan. Radhiya harda hajijiya a gaban mudubi.
"Mama nayi kyau ko?"
Murmushi tayi ta yaba sosai da 'yar tasu "kinyi kyau amma don Allah bana son baragada kinji ko. Wannan hayaniyar da saurin fushi ko fada ki ajiyesu. So nake naga kina taku daidai yadda babu wanda zai raina min ke"
"Idan nayi sanyi da yawa bazan kai labari ba a makarantar sojoji Mama. Anfi son mu da dakiya da fada saboda gudun raini"
"Allah nagode Maka. Har yanzu kina jiran zuwa sojan ne bayan miji zan samo miki"
Da murnarta tace "Likita?"
"Idan ba likita bane ba fa?"
"Gaskiya Mama ki barshi kawai. Idan ba likita ba sai dai ko soja irina. Sauran duk na rainasu, kada ayi auren su rinka kawo karata kullum"
Hannuwa Zainab ta tafa tana dariya, yanzu ta gama cewa ta dena shirme gashi ta hade fuska tana buga kayanta a ganinta kuma ba laifi bane.
"Jeki kici abinci kada azo ana jiranki"
Kallon kanta ta sake yi yadda tayi kyau abinci zai iya goge mats jambakin ta dawo tayi zamanta akan gado "bana jin yunwa"
"Ashe kuwa za'a tafi a barki" Zainab tace tana yin gaba.
Ba don taso ba ta tashi itama. Tana saka kafa a falon ta tuna abinda Awwab yayi mata sai ta juya suka kusa karo da Zainab.
"Wuce muje kici abinci" ta umarceta.
Gani tayi babu alamun Awwab din sai ta saki ranta ta fara gaishe da Hadir da yake kallon labarai sannan ta tafi gaban dinning table inda kayan tea suke za ta hada taji Zainab tana tambayar ko Awwab ya shirya.
"Da kyar idan ma ya tashi Mama, shi fa idan yana gida yafi zaman daki yayi bacci saboda yanayin aikinsa" Zahra ta bata amsa.
"Babu ruwana da wasanninku, Alheran matso mu ci yunwa nake ji"
Bude baki su kayi cike da mamaki harda ita Radhiyan.
Kifta mata ido Awwab yayi a kunyace ta matso ya dauki fork a kan tray din da aka kawo kwanukan abincin.
"Muyi kama-kama irin na yara?" Yayi magana yana kallon idanunta. Tsabar kunya tashi tayi zata gudu.
"Ba fa ki isa ba, wannan abincin na mutum biyu ne so just sit mu cinye"
"Kaci ka rage min Hamma Awwab" tace tana kallon su Zahra tana neman taimako.
"Tare zamu ci kada a barki da gyaran akwati"
"Babu komai zan iya"
Hade rai yayi "ina wasa dake ne?"
Ba shiri ta zauna tana bashi hakuri sai kuma ta waiga tana kallon kowa an zuba musu ido "don Allah ka bari su gama duka su tafi kunyarsu nake ji"
"Kin tabbata zaki zauna muci idan sun tafi?"
"Eh mana"
"Kamar gaske"
Bude baki tayi za ta sake magana kawai ya tura mata fork din da ya ciko da abinci tun dazu. Ibrahim ya dora hannu ya rufewa Emzee idanun da ya zaro sun ga abinda basu saba ba. Zahra ma sai ta rufe nata ta sakalo hannuwanta akan idanun Fauziyya da Zayyana suna faman dariya.
Radhiya kasa motsi tayi sai idanu da take ta kiftawa ba kakkautawa. Awwab yayi murmushi duk da yayi ne kawai saboda kannensa amma abin ya tsaya masa a rai dakewa kawai yayi ya dauko kofin da aka cika da juice ya miko saitin bakinta.
"Sorry na cika miki baki, hadiye ki sha wannan"
A guje Radhiya ta bar falon kafin ta kasa numfashi. Yau ta gamu da gamonta. Ita bata taba kunyar wani mahaluki ba kamar yadda taji Awwab ya gama da ita ba yau.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Bata tsaya ko ina ba sai daki ta cire hijabin da dankwali ta fada kan gado. Wani tunani ne ya shigeta haka kawai kada a sake tsautsayi ta dauki dankwalinta ta daura.
Awwab kamar bai san me yayi ba ya shiga cin abinci hankali kwance yana jin matan suna kuskus a junansu. To meye ma a ciki daga bata abinci. Da ace sun tashi tare baya jin akwai abinda zai kasa yi mata sai dai a taka masa birki tunda mace ce. Allah ne Ya hada jininsa da na iyayenta sai Ya sanya masa matukar kaunarta tun tana tsumman goyo.
