Sashe 89
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kina so su Mami su zo su ganki a nan ne ace kin biyo saurayi?"
"A'a"
"To ki koma idan ya dawo falo da kaina zan kirawoki kinji" ya koma lallabata saboda yadda ya kula ta shiga wani yanayi.
"To...toh...don Allah kada ka manta"
A sanyaye ta fita ta koma ta tada sallah.
Ibrahim kuma yaje bangaren Ummi lokacin su Daddy sun taso zasu je suyi sallah sai Excellency ya wuce a bar Zayyan haka sai gobe kuma. Da ya fada musu halin da ya baro Awwab mukullin mota ne bai gani ba zai kaishi asibiti Zayyan ya dakatar dashi.
"Yarona ya bawa kanshi wahala yaki cin komai tun jiya"
"Awwab din da bashi da juriyar yunwa?" Cewar Major.
"Ku bashi abu mai zafi ya sha sai yayi kamar rabin awa sai yaci abinci. Amma banda ci da sauri ko da yawa sosai. Nima da naci na shekara ashirin da biyu gashi da kyar nake tafiya"
Murmushi Ibrahim yayi yana jin Zayyan ya burge shi. Gidan ya koma lokacin su Zahra suna can ya fada musu a hada masa tea. Ita ta hada masa lipton kawai da yaji kayan kamshi da sugar daidai aka kai masa. Wanka kawai yayi da sallah ya sha ya sake kwantawa kansa na juyawa. Bai ga ta ina zai taba iya zama soja ba. Su da suke zama a bakin tituna domin tsaro ga mutane ko su yanki daji ko wuraren tarzoma ayi ta fafatawa babu ci babu sha na tsayin awanni.
Radhiya na idar da sallah Ibrahim ya fada mata me Daada yace game da Awwab din.
Ya zauna a kan kujera yana cewa "amma fa da gani yana jin jiki...cikinsa a dame sosai abin tausayi. Gaskiya yana bukatar kulawa. Naga kin fimu damuwa ko har an daidaita ne ban sani ba"
"Allah Ya kaimu yaji sauki sai ka maimaita masa" Emzee yace daga bayansa "Adda ki dafa masa wani abincin mana tunda na gidan ya saka shi amai"
Da sauri ta bar wurin ta koma kitchen din Ummi. Sai da ta tafi Emzee yace da Ibrahim "kana da problem fa, ka ga yadda ka karasa tayar mata da hankali da abinda kake cewa"
Shi bai hango me yayi ba da gaske yace "daga fada mata gaskiya? Kai baka ga alamun yana jin jikin ba?"
"Kai baka iya sakaya zance bane"
"Kamar wani mace ayi ta luguiguita magana saboda wahalar da kai"
"Anya Ibrahim zaka iya soyayya kuwa? Irin janyo hankalin yarinya da dadadan kalamai duk zero kake" Emzee yace da mamaki don Ibrahim kai tsaye yake abu yasha a jikin Mama.
"Magana mai dadi ta wuce ina sonki kina sona mu hade kai kawai a daura aure a wuce wurin? Kakale kakalen soyayya yasa na kasa samun wadda zata burgeni fa"
"Baka hadu da shagwababbiya bane sunfi tsayawa a rai"
"Allah Ya tsareni a rinka tale baki ana karya wuya kamar mara lafiya. Malamin jinya ne ni?"
Emzee yana dariya Zayyana ta banko kofar daki ta fito ashe tana jinsu. Tsaki taja da karfi yadda duka zasu ji ta wuce a fusace. Maganar Ibrahim ta sani sarai da ita yake ba wani ba. Duk da tana shiri da su duka kuma bata da abokan hira idan suna gidan sai su amma fa tafi jituwa da Emzee. A da bata ganewa idan Ibrahim ya fadi magana akan yanayinta amma yanzu an kile anje bodin an hadu da 'yan mata. Ba wannan Zayyan bace mai komai Daddy, ita ma yanzu ta san me take yi.
"Ka ga ka taba min kanwa."
"Da nayi me? Ai banyi komai ba sai na sami wannan bakin na dalle inji wa take yiwa tsaki ni da kai"
Emzee ya mike yana daga hannuwa "my friend da kai fa take. Ba dama tayi magana ka rinka cewa ana tale baki. Mutane irinka gidansu babu wani armashi komai a rinka yi kamar yaki. Irin dan tattalin nan da rarrashi ni ban ga alamun zaka iya ba"
Ibrahim kallon tausayi yayi masa don shi soyayya bacin lokaci ya dauketa musamman da ya dukufa karatun nan baji ba gani.
