Sashe 8
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ana tsaka da kiran magariba Salame ta shigo gidan. Can wurin Ta Madina da taje bacin rai kawai ta karo don sosai take fushi da ita har yanzu saboda abinda tayi mata a Kano. Sallama tayi a dakin Mairama ta amsata ciki-ciki. Tsaki ta doka ta ajiye gyalenta ta fita yin alwala. Bayan tayi sallah ne Mairama ta tambayeta ko ta ga mukullin sif din.
“Ajiya kika ban ko me?”
Zuciya ta soma cin Mairama saboda ta tabbatar dazu da gangan Salame ta fita duk da tasan kiranta take yi. Wai ma me ya kaita wurin Zayyan din.
“Shikenan”
“Shikenan me?”
Maimakon amsar fatar baki sai gani tayi Mairama tasa iyakar karfinta tana jijjiga kofofin sif din tana neman ballesu. Da saurinta ta mike don ta dakatar da ita.
“Meye hakan?”
“Dame yayi miki kama? Balleta zanyi tunda mukullin ya bata in nemi kayan sawa”
“Saboda saurayinki zai zo?”
Salame tace da kaushin murya.
“Adda Salame idan wani abu nayi miki ki fito fili ki fada min amma ba ki zauna kullum kina jin haushina kina min tsaki ba. Kin sani wallahi ba don ke Addata bace ….”
“Sai ki dakeni ko ba haka ba”
Wata fuzga ta kaiwa kofar sai gata ta bude ta dauko kayan da zata saka bata sake kula Salame ba. Gefe ita ma ta koma tana ta hucin kishi ganin yadda Mairama ta zage tana kwalliya saboda Zayyan.
“Aikin banza ki gama adon yace ya fasa tunda yanzu yasan daga wane irin gida ki ka fito.”
A tsorace ta waiwayo “fada masa kika yi?”
Salame sai ta tsame kafarta tayi waje. Tana zaune tana jira a raba tuwon gidan na al’ada a bata nata Mairama ta fito bayan an fada mata dawowar Zayyan. Da tazo wucewa tana jin uban tsakin da Salame taja har sai da Dije ta soma sababi ko da ita take.
Hira suka yi cikin nutsuwa rabi duk shi yake maganar saboda kunya irin ta Fulani. Tana son tambayarsa game da abubuwan da take zargin Salame ta fada masa amma ta gaza. Kamar ya sani kuwa da kansa ya shiga bata labarin asalinsa da rayuwarsa ta baya zuwa yanzu. Tausayinsa taji har idanunta su ka ciko da kwalla.
“Bana so yanayin rayuwar gidanku ya sanya ki fara tunanin zan gujeki ko hakan zai shafi zamantakewarmu. Gidajen da muka fito daban, sannan gidan da zamu samarwa kanmu da ‘ya’yan da nake burin ki haifa min shima daban.”
Tamkar kasa ta zage ta hadiyeta taji saboda kunyar kalaminsa na karshe. Da dabara ya samu ya rinka kwantar mata da hankali da kwadaita mata irin tanadin da yake mata idan ta zama mallakinsa. Ba shi ya bar gidan ba sai tara da rabi na dare. Washegari ya sake zuwa kuma a ranar ne ya sanar da Malamijo zuwan kawunnansa idan ya koma.
“Abin da nake so da kai shine ka fada musu su taho da sadakinsu ayi komai a kare. Yaran nan sun zaunu babu dalilin ayi ta jan lokaci. Budurwa kamar Mairama ta bawa shekaru shatakwas baya harda watanni ina kallonta tana kallona. Ga yayarta ita ma zan fadawa yaron nan Salisu sai ayi a lokaci guda”
Dadi maganar ta Malamijo tayi masa yayi na’am da ita. Ana gobe zai koma yana jiran fitowar Mairama sai ga Salame da ta shiga tashin hankali sakamakon gabatowar aurenta da Salisun da bata so. Hanyar waje tayi a daidai inda yake zaune ta jefa masa takarda ta fita. Ba nisa tayi ba tana layin bayan gidansu tana jiran ya karanta wasikar yazo ya sameta.
