Sashe 72
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daddy yana gidan Baba Hadir saboda Mama da Ummi sun hadu a gidan Mami suna girki. Suna shiga Awwab yayi ido hudu da Ummin da yake yiwa wasan buya.
"Allah Ya kamaka Awwab babu alkawari...oh ni Mairama 'yan sa ido sai su zuba ruwa a kasa su sha sunyi nasarar shiga tsakanina da dana"
Mama sai dariya "wai 'yan sa ido, kaga Awwab gara ka kamani don Ummi da Mami 'yan hamayya club ne"
Shi dai kunya ma suke bashi ya gaishe su duka yana neman wurin zama Ibrahim ya nuna masa dakin da aka tanadar masa don zaman hotel ya kare masa a garin tunda babu fuskar zuwa gidan Mummy.
"Kunga yadda Awwab ya sake zama babban mutum kuwa? Ni dai gaskiya ayi masa aure haka nan" cewar Mama
"To ya hau dokin zuciya yana ta fushi damu akan tafiyar Radhiya" Mama ta bata amsa.
"Shashanci kai, yana nan wallahi buzayen can zasu fara kawo mata hari. Wami hotonta da ta turo min fa Allah nayi mamakinta sosai. Ki turo min shi Mami idan kun huta ya kamata na karanta masa fari da baki"
Ummi tace "gidana zai fara zuwa akwai tamu dashi, duk abinsa sai yaje gidansu Ghazalatu ya gaishe da iyayensa wannan karon"
Mami ta ce "ni dai a nuna min nawa dakin naje nayi wanka yunwa nake ji"
"Ummi inkiya akeyi mana mu fita fa...kinga ni nayi nan kafin ki fara jin gyaran murya Daddy ya zo oyoyo"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, Zainab baki da dama wallahi. Amma zan fada masa tunda sharrin naki harda shi"
"Rufa min asiri don Allah" sai da ta kusa kai bakin kofa ta juyo "yo ai dai gaskiya na fada idan kin musa mu dawo mu tayaki wuni"
"Allah Ya shiryeki kina nan kina zance sai ya shigo" Ummi tace ta rigata fita.
Dawowa da baya Mama tayi tana nunawa Mami fridge "nayi miki ajiya fa ya kamata ki fara dubawa ki sha..."
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mami sai da ta waiga baya ta tabbatar su kadai ne sannan ta girgiza kai "kinyi sa'a da yara a gidan nan da na miki dan biki. Zan zo har gida na sameki"
Da dariya Mama ta bi bayan Ummi saboda yadda ta tsani gidan nata. Komai warinsa take ji ta rinka amai kenan. Ibrahim abu duk ya dame shi Allah bai sa ya fahimci kani ko kanwarsa ke tafe ba.
**********
Kwana biyar da dawowarsu Mami Major ya sami waya daga His Excellency yana shaida masa ya shigo Abuja ko zasu zo shi da Hadir su gaisa.
Mami ya fadawa ta rike baki "yanzu Daddy gwamna da kansa yake kiranka?"
"Mutumin kirkinsa yayi yawa har ina jin tsoro. Ni bana son shigewa 'yan siyasa"
"In sha Allahu alkhairi ya kawo shi garemu. Allah Ya sani bamu cuci kowa ba bazai hadamu da macuci ba"
"Shiyasa nake son Hassanata."
Dariya tayi tana jindadin yadda mijinta yake yaba mata komai kankantar abu.
"Ki sanar da danki ya shirya muje tare"
"Yau kuma? Awwab ya ga ta kansa. Umminsa ta saka shi a gaba akan zuwa gidan Gambo sai cewa yake zaije amma har yau shiru. Ni dama abin nasu da Hussaina ya dena bani mamaki. Biki ne zasu yi na huce haushi anki sakani cikin komai ba sai na kawo ido na saka musu ba"
"Kece babba fa Hassana, lokaci yana tafiya. Ina ganin ya kamata kiyi yunkuri da kanki kamar yadda Mairama ta baki shawara. Kunje kuna rigimarku ta mata kun bar min yaro yana hanging"
"Ya bar kansa dai. Idan yayi sake wani ya nemi Radhiya a Nijar shi ya sani"
Daddy ya mike "to ba dama na baki ba ki saka min yaro a gaba."