"Chege Emzee anya kai a NDA dinnan soja kaje zama ko kuwa dai idan kayi graduating buzu zamu shimfida maka a kofar gida ka koma mai bada lakanin mallaka da inganta kauna"
Cakumo shi Emzee yayi ya matse a tsakanin hannu da cikinsa yana cewa Allah Ya kawo shi neman shawara ya ga yadda zai rama.
***********
Sai da Radhiya tayi kusan minti biyar tana tunani kafin ta yanke shawarar me zata dafawa Awwab me sauki da zai ji dadinsa. Fridge ta bude ta fito da mince meat ta juye a karamar non-stick pot sannan ta hada albasa, tumatir uku da attaruhu biyu kanana tayi blending tare da tafarnuwa karama. Juyesu tayi a wani pan ta saki wuta nan da nan ruwan ya kafe. Sai ta dora mince meat din shima batare da ta saka ruwa ba na jikinsa ya bushe ya soma sauya kala sai ta zuba soyayyan mai a kai. Ta yanka albasa babba ta juye a ciki tare da wancan kayan miya ta zuba gishiri da kayan kamshi ta barsu suna suyowa a hankali. Sai da ta ga sauce din nata ya fara haduwa ta kara maggi da curry sannan ta dafa couscous wanda ta sakawa butter da dan gishiri a ruwan dahuwar. Ruwa ne kadan ake sakawa ayi komai cikin sauri kada ya cabe ko yayi tuwo. Yayi kyau sosai a ido ta kwashe ta zuba a karamin flask. Sauce din shi kuma ta zuba a wani bowl ta hada masa komai da plate da cokali ta bawa Zayyana dake zaune tana kunkunin maganar Ibrahim ta kaiwa Awwab.
Fauziyya ta rinka mita saboda abincin dan kadan Radhiya tayi gashi ransu ya mugun biyawa. Da yake hankalinta yana wurin Hammanta ko a jikinta sai cewa tayi idan suna so su jira Hamma ya warke tayi musu.
"Ke wallahi lallaba dangin miji akeyi a zamanin nan" Fauziyya tace tana maka mata harara don sosai tasa rai zata ci.
"Nima dangin mijin ce sai hakuri Adda babu yadda zakiyi dani"
"Don Allah ki taimaka min mana Radhiya idan banci ba bana jin bacci zai iya daukana yau" ta koma kwantar da kai.
Zahra ta bita da kallon tuhuma "anya Fauziyya kalau kike kuwa? Jiya ma fa kinyi mana daga an soya kwai da mince meat kika cinye fiye da rabin wanda aka ajiye a dinning. To ko dan mince meat kika dauko"
"Kada kiyi min fata har yau ina tuna kalar kukan da nayi ina nakuda. A bar zancen na yafe"
Radhiya ta sami na tsokana daga baya ta tausaya mata ta kawo sauran sauce din amma babu cous cous duka ta juye masa ta bata.
Zayyana ce ta zuba masa a plate ta mika masa.
"Gashi inji Adda Radhiya"
Karba yayi tun kafin ya fara ci cikinsa yana dada rarakewa da yunwa. Yanzu kam a hankali ya rinka ci sai abincin yayi masa dadi sosai. Yana gamawa ya kira wayarta kuwa.
"Hammana ya jikin?" Yaji muryarta ta shige shi a nutse 'yan salihancin na kusa.
"Better. Nag...."
"Hey! Ka manta babu godiya ne" tayi saurin dakatar dashi.
A kasalance yace "To me zance na nuna miki naji dadi?"
"Babu komai ni dai kawai ka warke"
"Love you Schatzi"
"Me too Hammana" ta kashe wayar da sauri kamar yana gabanta. Kalmar nauyi take yi mata bata jin zata iya fada.
Daga masallaci Excellency ya wuce Chibuzor yana mota tare da wani dreba su ka yi ta masa godiya. Su Major ma suka ce to yanzu dai zasu bar Zayyan ya huta ya wuce ciki.
"Ango" yaji Baba Hadir yace da sigar tsokana a kokarinsa na magana.
"Malam ka bude baki kayi tsokanar da gaske naji. Ba kyaleka zanyi ba sai naji ina fada kana fada"
"Kaga wuce wurin matarka. Idan kaso ma magrib da isha kayi naka jam'in da ita" Major yace yana nuna masa kofa. Shi da Baba Hadir kowa ya tafi nasa gidan.