Layuka kadan ya karanta inda take sanar dashi son da take masa da kuma jiransa da take a bayan layi idan ya amince yazo ya sameta. Mairama ce tayi sallama sai kawai ya yayyaga takardar ya dunkuleta a hannunsa.
Sun jima suna hira yana fada mata haduwarsu ta gaba ta zama tasa tana dariya a hankali Salame ta dawo kamar kububuwa. Ta kwashi awa guda da doriya tana jiransa bai zo ba. Yanzu da ta shigo takardar hannunsa ya watsa a iska ko kallonta baiyi ba. Zuciyarta kamar za ta fashe saboda bakinciki ta wuce ciki.
Bahaushe ma yasan babu wanda ya isa ya sauya kudurar Ubangiji ga bayinSa shiyasa mu kan ce wai tun ran gini….Bayan duka wasu shirye shirye da hassada daga bangaren ‘yan bakinciki irin su Jume da ‘ya’yanta da kuma Salame mai son maso wani, da azahar din wata asabar aka daura auren Zayyan Muhammad Tureta da Mairama Ali Gidado. Sai kuma Salisu Lawan da Ummusalma Ali Gidado. Kowacce cikinsu angonta yayi bajinta gwargwadon aljihunsa ya yi mata kayan lefe. Ko ba’a fada ba kayan Salame sun kere na Mairamu duk da Zayyan din ma baiyi kasa a gwiwa ba, amma a haka Salame ta dauko ido ta sakawa kayan Mairama a ganinta da ita su ka fi dacewa.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: G
*….TUN RAN ZANE*
Hakan take domin kuwa yau ne za’a kai amaren dakunansu. Dakin Yadikko aka tarasu Malamijo ya shigo zaiyi musu nasiha ta karshe safiyar lahadi.
Kallonsu yayi daya bayan daya sannan ya juya wurin Yadikko.
"Me ake cewa ne idan za'a kai amarya?"
"Ko addu'a ai ka yi musu"
Hularsa ya turo gaba "abi miji sau da kafa shine shawarata gareku. Banda tsiwa ko rashin kunya sannan ayi ta hakuri. Duk wadda ta kaso aurenta babu abinda ya shalleni ah to. Allah bada zaman lafiya ku tashi ku tafi kada ayi dare Mairama tana da nisa. Birnin Shehu kwai dan karen tafiya daga nan kamar za'a ya da shege"
Wannan magana ma sai da ta taba ran Salame. Babu wanda ya damu da cewa ita ke son Zayyan har ake wani zancen nisan garin. Haka su ka fito suna ta kuka, kowacce da abinda take yiwa. Salame kukan rabuwa da masoyi take yi don tasan an riga an cuceta an rabata da Zayyan. Mairama kuwa kukanta bai wuce na rabuwa da 'yar uwarta da gidan nasu duk da ba dadinsa suke ji ba, sai kuma fargabar sabuwar rayuwar da zata fara.
Akori kura biyu ke biye da motocin daukar amaren na kayan dakinsu da aka samu Malamijo yayi. Gadaje daidai ne da saitin kujeru da kuma kayan kitchen. Gidan Salame aka fara tsayawa a Kofar na'isa babban gida ne mai bangare uku na Salisu da 'yan uwansa. Yadikko da Hajjo su ne zasu tsaya a nan ayi jere tare da 'yan uwan Ta Madina. Basuyi mamaki ba ganin har sunyi jeren katon gado a daki daya da kwaba da madubi masu kyau daidai da zamani wanda Ta Madina da 'yan uwanta suka yi. A falon ma sunyi mata kujeru manya da suka fi na wajen Malamijo an malale kasan da leda mai ado da ta dace da labulen da suka yi mata. Kayan da suka zo dasu wani daki guda aka nuna musu suka jera kujerun da gadon ya dauke su tsaf saboda ba wani yawa garesu ba.
