← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 157

Sashe 43

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Radhiya ta saki murmushi "kice kamar dai mu sojoji ashe nasa aikin shima baya samun isasshen hutu". Suna mata dariya za ta fara abin nata ta mayar da hankali ga abinda take yi. Madara da milo ta zuba a cup din nata ta mika hannu za ta dauki sugar Awwab ya bude kofar dakin ya fito. Wani hadadden kamshi ke tasowa tun kafin ya iso tsakiyar falon. Yayi kyau cikin wani lallausan yadi ruwan madara. Rabonsa da manyan kaya ya kwana biyu sai jiya da Daddy ya bashi su guda biyu dinkakku da zai taho. Su Zainab ya fara gaisarwa sannan ya amsa gaisuwar kannensa da Radhiya da jikinta yayi sanyi saboda kada a sake irin ta jiya.

Tana tsaye ta kasa karasa abinda take yi balle ta ja kujera ta zauna. Jiya ke mata yawo a ka yadda ya bata abinci a baki kamar wata baby. Runtse idanu tayi tana son kawar da tunanin daga zuciyarta taji ya janye kofin daga hannunta.

"Kawo na karasa hadawa naga ba kya sauri"

Sakar masa tayi da sauri ya ture robar sugar din ya kara mata madara da milo ya fara zuba ruwan zafi.

"Hamma ya isa haka" tace da ta ga ya wuce rabi.

Bai saurareta ba sai da ya cika kofin ya ja kujerar gefenta ya zauna. Kujerar kusa dashi ya tura mata baya da kafarsa ta zauna tana waigen baya. Babu mai kallonsu Zainab da Hadir labarai suke gani a tashar Channels. Zahra da Fauziyya suna hirar angwayensu dake korafin sun makale a Kano. Zayyana kuwa ta tafi dafa indomie.

Wani irin kallo yayi mata sau daya ya dauke kansa, tayi masa kyau sosai har yana tsoron kada kallon da yake mata ya wuce gona da iri "namu ne mu biyu"

Turo baki tayi "Habaaa Hamma don Allah yunwa nake ji"

"Okay fara sha ki bani" yace yana tura mata kofin.

"Ni a'a, ka shanye na hada wani"

Lumshe idanu yayi yana mata murmushi "wannan zamu sha, jiya dama ance abincin da na rage miki dawo dashi kikayi. Ko muyi kama-kama da shima baki bari munyi ba"

"Na shiga uku" ta furta a hankali tana cike da kunya ta tura kujerarta baya za ta tashi ya bata rai.

"Ki dena tashi idan muna magana bana so"

Zama tayi tana ta zumbura masa baki ya sha rabin tea din ya mika mata ta karba ta bishi da harara.

"Baka saka suga ba ni kuma dashi nake sha" ta mika hannu zata dauko robar ya riga ta daukewa.

"Da zaki a haka, try it."

Samun kanta tayi da bin umarninsa ta sha tea din shi kuma ya tashi ya koma daki bai taba doyar da aka soya da kwai ba. Tana nan zaune ya dawo da ledoji masu kyau a hannunsa da tambarin wani babban kamfani a kasar Germany. Su Zainab ya fara mikawa ta karba da murmushi ta bude. Turaruka ne na alfarma na mace da na namiji ita da Babansu Hadir da agogo set shima na mace da namiji.

"Harda dorawa kanka wahala Awwab?"

"Ku sa mana albarka kawai Mama"

"To Allah Ya saka da alkhairi Yasa kafi haka. Allah Ya baku masu yi muku a nan gaba"

"Amin" kowa ya amsa harda Radhiya.

Leda ta biyu ya mika mata "na Ibrahim da Emzee, suna ina ne ma?"

"Leka ta window wankin mota ake mana"

Komawa yayi dinning table din ya zauna a inda ya tashi Radhiya ta kafe shi da ido.