"Na nawa kuma" tace tana murmushi.
Washegari da yamma Major, Baba Hadir da Awwab suka tafi gidan gwamnatin Plateau da yake unguwar Asokoro a Abuja. Kofar gida ya fito da kansa ya tarbesu bayan an bude kusu gate sun shigo. Da murmushi a saman fuskarsa yace "wannan me Awwab ko?"
Awwab ya rissina kai Excellency ya kamo hannun damansa suka yi musabaha sannan suka shiga ciki.
"Nayi zaton zaku taho da iyalinku shiyasa muka taho da Arifah da mamanta. Bari na kirasu ku gaisa"
Waya ya kira sai ga matarsa Haj Rabi da Arifah sun fito. Suna shigowa idanun Arifah suka sauka akan Awwab mamaki karara ya bayyana akan fuskarta. Sunfi shekara da haduwa amma ina zata manta shi bayan bata sati biyu bata kira shi a waya ba.
"Captain M.A Mustapha?" Tace tana rike baki.
Excellency ya saki fuska "kin san shi ne?"
Murmushi tayi ta gyada kai tana hango nasara a tattare da soyayyar da take yi masa. Ace gashi har cikin gidansu kuma da ga mutumin da Dad dinta ya daukesu da matukar kima a idanunsa.
"Ikon Allah, ashe sun san juna mu sai yanzu Allah Ya nufa"
Arifah dai murna kamar me ta fita taje ta sake kwalliya ta tura wata mai aikin ta kira mata shi zuwa garden din gidan.
Mai aikin kuwa taje ta isar da sako gashi a gaban mahaifinta dole ya tashi. Shi gabadaya tunaninsa ya kasa tuna wacece ita.
Takunsa kadai abin kallo ne a lokacin da yake tahowa gareta cikin shiga ta manyan kaya. Dinkin irin wanda matasa suke yayi ne riga ta dan zarce gwiwa amma hannunta da kadan ya wuce gwiwar hannu. Yadin yayi masa kyau sosai babu hula a kansa sai gyaran fuska da yayi batare da sake aski ba.
Tana zaune akan wata kujera karkashin wani abu da akayi da kaba ya bada sassanyar inuwa ya iso ya tsaya bayan tafiyar wadda tayi masa jagora.
"Zauna mana" Arifah tace tana murmushi.
Kamar bazai zauna ba sai kuma dai ya tuna cewa nan gidansu ne ga kuma irin karamcin mahaifinta ga nasa iyayen. Tunda ya zauna bata ce komai ba sai aikin kallonsa tana yaba komai na halittarsa.
"Ya dai?" Ya tambayeta yana hade rai.
"Hmmm Captain baka ganeni ba da gaske?"
Kalmar Captain din kawai tasa ya tuna a ina ya saba jinta "kece mai kirana?"
"Arifah sunana" ta bashi amsa da murmushi "Captain ka wahalar dani ko ince kana kan wahalar dani sai kuma ga ka a gidanmu abinda ban taba zata ba"
"Allah Yasa dai bazaki sa a kulleni ba a yar da key din"
Dariya tayi "ko daya sai dai ina neman sanin dalilin wannan mugun jan aji da yakamata ace ni nake yi maka"
Kai tsaye yace mata "na sha fada miki na kusa aure"
"Na dade ina kiranka Captain amma har yau ba'ayi auren ba sai kora da hali da kake yi min."
Kunyar abubuwan da ya rinka yi mata yaji da kuma rashin dacewarsu "kiyi hakuri maybe mun fara on the wrong side. Sunana Awwab ke fa?"