Kannen Ta Madina suna aiki suna yabawa su Yadikko magana wai kudin Malamijo bai tsinana musu komai ba. To su din ma basu tanka ba tunda idan anbi ta barawo abi ta mabi sawu.
Dije da Inno su ne jagora a tafiya kai Mairama nata gidan. Yamma likis suka isa Allah Yasa ba wata gayya ce ba basu fi su biyar ba. Sanin cewa idan ya kaisu gidansu Jume sai ta saka shi jin kunya ya nemi alfarmar kanin babansa zai saukesu a gidan kafin su yi jeren. Nan su ka kwana ana ta tarairayarsu. Mami matar Captain Mustapha ita ma tayi abinci mai yawa suka je aka yi taro a gidan. Jume ko zuwa bata yi ba amma 'ya'yanta mata sun je suna ta yada magana wai kalen dangi ya guji nasa asalin. Haka nan 'yan uwan Mal.Muhammadu sun je da yawansu.
Da safe Hadir ne yaje daukosu aka kaisu gidan da aka bawa Zayyan a bangaren gidajen da suke cikin barikin. Daki daya ne kato da bandaki a cikinsa sai falo madaidaici da kitchen karami. Bata zo da komai ba sai iya kayan da Malamijo yayi mata. Anyi jere lafiya a daren aka kawo amarya dakinta su kuma suka koma Sumaila washegari.
Zaman Zayyan da Mairama abin burgewa ne da sha'awa ga duk wanda ya sansu kuma yake mu'amala dasu. Babu abinda ya rageta dashi ta fannin soyayya da kyautatawa. Ita ma a nata bangaren tana binsa sau da kafa da biyayya da tattali. Yanayin gidansu yasa ta iya girki bashi da matsala ta wannan fannin ma.
Satinsu biyar da aure Zainab ta tare matar Hadir. Mami dadi ya isheta ga hausawa 'yan uwanta a kusa duk da nasu gidajen suna bangare daban. Sunfi girma da kyau. Su Mairama kuwa layinsu daya da Zainab. Hade kai suka yi suna zaman gaskiya da bawa juna shawarwari. Mami ce babba amma Zainab duk ta fisu wayewa. Mairama kuwa dama albarkacin boko ta san wasu abubuwan amma kifin rijiya ce. Idan suna hira abin dariya, Mairama kana jin hausarta zaka gane bafillatana ce, Zainab sakkwatanci ziryan ita kuma Mami Hausar Katsina.
Yau juma'a Mairama tana cikin girki kafin dawowar Zayyan taji sallamar Awwab. Kowa yasan dan gidanta ne na gaban goshi. Zainab har ta gaji da mita ta kama kannensa Zahra da Fauziyya a matsayin nata.
Kitchen din ya shigo ya sameta tana yanka salad.
"Anti kawo in yanka"
"So ka ke Anti Zainab ta shigo ta soma tsokanarka ko" tace tana murmushi.
"Mami tace in gaisheki kuma zata zo kiyi mata kalba anjima"
"Kaje kace mata nace sai ta shigo sannan ka dawo ka ci abinci"
Fita yayi zai tafi ya ga ta biyo bayansa a guje ta shige bandaki tana kakarin amai. Awwab ya rasa me zaiyi sai kuka yana mata sannu. Ita ke fama da matsananciyar tashin zuciya da amai kamar zata fitar da kayan cikinta amma kuma ita ke bashi hakuri saboda yadda ya gigice mata.
"Awwab ka dena kuka mana" tace cikin rashin kuzari.