Emzee yaso dauke kai amma ya kasa. Karshe ya dauko wani littafi a kusa dashi ya bude shi ya kifa akan fuskarsa yana dariyar da ba sauti. Gaskiya yaji kunya kamar shi aka bawa abincin. Ibrahim ne ya fara tsokanarsa sai kawai ya tashi da plate dinsa a hannu zai koma daki.
"Dawo ka zauna ka gama cin abincin nan" Awwab yace ko kallonsa baiyi ba.
"Na koshi"
"Kira min Alheran"
Ba musu yaje ya fadi sakon, maimakon amsa sai ta kara dukunkune kanta ta tura a karkashin filo. Murmushi yayi kawai ya fita ya dawo ya fadawa Awwab taki tashi.
Sai da yaci rabin abincin ya mika masa plate din "ka kai mata nata, sai da safen ku"
Tashi yayi zai tafi dakin Ibrahim inda aka yi masa masauki Zayyana da ta kasa hakuri ta fara shagwabe fuska "Hamma ni baka taba yi min irin haka ba, harda bata a baki"
"Ba kiji ta fada muku cewa a rashinta nake kulaki ba" ya fada da wasa.
Kukan shagwabar da ta saba ta fara "kuma sai na...."
"....fadawa Daddy" Ibrahim ya karashe mata yana kyabe fuska yadda take yi.
Awwab ya kusa kofa don idan ya biye mata karshenta a daren sai ya ga wayar Daddy. Juye juye ta soma yi Emzee ya dawo daga ajiyewa Radhiya abinci ya ganta.
"Wa kike nema?"
"Kai mana"
"Inyi miki me?"
"Ba Hamma Ibrahim bane yake tsokanata"
"In fada miki sunan Fulatancinsa ki rama?"
Cikin sauri Ibrahim yazo ya tura shi daki yana magiya da yayi shiru. Tun da Radhiya ta fassara masa ma'anar Surbajo yake gudun sunan kuma dashi Emzee yake samu ya dan kashe bakin idan ya dame su.
Da yake Mami ta fada musu cewa sammako zasuyi su baro Katsina su ma basu yi sanya ba wurin tashi da wuri. Zuwan 'yan matan ba karamin dadi ya yiwa Zainab ba. Su tayata hira ayi ta barkwanci sannan basa bari tayi komai. Zahra da Fauziyya sun jima da gogewa wurin aikin gida da girki. Saboda Mami taran safe zuwa taran dare tana gidan aikinta. Su ne suke komai. Shiyasa Zayyana ta shaku dasu sosai wani zubin bazaka ce yayyenta bane da suka girme mata da yawa.
Kowa ya shirya cikin kayan kirki Radhiya ta bude jakarta kenan bayan ta gama shafa mai Zainab ta leko tayi kiranta. Dakinta ta bar musu dama. Yanzu kuwa da ta kai Hadir falo bayan ya gama breakfast sai ta kirata dakinsa. Ledoji uku ne a gabanta manya ta tura mata daya.
"Ga naki kafin ku tashi daga bacci telan ya kawo"
Radhiya ta bude baki tana kallon kayan da Zainab din take zarowa. Atampa guda uku, material daya, shadda daya da wasu yadika combination biyu. Kwalkwal tayi ta idanu zata yi kuka. Duk wannan ita kadai.
"Bana son kuka fa kin sani ko yanzu naje na fada a hanaki yin sojan."
"Mama nagode" tace hawayen yana fitowa. Yarinya ce mai rike abu a rai shiyasa bata manta alkhairi ko sharri. Da yake dai wasa da shirme sunyi mata yawa a ka shiyasa sai ka ga kamar bata da damuwar komai.
Banda kaddara da Zayyan yana raye Zainab ta sani da yanzu sun kai wani mataki a aikinsu. Yadda yake da kwazo da himma tasan 'ya'yansa sai dai wani yaci arzikinsu. Babban dalilin kiran dama so take ta shirya Radhiya da kanta. Mama Zainab 'yar kwalliya ce ajin karshe. Idan ka ganta a yanzu da take cikin farincikin kasancewa da Hadir duk da a zahiri za'a iya cewa nauyi ne shi a gareta amma fes take kullum. Gogewarta a soyayya duba da tarihin rayuwarta yasa tun jiya ta daukarwa kanta nauyin sake hada Awwab da Alheran domin su cimma burinsu cikin sauki akan yaran.