"Arifah"
"Arifah ina da wadda nake so sabani ya shiga tsakaninmu. Kiyi hakuri idan hakan ya bata miki amma iya gaskiyata shine bazan iya hadata da kowa ba"
Ya dade yana fada mata shiyasa bata yi wani mamaki ba "she is lucky amma nima zan gwada tawa sa'ar idan ka amince"
"Kada muyi haka dake Arifah. Akwai danganta mai girma yanzu tsakaninmu. Mahaifinki ya taimakawa nawa iyayen kamar yadda naji labarin wadda nake so din itama nata mahaifin ya taimaki naki. Mu duka wata alaka ce tsakaninmu da bazan so soyayya ta sake batawa ba kamar yadda tayi min a abaya."
"Wai kana nufin Alheran kake so?"
"Ya akayi kika gane?"
"Saboda ita kadai ce wadda nasan babanta ya yiwa Dad abinda kullum baya gajiya da bada labarinsa yana binsa da addu'a"
Awwab da ya koma mai wuyar sha'ani sai gashi saboda hirar Alheran ce ya sake yana yiwa Arifah labarinta. Taji tausayinsu matuka da taji dalilin rabuwarsu.
"Na hakura ba don bazan iya ba sai don Alheran din nan da ban taba gani ba nasan tafi karfina indai a kan ka ne. Dad dina da naka duka owe their lives to hers. Ina son Dad dina dole ne in taya shi kyautatawa Alheran da family dinta"
"Nagode sosai Arifah" Awwab yace yana mikewa tsaye.
"Tunda na zama kanwarka Allah Yasa ka dena kin daukar wayata"
Yana tafiya ta jiyo shi yace "daga yanzu da kaina zan rinka kiranki"
Kyakkyawar alaka da aka gina bisa gaskiya da amana ita ce ta cigaba da wanzuwa tsakanin gidajen mutanen nan guda hudu. Wato gidan gwamna, Major, Baba Hadir da Mairama matar Tureta.
His Excellency Nasiruddeen ya cika alkawari domin kuwa har cikin gida aka je aka dauko masa Maikudi yasa aka kulle shi. Idan mutum yana cin kasa ya kiyayi ta shuri.
Radhiya ta mayarda kai sosai a karatunta Nasara tana goya mata baya. Akwai shakuwa mai karfi tsakaninta da Yousuf yana bata kulawa sosai duk domin sharar fagen gabatar da soyayyarsa gareta a gaba. Abubuwa da dama na halayenta rashin Awwab ya sanyata ta barsu sai dai shagwaba kam ko Zayyana albarka. Tazo Nigeria daga Niger ta zaga dangi sosai lokacin Awwab ya koma aiki.
A lokacin ne kuma akayi bikin Ghazalatu da Nura. Hadadden gift Awwab ya aiko mata dashi na aure amma bai sami damar zuwa ba saboda training course da ya tafi na shekara daya a Ukraine zai sami karin mukami idan ya dawo. Habaici da bakaken maganganu duk da Mami tana bakin kokarinta akan kannen nata sai da suka rinka yaba mata. Ummansu har tara su tayi ta sanar dasu cewa saboda zumuncinsu kada ya baci Mairama ta raba 'yarta da Awwab gashi har yanzu ya kasa aure. Hussaina sai cewa tayi dama can kwadayi ne ya kawosu da suka ga anfi karfinsu sai suka ja baya. Maganar ta yiwa Mami ciwo amma bahaushe yace wai gani ya kori ji. Idan kuwa hakane to zata basu mamaki su duka wallahi. Bazata ce musu komai game da tsatson da Radhiya ta fito ba sai dai ido ya gani anayi.
Duk wannan maganganun anyisu ne ranar Kamun Ghazalatu a Katsina kuma Mama taji saboda cikinta ya fara nauyi tafi son zama wuri daya shiyasa tana dakin suke yi. Da daddare suna dakin Mami a gidansu na Katsina daga ita sai Ummi ta tayar da maganar.