Kuka yake sosai "to ki dena aman"
"Na gama muje ka zuba abincin idan kaci sai ka tafi"
Kallonta yayi tana dafa bango tana daga kafa da kyar. Hannunta ya rike har kan kujera yace "In fadawa Mami ko Anti Zainab?"
Da sauri ta dakatar dashi "a'a kada ka fadawa kowa na ji sauki"
“Ajiya kika ban ko me?”
Zuciya ta soma cin Mairama saboda ta tabbatar dazu da gangan Salame ta fita duk da tasan kiranta take yi. Wai ma me ya kaita wurin Zayyan din.
“Shikenan”
“Shikenan me?”
Maimakon amsar fatar baki sai gani tayi Mairama tasa iyakar karfinta tana jijjiga kofofin sif din tana neman ballesu. Da saurinta ta mike don ta dakatar da ita.
“Meye hakan?”
“Dame yayi miki kama? Balleta zanyi tunda mukullin ya bata in nemi kayan sawa”
“Saboda saurayinki zai zo?”
Salame tace da kaushin murya.
“Adda Salame idan wani abu nayi miki ki fito fili ki fada min amma ba ki zauna kullum kina jin haushina kina min tsaki ba. Kin sani wallahi ba don ke Addata bace ….”
“Sai ki dakeni ko ba haka ba”
Wata fuzga ta kaiwa kofar sai gata ta bude ta dauko kayan da zata saka bata sake kula Salame ba. Gefe ita ma ta koma tana ta hucin kishi ganin yadda Mairama ta zage tana kwalliya saboda Zayyan.
“Aikin banza ki gama adon yace ya fasa tunda yanzu yasan daga wane irin gida ki ka fito.”
A tsorace ta waiwayo “fada masa kika yi?”
Salame sai ta tsame kafarta tayi waje. Tana zaune tana jira a raba tuwon gidan na al’ada a bata nata Mairama ta fito bayan an fada mata dawowar Zayyan. Da tazo wucewa tana jin uban tsakin da Salame taja har sai da Dije ta soma sababi ko da ita take.
Hira suka yi cikin nutsuwa rabi duk shi yake maganar saboda kunya irin ta Fulani. Tana son tambayarsa game da abubuwan da take zargin Salame ta fada masa amma ta gaza. Kamar ya sani kuwa da kansa ya shiga bata labarin asalinsa da rayuwarsa ta baya zuwa yanzu. Tausayinsa taji har idanunta su ka ciko da kwalla.
“Bana so yanayin rayuwar gidanku ya sanya ki fara tunanin zan gujeki ko hakan zai shafi zamantakewarmu. Gidajen da muka fito daban, sannan gidan da zamu samarwa kanmu da ‘ya’yan da nake burin ki haifa min shima daban.”
Tamkar kasa ta zage ta hadiyeta taji saboda kunyar kalaminsa na karshe. Da dabara ya samu ya rinka kwantar mata da hankali da kwadaita mata irin tanadin da yake mata idan ta zama mallakinsa. Ba shi ya bar gidan ba sai tara da rabi na dare. Washegari ya sake zuwa kuma a ranar ne ya sanar da Malamijo zuwan kawunnansa idan ya koma.
“Abin da nake so da kai shine ka fada musu su taho da sadakinsu ayi komai a kare. Yaran nan sun zaunu babu dalilin ayi ta jan lokaci. Budurwa kamar Mairama ta bawa shekaru shatakwas baya harda watanni ina kallonta tana kallona. Ga yayarta ita ma zan fadawa yaron nan Salisu sai ayi a lokaci guda”
Dadi maganar ta Malamijo tayi masa yayi na’am da ita. Ana gobe zai koma yana jiran fitowar Mairama sai ga Salame da ta shiga tashin hankali sakamakon gabatowar aurenta da Salisun da bata so. Hanyar waje tayi a daidai inda yake zaune ta jefa masa takarda ta fita. Ba nisa tayi ba tana layin bayan gidansu tana jiran ya karanta wasikar yazo ya sameta.
