Sashe 16
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A motocin yaki uku suka fito banda babbar range rover da suka ciko ta su Major Mustapha. A lissafe sun kai mutum ashirin da takwas amma su biyun suka rage wanda kusan da taimakon Zayyan ne Hadir bai mutu ba. Duk inda ka juya gawarwaki ne kwance cikin ruwa da jini. Kallo daya zaka yiwa wurin zuciya ta tsinke kaji inama dai mafarki ne. Duk mai imani bazai so koda makiyinsa ya tsinci kansa a wurin ba. Suna cikin wannan jeji dumu-dumu a tsakanin abokan gaba. Hankulansu a tashe kunnuwansu basa jin komai sun dode saboda karar bomb ya yi musu karfi.
Zayyan ne ya hango Major Mustapha wanda a bisa la'akari da matsayi shine shugabansu a wannan fitar. Mutumin da yake tsananin mutuntawa kwance yana daga hannu. Baya yayi da sauri Hadir yayi masa kallon mamaki don bai iya ganin komai shi saboda karfin ruwan "kada kace min komawa zakayi? Kazo mu bar wurin nan don Allah"
Kallon Hadir yayi ya sake kallon Major din ya koma gareshi a guje. Dago shi yayi da zafin nama sautin harsashi yasa shi komawa ya kifa a kansa suka fadi tare. Wata siririyar kara Major Mustapha ya saki mai cike da tsananin azaba wadda ta saka shi kai duba gareshi. Wani mummunan firgici ne ya saukar masa ganin kafar Major din ta dama a gutsire bomb ya tarwatsata. Zuciyarsa ce tayi nauyi ya soma kokarin daga shi domin su gudu.
Wata damka yaji ya kai masa ruwa yana wanke musu fuskoki "Lieutenant get out of here"
Bai saurare shi ba ya ciccibe shi duk da cewa ya fishi girma sosai ya saba shi a baya. Ture shi yaji yana yi yana dan dake muryarsa "this is my final command to you Tureta. Go!"
Sojoji sun horo da tsananin biyayya ga na gaba amma wannan karon bazai bi ba. Gudu ya soma yi dashi suka nufi inda Hadir yake tsaye hannunsa na zubar jini sakamakon harbinsa da akayi suka soma yankar daji.
Cak ya tsaya ya dena tafiya har Hadir yana cewa "muje mana"
Gabansa ke lugude ya kalli kafarsa ya dago a razane "Karbe shi ku bar wurin nan"
Major ya dan leko da kansa ta saman kafadar Zayyan "Lieutenant?"
Wata ajiyar zuciya ya sauke kafin Hadir ya karbi goyon duk da shima yana da raunuka. Matsawa yace suyi nesa dashi sannan ya dago idanunsa da suka jike da hawaye sosai. Kamar mai rada yake musu bayani.
"Bomb ne"
Su biyun duka suka kalle shi a gigice. Bai nuna damuwa ba ya cigaba da magana hawayensa suna tona asirin firgicinsa. Motsi kadan zaiyi bomb din wanda aka binne cikin kasa ya tarwatsa shi. Daya bayan daya yake kallonsu
"My friend..." yace da Hadir
"....Major am afraid this is the end"
Abinda Major ya dade baiyi ba ya soma shima sai kuka duka su ukun babu mai rarrashin dan uwansa.
Kafarsa ce ta danyi rawa cikin karaji yace su bar wurin. Ba yadda suka iya dole suka bar wurin a guje zukatansu suna kuka idanu na hawaye. Basuyi nisa sosai ba suka jiyo muryarsa mai dadin sauraro idan yana yi musu limanci.
"Mairama, Alheran waye zai dubi iyalina?"
Kuka ya fashe dashi sosai a hankali ya soma karanto kalmar shahada yana ji a ransa wannan ma dama ce da Allah Ya bashi.
Sunyi gudun rabin kilometer suka ji wata gigitacciyar kara wadda tasa su biyun faduwa su ka gangara kasan wani katon rami. Kafin su kai kasansa daga Major Mustapha har Hadir tunaninsu yana ga Zayyan Muhammad Tureta. Zayyan sarkin barkwanci, mutum mai tsananin so da kaunar iyalinsa da basu da wani wanda zasu jingina dashi suji dadi idan ba shi ba ya mutu a bakin aiki bayan yayi matukar kokari wurin tseratar da rayukansu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Dattijuwa ce goye da yaro tana gurfane a gaban gadon Salame wadda take hakimce tana bata umarnin ayyukan da zata yi a cikin gidan. Banda kudi sune masu gida rana yaushe wannan mata da a shekaru zata girmi Ta Madina ace ita ce Salame 'yar cikin cikinta take yiwa rashin kunya son rai tana kada kafafu tayi daurin Mayam Babangida.