"Mairama dan taso muyi magana don Allah"
"Allah Yasa lafiya uwar 'yan hudu"
"Allah Ya kamaka Awwab babu alkawari...oh ni Mairama 'yan sa ido sai su zuba ruwa a kasa su sha sunyi nasarar shiga tsakanina da dana"
Mama sai dariya "wai 'yan sa ido, kaga Awwab gara ka kamani don Ummi da Mami 'yan hamayya club ne"
Shi dai kunya ma suke bashi ya gaishe su duka yana neman wurin zama Ibrahim ya nuna masa dakin da aka tanadar masa don zaman hotel ya kare masa a garin tunda babu fuskar zuwa gidan Mummy.
"Kunga yadda Awwab ya sake zama babban mutum kuwa? Ni dai gaskiya ayi masa aure haka nan" cewar Mama
"To ya hau dokin zuciya yana ta fushi damu akan tafiyar Radhiya" Mama ta bata amsa.
"Shashanci kai, yana nan wallahi buzayen can zasu fara kawo mata hari. Wami hotonta da ta turo min fa Allah nayi mamakinta sosai. Ki turo min shi Mami idan kun huta ya kamata na karanta masa fari da baki"
Ummi tace "gidana zai fara zuwa akwai tamu dashi, duk abinsa sai yaje gidansu Ghazalatu ya gaishe da iyayensa wannan karon"
Mami ta ce "ni dai a nuna min nawa dakin naje nayi wanka yunwa nake ji"
"Ummi inkiya akeyi mana mu fita fa...kinga ni nayi nan kafin ki fara jin gyaran murya Daddy ya zo oyoyo"
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, Zainab baki da dama wallahi. Amma zan fada masa tunda sharrin naki harda shi"
"Rufa min asiri don Allah" sai da ta kusa kai bakin kofa ta juyo "yo ai dai gaskiya na fada idan kin musa mu dawo mu tayaki wuni"
"Allah Ya shiryeki kina nan kina zance sai ya shigo" Ummi tace ta rigata fita.
Dawowa da baya Mama tayi tana nunawa Mami fridge "nayi miki ajiya fa ya kamata ki fara dubawa ki sha..."
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Mami sai da ta waiga baya ta tabbatar su kadai ne sannan ta girgiza kai "kinyi sa'a da yara a gidan nan da na miki dan biki. Zan zo har gida na sameki"
Da dariya Mama ta bi bayan Ummi saboda yadda ta tsani gidan nata. Komai warinsa take ji ta rinka amai kenan. Ibrahim abu duk ya dame shi Allah bai sa ya fahimci kani ko kanwarsa ke tafe ba.
**********
Kwana biyar da dawowarsu Mami Major ya sami waya daga His Excellency yana shaida masa ya shigo Abuja ko zasu zo shi da Hadir su gaisa.
Mami ya fadawa ta rike baki "yanzu Daddy gwamna da kansa yake kiranka?"
"Mutumin kirkinsa yayi yawa har ina jin tsoro. Ni bana son shigewa 'yan siyasa"
"In sha Allahu alkhairi ya kawo shi garemu. Allah Ya sani bamu cuci kowa ba bazai hadamu da macuci ba"
"Shiyasa nake son Hassanata."
Dariya tayi tana jindadin yadda mijinta yake yaba mata komai kankantar abu.
"Ki sanar da danki ya shirya muje tare"
"Yau kuma? Awwab ya ga ta kansa. Umminsa ta saka shi a gaba akan zuwa gidan Gambo sai cewa yake zaije amma har yau shiru. Ni dama abin nasu da Hussaina ya dena bani mamaki. Biki ne zasu yi na huce haushi anki sakani cikin komai ba sai na kawo ido na saka musu ba"
"Kece babba fa Hassana, lokaci yana tafiya. Ina ganin ya kamata kiyi yunkuri da kanki kamar yadda Mairama ta baki shawara. Kunje kuna rigimarku ta mata kun bar min yaro yana hanging"
"Ya bar kansa dai. Idan yayi sake wani ya nemi Radhiya a Nijar shi ya sani"
Daddy ya mike "to ba dama na baki ba ki saka min yaro a gaba."