Layuka kadan ya karanta inda take sanar dashi son da take masa da kuma jiransa da take a bayan layi idan ya amince yazo ya sameta. Mairama ce tayi sallama sai kawai ya yayyaga takardar ya dunkuleta a hannunsa.
Sun jima suna hira yana fada mata haduwarsu ta gaba ta zama tasa tana dariya a hankali Salame ta dawo kamar kububuwa. Ta kwashi awa guda da doriya tana jiransa bai zo ba. Yanzu da ta shigo takardar hannunsa ya watsa a iska ko kallonta baiyi ba. Zuciyarta kamar za ta fashe saboda bakinciki ta wuce ciki.
Bahaushe ma yasan babu wanda ya isa ya sauya kudurar Ubangiji ga bayinSa shiyasa mu kan ce wai tun ran gini….Bayan duka wasu shirye shirye da hassada daga bangaren ‘yan bakinciki irin su Jume da ‘ya’yanta da kuma Salame mai son maso wani, da azahar din wata asabar aka daura auren Zayyan Muhammad Tureta da Mairama Ali Gidado. Sai kuma Salisu Lawan da Ummusalma Ali Gidado. Kowacce cikinsu angonta yayi bajinta gwargwadon aljihunsa ya yi mata kayan lefe. Ko ba’a fada ba kayan Salame sun kere na Mairamu duk da Zayyan din ma baiyi kasa a gwiwa ba, amma a haka Salame ta dauko ido ta sakawa kayan Mairama a ganinta da ita su ka fi dacewa.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: G
*….TUN RAN ZANE*
Hakan take domin kuwa yau ne za’a kai amaren dakunansu. Dakin Yadikko aka tarasu Malamijo ya shigo zaiyi musu nasiha ta karshe safiyar lahadi.
Kallonsu yayi daya bayan daya sannan ya juya wurin Yadikko.
"Me ake cewa ne idan za'a kai amarya?"
"Ko addu'a ai ka yi musu"
Hularsa ya turo gaba "abi miji sau da kafa shine shawarata gareku. Banda tsiwa ko rashin kunya sannan ayi ta hakuri. Duk wadda ta kaso aurenta babu abinda ya shalleni ah to. Allah bada zaman lafiya ku tashi ku tafi kada ayi dare Mairama tana da nisa. Birnin Shehu kwai dan karen tafiya daga nan kamar za'a ya da shege"
Wannan magana ma sai da ta taba ran Salame. Babu wanda ya damu da cewa ita ke son Zayyan har ake wani zancen nisan garin. Haka su ka fito suna ta kuka, kowacce da abinda take yiwa. Salame kukan rabuwa da masoyi take yi don tasan an riga an cuceta an rabata da Zayyan. Mairama kuwa kukanta bai wuce na rabuwa da 'yar uwarta da gidan nasu duk da ba dadinsa suke ji ba, sai kuma fargabar sabuwar rayuwar da zata fara.
Akori kura biyu ke biye da motocin daukar amaren na kayan dakinsu da aka samu Malamijo yayi. Gadaje daidai ne da saitin kujeru da kuma kayan kitchen. Gidan Salame aka fara tsayawa a Kofar na'isa babban gida ne mai bangare uku na Salisu da 'yan uwansa. Yadikko da Hajjo su ne zasu tsaya a nan ayi jere tare da 'yan uwan Ta Madina. Basuyi mamaki ba ganin har sunyi jeren katon gado a daki daya da kwaba da madubi masu kyau daidai da zamani wanda Ta Madina da 'yan uwanta suka yi. A falon ma sunyi mata kujeru manya da suka fi na wajen Malamijo an malale kasan da leda mai ado da ta dace da labulen da suka yi mata. Kayan da suka zo dasu wani daki guda aka nuna musu suka jera kujerun da gadon ya dauke su tsaf saboda ba wani yawa garesu ba.