Shima sai ya tafi yana murmushi. Daga falo ya soma jin wani irin kamshi mai shiga rai da bai taba sani ko jin makamancinsa ba. Turaren wuta ne dan gaske irin wanda su Mammee suke aiko mata dashi ta saka a ko ina. Kofar da ya ga ta shiga lokacin da take kuka ya bude. Nan ya sameta akan abin sallah tana addu'a ya zauna a kasa gefenta ta kammala sannan ya tashi tsaye.
"Yanzu me zanyi?"
"Ka kwanta ko baka yi bacci ba nasan jikinka yana bukatar kwanciyar"
Da yake yamma ce sanyin da aka fara ya karu sosai shiyasa ta kashe AC sai fanka kawai. Kayan jikinsa ta kalla tasan bazai ji dadin kwanciya dasu ba. Kamar yasan me take tunani ya cire rigar ya ajiye akan kujera daya dake dakin. Da farko kunya taji sai dai tana ganin yadda ya koma bata san lokacin da wani irin kuka yazo mata ba.
"Sojana kaine haka?" Ta bi wuyansa da kirji tana shafawa. Ya masifar ramewa fiye da yadda take tsammani dazu da yake cikin riga.
Rigar yayi saurin dauka "bari na rufe kasusuwan nan kada su firgita min mata" sai ya ga ta kama rigar ta mayar ta ajiye ta rungume shi tana jin wani iri a zuciyarta. Wace irin rayuwa Zayyan yayi ne. Ta sani har abada idan ba samun kanta tayi a irin wannan yanayin ba to bata isa ta fahimci ainihin radadin da yake ji a ransa yake ta kokarin dannewa da fara'ar dole ba. Sojoji nawa ne a irin rayuwar sun rabu da iyalansu babu ranar sake haduwa. Nawa ne matan suka sake aure suka sake sabuwar rayuwa ashe mazan nasu suna da rai. Yanzu da tayi aure fa? Da Allah Ya jarabceta da son waninsa fa kuma ya dawo full of hope na ganin iyalinsa. Shikenan duk wannan farincikin sai ya koma ciki ya dawo matarsa ta zama ta wani kila ma da zuri'a a tsakani. Wayyo bayin Allah. Allah Sarki sojojin kasata.
Kuka mai tsanani ta sake fashewa dashi yana shafa mata baya ta dago kanta a hankali "yanzu da nayi aure fa Zayyan? Da shikenan ni da kai..."
"A'a"
"To ki koma idan ya dawo falo da kaina zan kirawoki kinji" ya koma lallabata saboda yadda ya kula ta shiga wani yanayi.
"To...toh...don Allah kada ka manta"
A sanyaye ta fita ta koma ta tada sallah.
Ibrahim kuma yaje bangaren Ummi lokacin su Daddy sun taso zasu je suyi sallah sai Excellency ya wuce a bar Zayyan haka sai gobe kuma. Da ya fada musu halin da ya baro Awwab mukullin mota ne bai gani ba zai kaishi asibiti Zayyan ya dakatar dashi.
"Yarona ya bawa kanshi wahala yaki cin komai tun jiya"
"Awwab din da bashi da juriyar yunwa?" Cewar Major.
"Ku bashi abu mai zafi ya sha sai yayi kamar rabin awa sai yaci abinci. Amma banda ci da sauri ko da yawa sosai. Nima da naci na shekara ashirin da biyu gashi da kyar nake tafiya"
Murmushi Ibrahim yayi yana jin Zayyan ya burge shi. Gidan ya koma lokacin su Zahra suna can ya fada musu a hada masa tea. Ita ta hada masa lipton kawai da yaji kayan kamshi da sugar daidai aka kai masa. Wanka kawai yayi da sallah ya sha ya sake kwantawa kansa na juyawa. Bai ga ta ina zai taba iya zama soja ba. Su da suke zama a bakin tituna domin tsaro ga mutane ko su yanki daji ko wuraren tarzoma ayi ta fafatawa babu ci babu sha na tsayin awanni.
Radhiya na idar da sallah Ibrahim ya fada mata me Daada yace game da Awwab din.
Ya zauna a kan kujera yana cewa "amma fa da gani yana jin jiki...cikinsa a dame sosai abin tausayi. Gaskiya yana bukatar kulawa. Naga kin fimu damuwa ko har an daidaita ne ban sani ba"
"Allah Ya kaimu yaji sauki sai ka maimaita masa" Emzee yace daga bayansa "Adda ki dafa masa wani abincin mana tunda na gidan ya saka shi amai"
Da sauri ta bar wurin ta koma kitchen din Ummi. Sai da ta tafi Emzee yace da Ibrahim "kana da problem fa, ka ga yadda ka karasa tayar mata da hankali da abinda kake cewa"
Shi bai hango me yayi ba da gaske yace "daga fada mata gaskiya? Kai baka ga alamun yana jin jikin ba?"