Kallo daya zaka yi musu kasan sun dace da juna amma idan ka san kowannensu ta fannin zamantakewar rayuwa dole ka chanja shawara. Awwab dan boko ne tashin turai. Yana da ilimi, wayewa da kudi domin kuwa pilots masu aiki da kamfanin KLM suna cikin mafiya samun kudi cikin tsararrakinsu. Alheran Radhiya kuwa yarinya ce da ta tashi a rugar fulani a cikin wata karamar hukuma. Wannan kadai ya isa zama wawakeken bambamci tsakaninsu indai zaman aure zasuyi wanda babu soyayya. Abubuwan da ya sani ko yake so bata sansu ba bare ta so su. Wayewarsu ba iri daya bace. Tayi nata karatun daidai gwargwado amma baza'a taba hada shi da nasa ba tunda iyakarta secondary. Shiyasa indai ana so zaman aurensu yayi karko to a samu soyayya mai karfi da za ta zama igiyar dauresu.
Wani kaya Zainab ta ciro daga ledar ta mika mata "jeki ki saka wadannan gani nan zuwa. Ko hoda kada ki shafa sai nazo"
"To Mama" tace ta fita da murnarta taje ta nunawa su Zahra su ka tayata murna.
Yadi ne mai kala biyu. Mara adon light purple ne anyi mata skirt dogo da dankwali. Rigar kuwa yadinta duka zanen filawoyi ne manya pink da light light purple kamar skirt din. Tsayinta ya wuce gwiwa da kadan anyi mata dogon hannu mai dan fadi daga kasansa. Kadan akayi mata shape don kada ta kama jiki ba wani ado a jikinta sai maballai guda hudu na wuya amma tayi kyau musamman a jikin Radhiya. Wani juyi ta rinka yi tana jindadi su Zahra na zuga ta har Zainab ta shigo tace suyi sauri wanda basu ci abinci ba su je su ci nan da awa daya ko kasa da haka su Mami zasu iso. Duka su ukun su ka fita aka barsu su kadai.
Hoda, kwalli da janbaki pink mara duhu ta shafawa Radhiya a fuska bayan tayi mata lining da jagira pink mai duhu a leben. Simple make up ne amma fuskarta tayi kyau. Cikas din kawai kanta ne. Zainab ta daura mata dankwalin da kanta ya danyi tudu daga keya sannan ta mika mata hijab mai kyau da kananun duwatsu a kasansa pink irin kayan. Iyakarsa ya sauko kirjinta da kadan. Radhiya harda hajijiya a gaban mudubi.
"Mama nayi kyau ko?"
Murmushi tayi ta yaba sosai da 'yar tasu "kinyi kyau amma don Allah bana son baragada kinji ko. Wannan hayaniyar da saurin fushi ko fada ki ajiyesu. So nake naga kina taku daidai yadda babu wanda zai raina min ke"
"Idan nayi sanyi da yawa bazan kai labari ba a makarantar sojoji Mama. Anfi son mu da dakiya da fada saboda gudun raini"
"Allah nagode Maka. Har yanzu kina jiran zuwa sojan ne bayan miji zan samo miki"
Da murnarta tace "Likita?"
"Idan ba likita bane ba fa?"
"Gaskiya Mama ki barshi kawai. Idan ba likita ba sai dai ko soja irina. Sauran duk na rainasu, kada ayi auren su rinka kawo karata kullum"
Hannuwa Zainab ta tafa tana dariya, yanzu ta gama cewa ta dena shirme gashi ta hade fuska tana buga kayanta a ganinta kuma ba laifi bane.
"Jeki kici abinci kada azo ana jiranki"
Kallon kanta ta sake yi yadda tayi kyau abinci zai iya goge mats jambakin ta dawo tayi zamanta akan gado "bana jin yunwa"
"Ashe kuwa za'a tafi a barki" Zainab tace tana yin gaba.
Ba don taso ba ta tashi itama. Tana saka kafa a falon ta tuna abinda Awwab yayi mata sai ta juya suka kusa karo da Zainab.
"Wuce muje kici abinci" ta umarceta.
Gani tayi babu alamun Awwab din sai ta saki ranta ta fara gaishe da Hadir da yake kallon labarai sannan ta tafi gaban dinning table inda kayan tea suke za ta hada taji Zainab tana tambayar ko Awwab ya shirya.
"Da kyar idan ma ya tashi Mama, shi fa idan yana gida yafi zaman daki yayi bacci saboda yanayin aikinsa" Zahra ta bata amsa.