"Na nawa kuma" tace tana murmushi.
Washegari da yamma Major, Baba Hadir da Awwab suka tafi gidan gwamnatin Plateau da yake unguwar Asokoro a Abuja. Kofar gida ya fito da kansa ya tarbesu bayan an bude kusu gate sun shigo. Da murmushi a saman fuskarsa yace "wannan me Awwab ko?"
Awwab ya rissina kai Excellency ya kamo hannun damansa suka yi musabaha sannan suka shiga ciki.
"Nayi zaton zaku taho da iyalinku shiyasa muka taho da Arifah da mamanta. Bari na kirasu ku gaisa"
Waya ya kira sai ga matarsa Haj Rabi da Arifah sun fito. Suna shigowa idanun Arifah suka sauka akan Awwab mamaki karara ya bayyana akan fuskarta. Sunfi shekara da haduwa amma ina zata manta shi bayan bata sati biyu bata kira shi a waya ba.
"Captain M.A Mustapha?" Tace tana rike baki.
Excellency ya saki fuska "kin san shi ne?"
Murmushi tayi ta gyada kai tana hango nasara a tattare da soyayyar da take yi masa. Ace gashi har cikin gidansu kuma da ga mutumin da Dad dinta ya daukesu da matukar kima a idanunsa.
"Ikon Allah, ashe sun san juna mu sai yanzu Allah Ya nufa"
Arifah dai murna kamar me ta fita taje ta sake kwalliya ta tura wata mai aikin ta kira mata shi zuwa garden din gidan.
Mai aikin kuwa taje ta isar da sako gashi a gaban mahaifinta dole ya tashi. Shi gabadaya tunaninsa ya kasa tuna wacece ita.
Takunsa kadai abin kallo ne a lokacin da yake tahowa gareta cikin shiga ta manyan kaya. Dinkin irin wanda matasa suke yayi ne riga ta dan zarce gwiwa amma hannunta da kadan ya wuce gwiwar hannu. Yadin yayi masa kyau sosai babu hula a kansa sai gyaran fuska da yayi batare da sake aski ba.
Tana zaune akan wata kujera karkashin wani abu da akayi da kaba ya bada sassanyar inuwa ya iso ya tsaya bayan tafiyar wadda tayi masa jagora.
"Zauna mana" Arifah tace tana murmushi.
Kamar bazai zauna ba sai kuma dai ya tuna cewa nan gidansu ne ga kuma irin karamcin mahaifinta ga nasa iyayen. Tunda ya zauna bata ce komai ba sai aikin kallonsa tana yaba komai na halittarsa.
"Ya dai?" Ya tambayeta yana hade rai.
"Hmmm Captain baka ganeni ba da gaske?"
Kalmar Captain din kawai tasa ya tuna a ina ya saba jinta "kece mai kirana?"
"Arifah sunana" ta bashi amsa da murmushi "Captain ka wahalar dani ko ince kana kan wahalar dani sai kuma ga ka a gidanmu abinda ban taba zata ba"
"Allah Yasa dai bazaki sa a kulleni ba a yar da key din"
Dariya tayi "ko daya sai dai ina neman sanin dalilin wannan mugun jan aji da yakamata ace ni nake yi maka"
Kai tsaye yace mata "na sha fada miki na kusa aure"
"Na dade ina kiranka Captain amma har yau ba'ayi auren ba sai kora da hali da kake yi min."
Kunyar abubuwan da ya rinka yi mata yaji da kuma rashin dacewarsu "kiyi hakuri maybe mun fara on the wrong side. Sunana Awwab ke fa?"
