← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 157

Sashe 10

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru Zayyan yayi sai ya koma ciki da sauri wurin Mairama a daki.

“Mairam bamu tsayar da shawarar suna ba ga Major can yana jira”

“Sunanta Alheran” tace tana gyara daurin zaninta.

“Nace sunan Innarmu ta Sumaila zamu fara sakawa”

“Don Allah Sojana sunanta Alheran, idan na sake haihuwa sai a saka sunan Innar”

Muhawara suke yi sosai ya gaji ya karbi nata “baki da wani suna da kike son a saka mata? Suna biyu nake son a saka”

Sarai ta fahimce shi, a dole yana son bata dama ita ma ta sanyawa yarinyar suna. Sai dai duk yadda take son saka sunan innarta tana ganin shi yafi dacewa da ya fara sakawa. Bata yi dogon tunani ba tace “Radhiya”.

Murmushi kawai yayi ya fita ya sanar da Major sunan ‘yarsa Alheran Radhiya Zayyan Muhammad Tureta. Hadir yace “mutumina wannan sunaye haka”

“ ‘Yar soja ce, ya kamata a komai ta fita daban” ya bashi amsa yana magana a hankali kada a ji.

Major Mustapha ya gama yi mata huduba sannan yace ya maidata ciki suyi shirin tafiya bakwai ta kusa.

Kwanaki hudu da haihuwa duk wanda ya kamata ya sami labarin haihuwa daga danginsu ya sani. Tasha Zayyan yaje ya bada sakon wasika zuwa ga Kawunsa Ghoumar domin a sanar da sauran dangi abinda aka samu. Sai wasikar ta isa akan gaba suna shirin zuwa saboda aurensa da yazo da gaggawa basu sami damar halarta ba.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: H
**********

“Kasan Allah Malamijo idan naje Sakkwato haka zikau Allah shi tsinan”

Fuskarsa a murtuke kamar zai kai mata duka ya tashi daga kwanciyar da yayi “ wai ni dake waye ya haifi yarinyar nan ne eyyee?”

Yadikko ta galla masa harara “kaine ubanta wanda na sani da ana sakewa wallahi bana jin ko tsinken ashanar gidan nan zai so a alakanta shi da kai. Me kake yiwa yaran bayan haihuwarsu? Nan haka muka kaita gidan miji abin kunya babu wani kayan arziki wai kuma ‘yarka ce, kai da garin nan kowa ya shaida arziki gareka”

“Sa ido, sa ido…kowa zaiyi ya bari tunda ba da uban mutum muke kiwon ba”

“Ba sai ka zageni ba, gaskiya ce dai dole na fada maka. Mairama baka fitar da ita kunya da biki ba dole kayi bajinta ita ta fara kawo maka jika a gidan nan. Ka kuma hada da gara tunda ba’ayi musu komai ba da bikin. Salame ba don mahaifiyarta tana kusa ba itama da haka za ta tare ba garar”

Malamijo ya mike yana kada hannuwa yana kumfar baka saboda an bukaci kudi “garo ba gara ba, idan sai na bada kudi kunyi mata gara zaku je don Allah kuyi zamanku na yafe. Yo dangin uwarta ma suka bace bat a doron kasa basa waiwayarta tunda ta rasu balle ku”

“Laifin waye to idan bana ka ba? Kowace mace ka gani kana so saboda zalama. Kuma ba dole su bace ba. Kayi auren biyan bashi tana haihuwa kace ka saketa kuma sai sun biya rabin kudin. Tsoro yasa sun gudu bakinciki kuma ya kashe yarinya karama ta bar marainiya”

Yadikko kin hakura tayi sai da kyar da sudin goshi Malamijo ya bata dubu uku da kuma tinkiya guda daya “gashi nan a tafi a kaiwa ‘yar kunama kafin na fara ganinki cikin bacci na. Ke dai da mayya ce da tuni na dade a tukunya”

Warce kudin tayi a hannunsa “fadi ka kara, aradu da ina maita da tuni an dade da raba gadon ka”

Hanjin cikin Malamijo ne ya kada da gaske furucinta ya bashi tsoro. Ko dai mayyar ce ne? shiyasa kullum baya gaba sai dai baya kamar kudin guzuri.

**********

Kwance take akan doguwar kujera a falonta lokaci lokaci ta dago kai ta tsartar da miyau a duk inda ta ga dama tana faman yatsina fuska. Salisu ne ya shigo da langa cike da gurasa da tsire irin wanda take so.

“Salame tashi kici abincin”
Kallonsa tayi ta watsar tana kokarin zubar da wani yawun ya taho da sauri ya mika mata kurtun da ya ciko da kasa “zuba a nan kinji don Allah Salame na” yace da rarrashi.

Kamar bazata zuba ba sai kuma ta tofa ya mayar ya ajiye jiki na rawa ya miko mata langar ta amshe ta soma ci don yunwa take ji dama. Ta dauko yanka na biyu ya saki fuska yana dariya “yau da albishir na dawo, me zaki bani tukwici?”

“Rike kayanka indai sai na bada wani abu zaka fada”

Baiyi fushi ba don ya saba da halinta. Bata boye masa kiyayya har yanzu da take dauke da ciki na wata biyu. Tsiyarta take tsulawa a gidan tana cin karenta babu babbaka kawai don tasan Salisu yana masifar son ta.

“Mairama ta sauka yau kwana hudu an sami mace”

Naman da take shirin hadiya ne ya makale mata a makoshi ta soma tari. Ruwa ya bata ko kalla bata yi ba bare ta karba.

“Me kace?”

“Mairama….”

“Dakata malam, wannan har wani labarin fada ne?”