"Kada ki sake na fito baki gama aikin nan ba Kande" ta kare cikin fada.
"Sha Allahu ma zan gama da wuri." Sai ta dan kwantar da kai "nace ko na kwantar miki da Halifa tunda ya riga yayi bacci? Aikin nawa zai fi sauri"
Wata uwar harara da Salame ta galla mata ya sanya ta tashi da sauri ta fita daga dakin. Tana fitowa ta sami wani matashi yana sallama. Kallo daya tayi masa ta gane ya hada jini da matar gidan shiyasa tace ya zauna. Ruwa ta kawo masa sannan ta sanar da Salame tayi bako.
Sai da ta gama bata lokaci sannan ta fito tana takaicin hanata hutu da akayi. Tun aurenta da Salisu bazata ce ga wata rana da take cikin farinciki sosai ba. Haka dai take rayuwa daga fada sai masifa sai kuma muguwar hassadar Mairama da tayi sake ta kama zuciyarta sosai.
Dago labulen dakinta tayi ta fito. A wulakance take kallon kanin nata "ah'a Bature kai ne dama"
Zamowa yayi daga kan kujerar ya gaisheta. Bai manta zuwansu da sallah ba inda ta karesu musu tas wai sun haye kujeru abinda ba'a saba ba. Da suka koma gida kowa yana korafi suna cewa da Adda Mairama ce bazata musu haka ba banda shi don ransa ya baci. Ya dai ci alwashin idan ba aike ba babu abinda zai sake kaishi gidanta. Gaisuwar kuwa albarkacin mai aikinta da ya gani ne kada ace basu da hadin kai. Kusan halinsu daya da Mairama shiyasa Malamijo ya aiko shi don sauran babu mai yarda yazo.
"Wani abin ne ya faru kazo ko kuwa?"
Shigowar Salisu kenan yaji yadda take yiwa kaninta magana. Shi ya rasa dalilinta na kin 'yan uwanta yanzu kaf bata son mu'amala ta hadasu. Nashi dangin ma bata raga musu amma yana daf da magance matsalar nan.
Bature ya gaishe shi ya amsa a mutumce sannan yace ta biyo shi daki. Bakin nan a gaba ta bi bayansa.
"Me yake damunki ne? Yaro ya taho tun daga Sumaila babu wata tarba me kyau sai me ya faru? Yanzu ke da 'yan uwanki babu wanda zai zo don sada zumunci wurinki sai da wani dalili?" Ya jero mata tambayoyin cikin bacin rai.
Juya idanu tayi "ai dai 'yan uwana ne ba na mutum ba"
"Ni kike yiwa magana haka ko Salame?"
Bata saurare shi ba ta fice don sallamar Bature ya koma inda ya fito. Salisu ashe yana bayanta sai ganinsa tayi ya zauna yana tambayarsa mutanen gida.
"Kawo masa abinci mana Salame" ya umarceta.
Cire baki tayi ta kwalawa Kande kira.
"Ki kyale Kande aiki na ga tana yi. Kuma shi Halifa ba'a kwantar dashi ne? Kusan a bayan matar nan yake wuni ita bata huta ba shi ba'a barshi ya sake yayi wasa ba"
"Idan ta sauke shi damuna zaiyi. Kuma dai tunda biyanta akeyi meye a ciki?"
"Babu komai kuwa tunda kudinki ne Hajiya"
Magana suke yiwa juna a hasale kowa rai a bace. Bature da bashi da sha'awar kwanar musu a gida ya katse rigimar ta hanyar fada musu abinda aka turo shi ya fada. A tare suka juyo kansa. Salisu hankali a tashe Salame kuwa numfashinta taji ya tsaya na wucin gadi.
"Wane Zayyan din?" Salisu ya tattaro karfin halin tambaya.
"Mijin Adda Mairama."
"Salame kin..." kasa karasa magana yayi ganin ta tafi luuu kamar zata fadi ta saki kara iya karfinta.
Maimakon Salisu ya tarota sai mamaki ya kama shi har ya kasa motsi. Salame ce fa da yasan bata kaunar kanwarta. Me zai sa ta shiga wannan yanayi kamar ance mata shi da kansa ne ya mutu ko mahaifinta.