Kannen Ta Madina suna aiki suna yabawa su Yadikko magana wai kudin Malamijo bai tsinana musu komai ba. To su din ma basu tanka ba tunda idan anbi ta barawo abi ta mabi sawu.
Dije da Inno su ne jagora a tafiya kai Mairama nata gidan. Yamma likis suka isa Allah Yasa ba wata gayya ce ba basu fi su biyar ba. Sanin cewa idan ya kaisu gidansu Jume sai ta saka shi jin kunya ya nemi alfarmar kanin babansa zai saukesu a gidan kafin su yi jeren. Nan su ka kwana ana ta tarairayarsu. Mami matar Captain Mustapha ita ma tayi abinci mai yawa suka je aka yi taro a gidan. Jume ko zuwa bata yi ba amma 'ya'yanta mata sun je suna ta yada magana wai kalen dangi ya guji nasa asalin. Haka nan 'yan uwan Mal.Muhammadu sun je da yawansu.
Da safe Hadir ne yaje daukosu aka kaisu gidan da aka bawa Zayyan a bangaren gidajen da suke cikin barikin. Daki daya ne kato da bandaki a cikinsa sai falo madaidaici da kitchen karami. Bata zo da komai ba sai iya kayan da Malamijo yayi mata. Anyi jere lafiya a daren aka kawo amarya dakinta su kuma suka koma Sumaila washegari.
Zaman Zayyan da Mairama abin burgewa ne da sha'awa ga duk wanda ya sansu kuma yake mu'amala dasu. Babu abinda ya rageta dashi ta fannin soyayya da kyautatawa. Ita ma a nata bangaren tana binsa sau da kafa da biyayya da tattali. Yanayin gidansu yasa ta iya girki bashi da matsala ta wannan fannin ma.
Satinsu biyar da aure Zainab ta tare matar Hadir. Mami dadi ya isheta ga hausawa 'yan uwanta a kusa duk da nasu gidajen suna bangare daban. Sunfi girma da kyau. Su Mairama kuwa layinsu daya da Zainab. Hade kai suka yi suna zaman gaskiya da bawa juna shawarwari. Mami ce babba amma Zainab duk ta fisu wayewa. Mairama kuwa dama albarkacin boko ta san wasu abubuwan amma kifin rijiya ce. Idan suna hira abin dariya, Mairama kana jin hausarta zaka gane bafillatana ce, Zainab sakkwatanci ziryan ita kuma Mami Hausar Katsina.
Yau juma'a Mairama tana cikin girki kafin dawowar Zayyan taji sallamar Awwab. Kowa yasan dan gidanta ne na gaban goshi. Zainab har ta gaji da mita ta kama kannensa Zahra da Fauziyya a matsayin nata.
Kitchen din ya shigo ya sameta tana yanka salad.
"Anti kawo in yanka"
"So ka ke Anti Zainab ta shigo ta soma tsokanarka ko" tace tana murmushi.
"Mami tace in gaisheki kuma zata zo kiyi mata kalba anjima"
"Kaje kace mata nace sai ta shigo sannan ka dawo ka ci abinci"
Fita yayi zai tafi ya ga ta biyo bayansa a guje ta shige bandaki tana kakarin amai. Awwab ya rasa me zaiyi sai kuka yana mata sannu. Ita ke fama da matsananciyar tashin zuciya da amai kamar zata fitar da kayan cikinta amma kuma ita ke bashi hakuri saboda yadda ya gigice mata.
"Awwab ka dena kuka mana" tace cikin rashin kuzari.
Kuka yake sosai "to ki dena aman"
"Na gama muje ka zuba abincin idan kaci sai ka tafi"
Kallonta yayi tana dafa bango tana daga kafa da kyar. Hannunta ya rike har kan kujera yace "In fadawa Mami ko Anti Zainab?"
Da sauri ta dakatar dashi "a'a kada ka fadawa kowa na ji sauki"