"Arifah"
"Arifah ina da wadda nake so sabani ya shiga tsakaninmu. Kiyi hakuri idan hakan ya bata miki amma iya gaskiyata shine bazan iya hadata da kowa ba"
Ya dade yana fada mata shiyasa bata yi wani mamaki ba "she is lucky amma nima zan gwada tawa sa'ar idan ka amince"
"Kada muyi haka dake Arifah. Akwai danganta mai girma yanzu tsakaninmu. Mahaifinki ya taimakawa nawa iyayen kamar yadda naji labarin wadda nake so din itama nata mahaifin ya taimaki naki. Mu duka wata alaka ce tsakaninmu da bazan so soyayya ta sake batawa ba kamar yadda tayi min a abaya."
"Wai kana nufin Alheran kake so?"
"Ya akayi kika gane?"
"Saboda ita kadai ce wadda nasan babanta ya yiwa Dad abinda kullum baya gajiya da bada labarinsa yana binsa da addu'a"
Awwab da ya koma mai wuyar sha'ani sai gashi saboda hirar Alheran ce ya sake yana yiwa Arifah labarinta. Taji tausayinsu matuka da taji dalilin rabuwarsu.
"Na hakura ba don bazan iya ba sai don Alheran din nan da ban taba gani ba nasan tafi karfina indai a kan ka ne. Dad dina da naka duka owe their lives to hers. Ina son Dad dina dole ne in taya shi kyautatawa Alheran da family dinta"
"Nagode sosai Arifah" Awwab yace yana mikewa tsaye.
"Tunda na zama kanwarka Allah Yasa ka dena kin daukar wayata"
Yana tafiya ta jiyo shi yace "daga yanzu da kaina zan rinka kiranki"
Kyakkyawar alaka da aka gina bisa gaskiya da amana ita ce ta cigaba da wanzuwa tsakanin gidajen mutanen nan guda hudu. Wato gidan gwamna, Major, Baba Hadir da Mairama matar Tureta.
His Excellency Nasiruddeen ya cika alkawari domin kuwa har cikin gida aka je aka dauko masa Maikudi yasa aka kulle shi. Idan mutum yana cin kasa ya kiyayi ta shuri.
Radhiya ta mayarda kai sosai a karatunta Nasara tana goya mata baya. Akwai shakuwa mai karfi tsakaninta da Yousuf yana bata kulawa sosai duk domin sharar fagen gabatar da soyayyarsa gareta a gaba. Abubuwa da dama na halayenta rashin Awwab ya sanyata ta barsu sai dai shagwaba kam ko Zayyana albarka. Tazo Nigeria daga Niger ta zaga dangi sosai lokacin Awwab ya koma aiki.
A lokacin ne kuma akayi bikin Ghazalatu da Nura. Hadadden gift Awwab ya aiko mata dashi na aure amma bai sami damar zuwa ba saboda training course da ya tafi na shekara daya a Ukraine zai sami karin mukami idan ya dawo. Habaici da bakaken maganganu duk da Mami tana bakin kokarinta akan kannen nata sai da suka rinka yaba mata. Ummansu har tara su tayi ta sanar dasu cewa saboda zumuncinsu kada ya baci Mairama ta raba 'yarta da Awwab gashi har yanzu ya kasa aure. Hussaina sai cewa tayi dama can kwadayi ne ya kawosu da suka ga anfi karfinsu sai suka ja baya. Maganar ta yiwa Mami ciwo amma bahaushe yace wai gani ya kori ji. Idan kuwa hakane to zata basu mamaki su duka wallahi. Bazata ce musu komai game da tsatson da Radhiya ta fito ba sai dai ido ya gani anayi.
Duk wannan maganganun anyisu ne ranar Kamun Ghazalatu a Katsina kuma Mama taji saboda cikinta ya fara nauyi tafi son zama wuri daya shiyasa tana dakin suke yi. Da daddare suna dakin Mami a gidansu na Katsina daga ita sai Ummi ta tayar da maganar.
"Mairama dan taso muyi magana don Allah"
"Allah Yasa lafiya uwar 'yan hudu"