Bature ma abin ya daure masa kai "Adda cewa nayi mijin Adda Mairama fa ba Malamijo ba"
Zama kawai tayi dabas akan kujera tana kuka sosai. Shikenan Zayyan ashe bata da rabon zama dashi. Salisu ya kawar da kai daga gareta.
"Bature yau zaka koma ne?"
"Yanzu ma kuwa in sha Allahu. Gobe za'a tafi gaisuwa"
Zumbur ta mike "ku biyo min, ko kuma dai ka jirani na shirya"
Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje"
Bakin gate ya raka Bature ta bashi kudin mota sannan ya koma ciki. Tana nan tana rusa kuka Kande na bata hakuri. Yana zuwa ya finciko hannunta sai da Kande ta tsorata. Dakinsa ya kaita ya jefata kan gado iya karfinsa. Fuskarsa a daure babu wasa ko kadan ya jefa mata tambayar da ta kada mata hanji.
"Tun farkon haduwarmu dama Zayyan kike so?"
Shiru tayi sai faduwar gabanta da ta tsananta.
"Ki bani amsa mana!" Ya sake yi mata tsawa sai da ta firgice.
Wasu sababbin hawayen ta soma yi yaji kamar ya rufeta da duka.
"Kin cuceni, ban dade da aurenki ba zuciyata ta bani cewa ban yiwa kaina adalci wurin zabar matar aure ba. A tunanina na auro mace mara son zumunci ne kawai da raina na kasa da ita. Ashe kin wuce haka. Salame mijin kanwarki kike so kuma har kike kishi da ita alhalin kina gidan naki mijin"
Har yanzu ta kasa magana sai kuka. Shi din ma nasa idon da hawaye saboda bai taba kawo hakan a matsayin dalilin da yasa take yiwa Mairama haka ba.
"Bazaki je Sakkwato gaisuwa ba" kallonsa tayi da sauri ya sake hade rai "ke daga yau sai abu yayi tsanani sosai zanyi miki izinin fita kina ji na. Idan kika karya min doka wallahi, wallahi sai na shayar dake mamaki"
**********
Ranar da aka sallami Mairama a ranar Mal Aminu da Jume su ka amince da a kwashe kayanta ta koma gidansu Zayyan. Idan iyayenta sun zo sai su tafi da ita gida.
"Ku wuce da ita su Mubaraka sai su zo a kwashe kayan gobe tunda zaman barikin babu amfani"
Mairama tana jin haka ta ajiye kunyarta a gefe "Kawu ina son zuwa don akwai abubuwan da nake son hadawa da kaina"
Caraf a kunnen Maikudi "ko ma meye muma din jinin Zayyanu ne. Kije ki huta ni da kaina zan jagoranci zuwa a debo kayan saboda kada wani abu ya salwanta"
Zayyan ne ya hango Major Mustapha wanda a bisa la'akari da matsayi shine shugabansu a wannan fitar. Mutumin da yake tsananin mutuntawa kwance yana daga hannu. Baya yayi da sauri Hadir yayi masa kallon mamaki don bai iya ganin komai shi saboda karfin ruwan "kada kace min komawa zakayi? Kazo mu bar wurin nan don Allah"
Kallon Hadir yayi ya sake kallon Major din ya koma gareshi a guje. Dago shi yayi da zafin nama sautin harsashi yasa shi komawa ya kifa a kansa suka fadi tare. Wata siririyar kara Major Mustapha ya saki mai cike da tsananin azaba wadda ta saka shi kai duba gareshi. Wani mummunan firgici ne ya saukar masa ganin kafar Major din ta dama a gutsire bomb ya tarwatsata. Zuciyarsa ce tayi nauyi ya soma kokarin daga shi domin su gudu.
Wata damka yaji ya kai masa ruwa yana wanke musu fuskoki "Lieutenant get out of here"
Bai saurare shi ba ya ciccibe shi duk da cewa ya fishi girma sosai ya saba shi a baya. Ture shi yaji yana yi yana dan dake muryarsa "this is my final command to you Tureta. Go!"
Sojoji sun horo da tsananin biyayya ga na gaba amma wannan karon bazai bi ba. Gudu ya soma yi dashi suka nufi inda Hadir yake tsaye hannunsa na zubar jini sakamakon harbinsa da akayi suka soma yankar daji.
Cak ya tsaya ya dena tafiya har Hadir yana cewa "muje mana"
Gabansa ke lugude ya kalli kafarsa ya dago a razane "Karbe shi ku bar wurin nan"
Major ya dan leko da kansa ta saman kafadar Zayyan "Lieutenant?"