"Kai baka iya sakaya zance bane"
"Kamar wani mace ayi ta luguiguita magana saboda wahalar da kai"
"Anya Ibrahim zaka iya soyayya kuwa? Irin janyo hankalin yarinya da dadadan kalamai duk zero kake" Emzee yace da mamaki don Ibrahim kai tsaye yake abu yasha a jikin Mama.
"Magana mai dadi ta wuce ina sonki kina sona mu hade kai kawai a daura aure a wuce wurin? Kakale kakalen soyayya yasa na kasa samun wadda zata burgeni fa"
"Baka hadu da shagwababbiya bane sunfi tsayawa a rai"
"Allah Ya tsareni a rinka tale baki ana karya wuya kamar mara lafiya. Malamin jinya ne ni?"
Emzee yana dariya Zayyana ta banko kofar daki ta fito ashe tana jinsu. Tsaki taja da karfi yadda duka zasu ji ta wuce a fusace. Maganar Ibrahim ta sani sarai da ita yake ba wani ba. Duk da tana shiri da su duka kuma bata da abokan hira idan suna gidan sai su amma fa tafi jituwa da Emzee. A da bata ganewa idan Ibrahim ya fadi magana akan yanayinta amma yanzu an kile anje bodin an hadu da 'yan mata. Ba wannan Zayyan bace mai komai Daddy, ita ma yanzu ta san me take yi.
"Ka ga ka taba min kanwa."
"Da nayi me? Ai banyi komai ba sai na sami wannan bakin na dalle inji wa take yiwa tsaki ni da kai"
Emzee ya mike yana daga hannuwa "my friend da kai fa take. Ba dama tayi magana ka rinka cewa ana tale baki. Mutane irinka gidansu babu wani armashi komai a rinka yi kamar yaki. Irin dan tattalin nan da rarrashi ni ban ga alamun zaka iya ba"
Ibrahim kallon tausayi yayi masa don shi soyayya bacin lokaci ya dauketa musamman da ya dukufa karatun nan baji ba gani.
"Chege Emzee anya kai a NDA dinnan soja kaje zama ko kuwa dai idan kayi graduating buzu zamu shimfida maka a kofar gida ka koma mai bada lakanin mallaka da inganta kauna"
Cakumo shi Emzee yayi ya matse a tsakanin hannu da cikinsa yana cewa Allah Ya kawo shi neman shawara ya ga yadda zai rama.
***********
Sai da Radhiya tayi kusan minti biyar tana tunani kafin ta yanke shawarar me zata dafawa Awwab me sauki da zai ji dadinsa. Fridge ta bude ta fito da mince meat ta juye a karamar non-stick pot sannan ta hada albasa, tumatir uku da attaruhu biyu kanana tayi blending tare da tafarnuwa karama. Juyesu tayi a wani pan ta saki wuta nan da nan ruwan ya kafe. Sai ta dora mince meat din shima batare da ta saka ruwa ba na jikinsa ya bushe ya soma sauya kala sai ta zuba soyayyan mai a kai. Ta yanka albasa babba ta juye a ciki tare da wancan kayan miya ta zuba gishiri da kayan kamshi ta barsu suna suyowa a hankali. Sai da ta ga sauce din nata ya fara haduwa ta kara maggi da curry sannan ta dafa couscous wanda ta sakawa butter da dan gishiri a ruwan dahuwar. Ruwa ne kadan ake sakawa ayi komai cikin sauri kada ya cabe ko yayi tuwo. Yayi kyau sosai a ido ta kwashe ta zuba a karamin flask. Sauce din shi kuma ta zuba a wani bowl ta hada masa komai da plate da cokali ta bawa Zayyana dake zaune tana kunkunin maganar Ibrahim ta kaiwa Awwab.
Fauziyya ta rinka mita saboda abincin dan kadan Radhiya tayi gashi ransu ya mugun biyawa. Da yake hankalinta yana wurin Hammanta ko a jikinta sai cewa tayi idan suna so su jira Hamma ya warke tayi musu.
"Ke wallahi lallaba dangin miji akeyi a zamanin nan" Fauziyya tace tana maka mata harara don sosai tasa rai zata ci.
"Nima dangin mijin ce sai hakuri Adda babu yadda zakiyi dani"
"Don Allah ki taimaka min mana Radhiya idan banci ba bana jin bacci zai iya daukana yau" ta koma kwantar da kai.