"Ya?" Yace yana gimtse dariya don ya kula ta fara cika tana jiran nata.

"Ina nawa?"

"Me din?"

Kai tsaye tace "Abin cikin ledar" 

"Kina harar tawa zan baki abin cikin leda? Wanda na siyo da sunanki ma zan je in kaiwa Ummi tayi sadaka dasu"

Kallon shirts da agoguna da Zainab ke fitarwa da sunan Emzee da Ibrahim yasa ta sake hade rai harda kwalla. Ita da tafi kowa cika baki akan Hamma Awwab amma ita ce ko tsinke bai bata ba. Abincin ma fushi tayi dashi ta ture. Sai yaji ta dan bashi tausayi ya gama dariyar abinda yake shirin kulla mata kawai don ya tsokaneta ya matso da kansa yana mata magana a hankali.

"Kin yarda daga yanzu ko me zamu ci zamu ragewa juna har na koma?" yayi dan murmushin rigimarsa da Mami a baya "da ko me naci sai na rage miki Mami tayi ta fada wai ba komai zaki iya ci ba. Ni kuma tana barin wurin sai na tura miki a baki ko yaya ne ki cinye"

Murmushin da tayi masa jinsa yayi har ransa saboda yadda take lumshe idanu batare da tayi la'akari da tasirin hakan gareshi ba "to ai kaine baka yi min bayani ba kawai kasa ni jin kunya jiya."

"Silly girl me akayi na jin kunyar? Kinsan me kike yi min kuwa da?"

Radhiya ta girgiza kai.

Yafito ta yayi da hannu ta sake duku kanta tana shakar daddadan kamshinsa "abin bakina kike cirewa ki saka a naki idan na hanaki"

Hannuwanta ta saka a gefe da gefen kumatunta ta bude baki da idanu duka a lokaci daya. Tana ta jiran Hamma Awwab ya dawo gashi ya dawo ya hadata da jin kunyar da bata taba sanin tana da ita ba. Abin bakinsa fa yace! Yanzu tana tashi kuma zai ce ta zauna ko yayi maganar yadda kowa sai yaji. Gara kawai tayi kamar bata ji komai ba ta bawa kanta shawara. Daurewa tayi kamar bata ji nauyin maganar ba tace

"Yanzu dai kasan bazan ci abin baki ba"

"Sure?" Yace yana mata kallon gefen ido.

"Na fa girma"

"If you say so" ya rausaya kansa sai kuma ya tashi tsaye "kinsan me? sai na sa kin karbi abin bakina kafin na koma Katsina"

"Idan naki fa?"

"Ki tambayeni duk abinda kike so. Amma nima idan nayi winning zan tambayeki"

"Ka shirya bani tsarabata kawai" tace tana dariya ta tashi tayi waje da sauri. Sai da ta rufe kofar falon ta dafe kirjinta da yake bugu kamar zai ballo. Kofar ta kalla ta jingina da bango tana girgiza kai

"Abin baki? Hmmuhmm, kai lallai ma Hamma Awwab dinnan idan ba bazan karba ba" kunya ta ji kamar me amma ta daure sosai tana bashi amsa saboda kada ya gane zancen na shigarta tana bashi wata ma'anar daban.

Emzee yana kallonta shi ya gama wanke motar Mamansu Zainab har ya fara taya Ibrahim da yake wankin bus din da zasu tafi Sumaila a ciki. Dauraye hannuwansa yayi Ibrahim ya bata baya bai hangota ba ya karasa gabanta.

"Ke da wa Adda?"

Dantsen hannunsa ta riko tana dariyar jindadi "Emzee yau na koyi basarwa"

Yasan Addarsa da shirirta "na tayaki murna, wa kika basar?"

"Hamma Awwab mana, wai kasan me yace min kuwa?"

Yatsunsa na nuni ya sanya a kunnuwansa ya toshesu "bana son ji don Allah"

Shan kunu tayi tana harararsa "me yasa?"