Mamaki ya kama shi “ke, Mairama kanwarki nake nufi”

Zuciyarta ce take tafasa da bakin kishi. Yanzu Mairama har ciki Zayyan yayi mata ta haihu. Saboda shi tafi wata uku Salisu bai sami kanta ba sai da ya hada da fin karfi. Rigima sosai suka kwasa kamar auren bariki tana ta yi masa Allah Ya isa. Ganin babu sarki sai Allah daga baya ta hakura ba don tana son sa din ba sai don kawai ba ta hango mafita daga kaddararren aurensa ba. Da ciki ya bullo kamar ta zare don bata kaunar komai tsakaninsu lokacin da za ta kasha auren ta nemi hanyar shiga gidan Zayyan. Indai soyayya na saka hauka, kan Salame ya dade da kwancewa akan mijin kanwarta. Kuka ne ya kwace mata mai cin rai da zuciya. Mairama ta rigata samun abinda take muradi. Salisu ya tsaya kallon ikon Allah yadda take kuka haikan.

“Yanzu meye abin kuka bayan kema kina da cikin nan” a tunaninsa ko don ta riga ta haihuwa ne.

“Allah Ya sauwake nayi kuka don ta rigani haihuwa” tace cike da tsiwa.

Tsareta yayi da idanu “to kukan me kike yi?”

Gabanta ne ya fadi ta soma inda-inda “banda abin Mairama da kwarewa a rashin kunya daga auren sai ta bashi kanta. Wannan ai zubar da mutumci ne. A lissafina sai nan da kwana hudu ma zamu cika wata tara da aure amma gashi ita ta haihu. Anya ma kuwa cikin nan….”

“Ke Salame! Shiga taitayinki. Kanwar ta ki kike neman jifa da kazafi saboda wani shirmenku na banza da hofi. Na dade da kula ko sunanta na ambata ko agidan ku aka ambaceta sai fuskarki ta sauya. Idan ma wani abin ne ya hadaku ki shirya jibi zamu wuce Sakkwaton sai ku sasanta”

Kallon wulakanci ta jefa masa duk da taji tsoron tsawar da yayi mata “ba zani ba idan ka matsu da ganinsu kaje kai kadai”

Ransa ne ya soma baci shima “na fasa a gobe ma zamu tafi, haba yarinya mai nutsuwa da kunya baki da aiki sai na kusheta da jifanta da bakaken kalamai”

“Da kasan tana da halayen kirki me ya hana ka nemi aurenta ka barni na auri wanda nake….”

Tasss taji saukar mari a kumatunta sai da ta ga haske, rai a matukar bace Salisu ya nunata da yatsa “bar ganin ina lallabaki wallahi sai nayi miki shegen duka a gidan nan. Ke wace irin mutum ce ne? Kina ta abubuwa ina kawar da kai to amma tura ta kai bango tunda har jininki baki raga musu ba. Ki shirya gobe zamu tafi sannan ki tashi ki hada ruwan omo da dettol ki bi duka gidan nan ki goge min. Su bayan kofofi da kujeru duka ki tsaftace min gida ko ina warin yawu ya isheni. Idan na sake kamaki kina tofa yawu nan ba a wancan abin ba wallahi jikinki ne zai gaya miki. Tashi ki bani wuri ni”

Ba karamin tsorata tayi ba ta kai mai hakuri bango. Tsoro ne da ita tun da can, soyayyar Zayyan da ta bari a zuciyarta da kyashin kanwarta su ne suka maidata haka. Jiki na rawa ta tashi yace ta dawo sai ta gama cin abincinta tukunna.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: I
*KANA NAKA…*

Shirye shiryen tarbar bakin da zasu zo suna ya kankama. Zayyan ya dage a gidan mahaifinsa za’ayi taron duk da cewa kawunansa da Mal Aminu sun ce gara ya yi a nasu saboda gudun bacin rai da ga Jume ko ‘ya’yanta. Ya riga ya gama tsara yadda zai bi da su domin gujewa hakan. Gidan yaje har daki ya same ta ta hakimce tana taunar goro.

“Hutawa akeyi ne Jume? Kawarki tana gaisheki”

Tabe baki tayi tana kallonsa ya zauna a kan yagaggiyar ledar dakin “kawarsu dai wadanda aka haifawa. Ni a su wa kuma?”

Basarwa yayi ya tankwashe kafafu “dama alfarma nazo nema, ina son ayi taron sunan a gidan nan ne”

“Dama jiranka nake naga iya gudun ruwanka tun da aka fara shigowa da bokatan fenti dazu. Ita matar taka basu da dangi ne da bazata koma gidansu ba? Naga haihuwar fari ce, ya dace ace tana gaban iyayenta. Tsabagen rashin ta ido ka barta a gidanka kuna kwana daki guda.”

“Cikin masu zuwa sunan akwai matar babanta da zata zauna har ayi arba’in tare da ita. Ni zan koma wani gidan a cikin barikin kafin su gama”

Maikudi ne ya shigo fakam fakam ya sami guri ya tsaya ayi zancen dashi. Zayyan ya sake fada mata yana son sauke baki da ga Nijar da kuma mutanen Sumaila a gidan nasu tunda babba ne.

“Ince ko ka ga nayi kama da baiwar gidanku da zan zauna tarbar baki. Kaga Zayyanu tun wuri ka san me kake ciki da bakinka”

Murmushi ta ga yayi maimakon ya tashi ma sai ya gyara zama “to babu matsala zan yiwa su Kawu magana. Sai abu na biyu nace idan an kawo kudin rakuman wace sana’a Maikudi zai fara?”

A tare su ka taso masa kamar zasu zaune sh. Maikudi ya zauna a gefensa yana fara’a kamar gonar auduga, hakansa zai cimma ruwa. Jume ma sai ta saki fuska kamar ba ita ba.
Chapter 10 · 0% Book details