Wata ajiyar zuciya ya sauke kafin Hadir ya karbi goyon duk da shima yana da raunuka. Matsawa yace suyi nesa dashi sannan ya dago idanunsa da suka jike da hawaye sosai. Kamar mai rada yake musu bayani.
"Bomb ne"
Su biyun duka suka kalle shi a gigice. Bai nuna damuwa ba ya cigaba da magana hawayensa suna tona asirin firgicinsa. Motsi kadan zaiyi bomb din wanda aka binne cikin kasa ya tarwatsa shi. Daya bayan daya yake kallonsu
"My friend..." yace da Hadir
"....Major am afraid this is the end"
Abinda Major ya dade baiyi ba ya soma shima sai kuka duka su ukun babu mai rarrashin dan uwansa.
Kafarsa ce ta danyi rawa cikin karaji yace su bar wurin. Ba yadda suka iya dole suka bar wurin a guje zukatansu suna kuka idanu na hawaye. Basuyi nisa sosai ba suka jiyo muryarsa mai dadin sauraro idan yana yi musu limanci.
"Mairama, Alheran waye zai dubi iyalina?"
Kuka ya fashe dashi sosai a hankali ya soma karanto kalmar shahada yana ji a ransa wannan ma dama ce da Allah Ya bashi.
Sunyi gudun rabin kilometer suka ji wata gigitacciyar kara wadda tasa su biyun faduwa su ka gangara kasan wani katon rami. Kafin su kai kasansa daga Major Mustapha har Hadir tunaninsu yana ga Zayyan Muhammad Tureta. Zayyan sarkin barkwanci, mutum mai tsananin so da kaunar iyalinsa da basu da wani wanda zasu jingina dashi suji dadi idan ba shi ba ya mutu a bakin aiki bayan yayi matukar kokari wurin tseratar da rayukansu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Dattijuwa ce goye da yaro tana gurfane a gaban gadon Salame wadda take hakimce tana bata umarnin ayyukan da zata yi a cikin gidan. Banda kudi sune masu gida rana yaushe wannan mata da a shekaru zata girmi Ta Madina ace ita ce Salame 'yar cikin cikinta take yiwa rashin kunya son rai tana kada kafafu tayi daurin Mayam Babangida.
"Kada ki sake na fito baki gama aikin nan ba Kande" ta kare cikin fada.
"Sha Allahu ma zan gama da wuri." Sai ta dan kwantar da kai "nace ko na kwantar miki da Halifa tunda ya riga yayi bacci? Aikin nawa zai fi sauri"
Wata uwar harara da Salame ta galla mata ya sanya ta tashi da sauri ta fita daga dakin. Tana fitowa ta sami wani matashi yana sallama. Kallo daya tayi masa ta gane ya hada jini da matar gidan shiyasa tace ya zauna. Ruwa ta kawo masa sannan ta sanar da Salame tayi bako.
Sai da ta gama bata lokaci sannan ta fito tana takaicin hanata hutu da akayi. Tun aurenta da Salisu bazata ce ga wata rana da take cikin farinciki sosai ba. Haka dai take rayuwa daga fada sai masifa sai kuma muguwar hassadar Mairama da tayi sake ta kama zuciyarta sosai.
Dago labulen dakinta tayi ta fito. A wulakance take kallon kanin nata "ah'a Bature kai ne dama"
Zamowa yayi daga kan kujerar ya gaisheta. Bai manta zuwansu da sallah ba inda ta karesu musu tas wai sun haye kujeru abinda ba'a saba ba. Da suka koma gida kowa yana korafi suna cewa da Adda Mairama ce bazata musu haka ba banda shi don ransa ya baci. Ya dai ci alwashin idan ba aike ba babu abinda zai sake kaishi gidanta. Gaisuwar kuwa albarkacin mai aikinta da ya gani ne kada ace basu da hadin kai. Kusan halinsu daya da Mairama shiyasa Malamijo ya aiko shi don sauran babu mai yarda yazo.
"Wani abin ne ya faru kazo ko kuwa?"
Shigowar Salisu kenan yaji yadda take yiwa kaninta magana. Shi ya rasa dalilinta na kin 'yan uwanta yanzu kaf bata son mu'amala ta hadasu. Nashi dangin ma bata raga musu amma yana daf da magance matsalar nan.
Bature ya gaishe shi ya amsa a mutumce sannan yace ta biyo shi daki. Bakin nan a gaba ta bi bayansa.
"Me yake damunki ne? Yaro ya taho tun daga Sumaila babu wata tarba me kyau sai me ya faru? Yanzu ke da 'yan uwanki babu wanda zai zo don sada zumunci wurinki sai da wani dalili?" Ya jero mata tambayoyin cikin bacin rai.