"Rike kayanki, hirarku ce" ya bata amsa yana komawa wurin Ibrahim. Haka kawai jikinsa ya bashi wani abin jin kunyar Awwab yayi don abinda zai korota waje ita kadai ba karami bane. Shi kuwa bai tashi jin ko ma meye ba a saka shi jin kunyar da za ta jima bata barshi ba su kuma su cigaba da harkokinsu.

**********
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Shadaya da rabi mutanen Katsina suka iso. Radhiya sai murna ta ga Umminta ta kara kyau. Mairama hadaddiyar mace ce da rayuwa ta yiwa cikas. Kwanakin da tayi a Katsina da kulawar Mami yasa jikinta ya kara kyau kamar ba ita ba. 

Zahra da Fauziyya na ganin Ghazalatu suka sa ihun murna don basu san da ita za'a zo ba. Mami tace bata san lokacin da zasu girma ba irin wannan tsalle da suke yi. Ita Ghazalatu hankalinta yana kan Radhiya dake zaune a gefen Umminta ana mata tsiyar Ummin na tureta bata ma san tana yi ba. Gaisawa suka yi aka dan taba hira Mami tace gara su zo su dau hanya saboda a ranar suke son dawowa.

"Ku tsaya kuci abinci an gama tun dazu"

Mami tace "muci abinci muji bacci kenan, ni kin sanni da na koshi sai na fara neman wurin kwanciya"

"Shiyasa nake jin alamun kinyi ukun yadda na sanki ashe" Mairama tace tana murmushi.

Yaran dariya suke yi Zainab tace lokaci ne ai, shekarunsu na soma ja zasu fara ajiye kiba ko da ta girma ce.

"Mama banda ni a kibar, mu sojoji ina muka ga lokacin yin kiba muna faman guje-guje a daji"

Sai da kowa ya dara Fauziyya ta tabo Ghazalatu "kinga kanwar Hamma ko, Radhiya ake ce mata. Yini daya kika yi da ita sai cikinki ya kusa ciwo don dariya"

"Na ganta". Gabadaya ranta babu dadi tun da ta ga wacece Alheran din da Awwab yake ta rawar kafa a kai. Tayi zaton wata 'yar yarinya zata gani da bata fi Zayyana ko kasa da haka ba. Dama jiya saboda wannan budurwar mai idanu a tsatstsaye ya taho Kano ya barta.

Shigowar Awwab da Abdallah wanda ya kawo su Mami dan Hussainarta daga waje kenan daidai lokacin da Mamin take ce mata.

"Idan ke soja ce bakiyi kibar ba mijinki da ba soja ba zaiyi ne"

Tsuke baki tayi tana kada yatsa "No, no, no, no , no Mami. Ni likita zan aura fa. Kinsan shima aikinsu babu zama bazaiyi kibar ba"

"Mara kunya" Mairama tace tana daka mata duka a baya. Su Ibrahim an sami abinda ake so suna ta dariya. Zainab ta maimaita musu abinda Radhiyan tace dazu wai ta raina kowa idan ba soja da likita ba.

"Mama mu dasu aikin ceton rai muke yi shiyasa kowa bai kai mu ba"

Mairama sarkin kunya sai ta soma tsoron kada Radhiyan ta fadi wani abin da yafi wannan. Ta tuna ranar da tace mata tana abu kamar ba bafillatana ba. Ita kuwa ta ce dama ba ita bace, su Sakkwatawa ne.

"Ku barni da ita kwanannan zanyi mata miji a aurar da ita mu huta" inji Zainab.

Tun shigowarsu Awwab yake kallon yadda take ta zuba surutu. Dauke kansa yayi ya kalli Ghazalatu ya sakar mata murmushi ta maida masa.

Ibrahim ne yace "Mama ki samo mata malamin makaranta kawai"
Chapter 43 · 0% Book details