Zahra ta bita da kallon tuhuma "anya Fauziyya kalau kike kuwa? Jiya ma fa kinyi mana daga an soya kwai da mince meat kika cinye fiye da rabin wanda aka ajiye a dinning. To ko dan mince meat kika dauko"
"Kada kiyi min fata har yau ina tuna kalar kukan da nayi ina nakuda. A bar zancen na yafe"
Radhiya ta sami na tsokana daga baya ta tausaya mata ta kawo sauran sauce din amma babu cous cous duka ta juye masa ta bata.
Zayyana ce ta zuba masa a plate ta mika masa.
"Gashi inji Adda Radhiya"
Karba yayi tun kafin ya fara ci cikinsa yana dada rarakewa da yunwa. Yanzu kam a hankali ya rinka ci sai abincin yayi masa dadi sosai. Yana gamawa ya kira wayarta kuwa.
"Hammana ya jikin?" Yaji muryarta ta shige shi a nutse 'yan salihancin na kusa.
"Better. Nag...."
"Hey! Ka manta babu godiya ne" tayi saurin dakatar dashi.
A kasalance yace "To me zance na nuna miki naji dadi?"
"Babu komai ni dai kawai ka warke"
"Love you Schatzi"
"Me too Hammana" ta kashe wayar da sauri kamar yana gabanta. Kalmar nauyi take yi mata bata jin zata iya fada.
Daga masallaci Excellency ya wuce Chibuzor yana mota tare da wani dreba su ka yi ta masa godiya. Su Major ma suka ce to yanzu dai zasu bar Zayyan ya huta ya wuce ciki.
"Ango" yaji Baba Hadir yace da sigar tsokana a kokarinsa na magana.
"Malam ka bude baki kayi tsokanar da gaske naji. Ba kyaleka zanyi ba sai naji ina fada kana fada"
"Kaga wuce wurin matarka. Idan kaso ma magrib da isha kayi naka jam'in da ita" Major yace yana nuna masa kofa. Shi da Baba Hadir kowa ya tafi nasa gidan.
Shima sai ya tafi yana murmushi. Daga falo ya soma jin wani irin kamshi mai shiga rai da bai taba sani ko jin makamancinsa ba. Turaren wuta ne dan gaske irin wanda su Mammee suke aiko mata dashi ta saka a ko ina. Kofar da ya ga ta shiga lokacin da take kuka ya bude. Nan ya sameta akan abin sallah tana addu'a ya zauna a kasa gefenta ta kammala sannan ya tashi tsaye.
"Yanzu me zanyi?"
"Ka kwanta ko baka yi bacci ba nasan jikinka yana bukatar kwanciyar"
Da yake yamma ce sanyin da aka fara ya karu sosai shiyasa ta kashe AC sai fanka kawai. Kayan jikinsa ta kalla tasan bazai ji dadin kwanciya dasu ba. Kamar yasan me take tunani ya cire rigar ya ajiye akan kujera daya dake dakin. Da farko kunya taji sai dai tana ganin yadda ya koma bata san lokacin da wani irin kuka yazo mata ba.
"Sojana kaine haka?" Ta bi wuyansa da kirji tana shafawa. Ya masifar ramewa fiye da yadda take tsammani dazu da yake cikin riga.
Rigar yayi saurin dauka "bari na rufe kasusuwan nan kada su firgita min mata" sai ya ga ta kama rigar ta mayar ta ajiye ta rungume shi tana jin wani iri a zuciyarta. Wace irin rayuwa Zayyan yayi ne. Ta sani har abada idan ba samun kanta tayi a irin wannan yanayin ba to bata isa ta fahimci ainihin radadin da yake ji a ransa yake ta kokarin dannewa da fara'ar dole ba. Sojoji nawa ne a irin rayuwar sun rabu da iyalansu babu ranar sake haduwa. Nawa ne matan suka sake aure suka sake sabuwar rayuwa ashe mazan nasu suna da rai. Yanzu da tayi aure fa? Da Allah Ya jarabceta da son waninsa fa kuma ya dawo full of hope na ganin iyalinsa. Shikenan duk wannan farincikin sai ya koma ciki ya dawo matarsa ta zama ta wani kila ma da zuri'a a tsakani. Wayyo bayin Allah. Allah Sarki sojojin kasata.
Kuka mai tsanani ta sake fashewa dashi yana shafa mata baya ta dago kanta a hankali "yanzu da nayi aure fa Zayyan? Da shikenan ni da kai..."