Juya idanu tayi "ai dai 'yan uwana ne ba na mutum ba"
"Ni kike yiwa magana haka ko Salame?"
Bata saurare shi ba ta fice don sallamar Bature ya koma inda ya fito. Salisu ashe yana bayanta sai ganinsa tayi ya zauna yana tambayarsa mutanen gida.
"Kawo masa abinci mana Salame" ya umarceta.
Cire baki tayi ta kwalawa Kande kira.
"Ki kyale Kande aiki na ga tana yi. Kuma shi Halifa ba'a kwantar dashi ne? Kusan a bayan matar nan yake wuni ita bata huta ba shi ba'a barshi ya sake yayi wasa ba"
"Idan ta sauke shi damuna zaiyi. Kuma dai tunda biyanta akeyi meye a ciki?"
"Babu komai kuwa tunda kudinki ne Hajiya"
Magana suke yiwa juna a hasale kowa rai a bace. Bature da bashi da sha'awar kwanar musu a gida ya katse rigimar ta hanyar fada musu abinda aka turo shi ya fada. A tare suka juyo kansa. Salisu hankali a tashe Salame kuwa numfashinta taji ya tsaya na wucin gadi.
"Wane Zayyan din?" Salisu ya tattaro karfin halin tambaya.
"Mijin Adda Mairama."
"Salame kin..." kasa karasa magana yayi ganin ta tafi luuu kamar zata fadi ta saki kara iya karfinta.
Maimakon Salisu ya tarota sai mamaki ya kama shi har ya kasa motsi. Salame ce fa da yasan bata kaunar kanwarta. Me zai sa ta shiga wannan yanayi kamar ance mata shi da kansa ne ya mutu ko mahaifinta.
Bature ma abin ya daure masa kai "Adda cewa nayi mijin Adda Mairama fa ba Malamijo ba"
Zama kawai tayi dabas akan kujera tana kuka sosai. Shikenan Zayyan ashe bata da rabon zama dashi. Salisu ya kawar da kai daga gareta.
"Bature yau zaka koma ne?"
"Yanzu ma kuwa in sha Allahu. Gobe za'a tafi gaisuwa"
Zumbur ta mike "ku biyo min, ko kuma dai ka jirani na shirya"
Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje"
Bakin gate ya raka Bature ta bashi kudin mota sannan ya koma ciki. Tana nan tana rusa kuka Kande na bata hakuri. Yana zuwa ya finciko hannunta sai da Kande ta tsorata. Dakinsa ya kaita ya jefata kan gado iya karfinsa. Fuskarsa a daure babu wasa ko kadan ya jefa mata tambayar da ta kada mata hanji.
"Tun farkon haduwarmu dama Zayyan kike so?"
Shiru tayi sai faduwar gabanta da ta tsananta.
"Ki bani amsa mana!" Ya sake yi mata tsawa sai da ta firgice.
Wasu sababbin hawayen ta soma yi yaji kamar ya rufeta da duka.
"Kin cuceni, ban dade da aurenki ba zuciyata ta bani cewa ban yiwa kaina adalci wurin zabar matar aure ba. A tunanina na auro mace mara son zumunci ne kawai da raina na kasa da ita. Ashe kin wuce haka. Salame mijin kanwarki kike so kuma har kike kishi da ita alhalin kina gidan naki mijin"
Har yanzu ta kasa magana sai kuka. Shi din ma nasa idon da hawaye saboda bai taba kawo hakan a matsayin dalilin da yasa take yiwa Mairama haka ba.
"Bazaki je Sakkwato gaisuwa ba" kallonsa tayi da sauri ya sake hade rai "ke daga yau sai abu yayi tsanani sosai zanyi miki izinin fita kina ji na. Idan kika karya min doka wallahi, wallahi sai na shayar dake mamaki"
**********
Ranar da aka sallami Mairama a ranar Mal Aminu da Jume su ka amince da a kwashe kayanta ta koma gidansu Zayyan. Idan iyayenta sun zo sai su tafi da ita gida.
"Ku wuce da ita su Mubaraka sai su zo a kwashe kayan gobe tunda zaman barikin babu amfani"
Mairama tana jin haka ta ajiye kunyarta a gefe "Kawu ina son zuwa don akwai abubuwan da nake son hadawa da kaina"
Caraf a kunnen Maikudi "ko ma meye muma din jinin Zayyanu ne. Kije ki huta ni da kaina zan jagoranci zuwa a debo kayan saboda kada wani abu ya salwanta"