Sashe 53
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana fitowa har ta kusa kure layin nasu ya bi bayanta da sauri. Sai da ta dan tsorata da taji muryarsa da ya kira sunanta. Ta juyo a nutse yayi mata nuni da gidan da hannunsa.
"Ki jirani a wurin zaman nan ina zuwa"
Wani salihanci ne ya saukar mata a yau din, babu musu ta koma ta zauna akan tudun nan tana jiransa. Hamma Awwab ne ya tambayeta ko zata aure shi. Tunanin maganar kawai sai da ya sanya zuciyarta kadawa tsigar jikinta ta tashi. Kankame jikinta tayi tana jin yadda farinciki ke mamayarta.
Magana take yiwa kanta ita kadai tana murmushi "lallai ta kare min, dreba kuma nake so"
Shagon babu nisa bata dade ba Awwab ya shigo da katan din ruwan roba mai manyan robobi. Za ta tashi yace ta bari ya kaiwa Ummi ya dawo.
Gabanta ke dukan uku-uku wannan karon da ya kuma dawowa. Zaman me zasuyi take tambayar zuciyarta. Zance!
Bai dauke idonsa daga kallonta ba har sai da ya zo gabanta ya durkusa a tsugunne. Kallon kofofi biyun da za'a iya shigowa wurin a same su take yi ta shiga gidan da ta fita tana addu'ar kada Allah Ya kawo kowa.
"Amsar tambayata nake jira"
Rufe fuskarta tayi da hannu sai murmushi da yake manne akan kyakkyawar fuskarta.
Ba burinsa bane ta chanja daga Alheran din da ya sani don kawai matsayinta a wurinsa ya chanja.
"Na takuraki ko?"
"A'a"
Tsoro ne ya dan darsu a zuciyarsa da sauri yace "Baki amince ba ne?"
"A'a"
"To menene?"
Kofofin ya ga tana bi da kallo kafin tace "Hamma ni kunya nake ji kada wani ya shigo"
"Sai ki bani amsar da nake jira in tashi. Nima bakiji kafafuna ba sun fara sagewa" ya kare maganar yana marairaice mata.
Tsokanarsa ta fara yi kawai don ta ja nasa rai "kasan sojoji an sanmu da dauriya ya kamata kaima ka gwada jarumta ko na rabin awa ne"
Idan ta kara minti daya yana jin kila zama zaiyi kawai a wurin ya lankwashe kansa gefe "habaaa mana"
"Na amince" din da yake jira ta fada kamar mai rada ta rufe kanta tsaf baya ganin komai a fuskarta.
Tashi yayi ya zauna a gefenta a kan tudun "wahhhsh, da kin kara jan lokaci sai dai ki daukeni idan mun tashi"
"Kai" ta waro ido tana dariya. Ta ina za ta dauke shi.
"Seriously, sai ya tuna min da punishment din primary dinmu a Sokoto. Frog jump haka kawai don a wahalar da mutane mu kasa tafiya"
Da yake taji mugunta ta sami abinda take so sai dariya "yanzu harda zaman babur akeyi yafi frog jump wahala"
"Bana fatan sanin yaya yake tunda ya saka ki wannan dariyar nasan ba abin kirki bane"
Gyara zama yayi sosai ya kira sunanta domin yana son suyi magana ta nutsuwa da fahimtar juna "abinda zan fada miki ina so kiyi masa kyakkyawar fahimta kinji" ya kafa mata ido.
"To Hamma"
Nannauyan numfashi ya sauke saboda mahimmancin maganar da yadda ta rinka cin ransa har ya kasa zama dole ya biyota ayita ta kare.
"I love you Alheran Radhiya, I miss you a duk lokacin da kika bacewa ganina. Da zan iya da na dora hannunki kinji yadda kike hana zuciyata samun nutsuwa saboda tunaninki"
Tamkar ana zubawa jikinta ruwan dumi haka take jin saukar kalamansa suna kwantar da duk wani abu da yake yawo a ranta sai shi kadai da tunaninsa.
"A cikin kwanakin nan da na kara saninki na fahimci kina da kishi" gefensa ta dan kalla kamar zata yi magana sai ta fasa. Tabbas tana kishinsa, kishi ba na wasa ba kuwa "gashi ni kuma na hadawa kaina zafi ina zaman zamana. Ban san inda zan kai mata biyu ba amma Alheran bazan iya rabuwa da Ghazalatu ba don ina sonki"
Sake kallonsa tayi sai ya ga kwalla ta soma taruwa a idonta. Har cikin zuciyarsa yake jin komai na kanwar tasa. A zahiri zai iya boyewa amma a zuciyarsa yasan soyayyar gaskiyarsa tana hannun Alheran "kada kiyi kuka please. Ban zo gareki ba sai da nayi ta tunanin what will be the best for the three of us. Look at me!"
Umarnin yayi mata tsauri a yanzu da ya gama da zuciyarta amma bata iya ketarewa ba ta dago idanunta hawayen zuna zubowa batare da sauti ba. Da zai iya da ya rungumeta sai dai ko da suka tashi nesa da gida Mami na aiki sauran tarbiyarsu ta koma ga mahaifinsu baiyi musu da wasa ba. Bai bar yaransa dabi'un nasara sunyi galaba a kansu ba ta hanyar yawan kulawa, tsawatarwa, ja a jiki da kaiwa Allah kuka.
"I love you! I love you!! I love you!!!....kafin komai ki bar wannan ya zauna a zuciyarki. Kin tuna ranar da nace idan kin sha abin bakina zan tambayeki wani abu?"
Jikinta a sanyaye ta gyada kai "kiyi hakuri amma alfarma zan rokeki da wannan damar. ALHERAN DON ALLAH KI YARJE MIN NA FARA AUREN GHAZALATU."
Jin maganar tashi tayi tamkar saukar aradu a tsakar kanta. Tsiwa take son tayi masa ko tayi bore ko dai tayi wani abin domin nuna masa cewa bata yarda ba, zuciyarta ma bazata barta ba sai ta kasa sakamakon raunin da take iya karanta a idanunsa da suka soma chanja launi.
"Mummyn Ghazalatu sister din Mami ce iyayensu daya. Daddy dinsu kuma cousin din Mami ne kuma cousin din Daddy. Iyayensu maza duka ukun brothers ne. Shekararmu biyu tare da ita sai yanzu muka yanke shawarar fada a gida bayan bikin su Zahra. Kina ganin na kyauta idan nace mata na fasa saboda ke?"
Roko ne yake yi duk da bai furta yadda zata gane a magana ba amma ta gane a yanayinsa. Duk kishinta tana da hankali kuma tasan daidai. Indai zata zama mallakinsa itama wallahi zata iya hakura ya fara aurenta. Da dai ace da ita ya fara haduwa da labari ya sha bambam amma tunda ita ce tazo daga baya hakuri ya zame mata dole.
"A'a" tace a nutse don ta bashi kwarin gwiwa.
Farinciki ne ya bayyana a fuskarsa ma'abociyar yawan murmushi "Don Allah kin yarda zaki jirani ko na shekara daya ne na fara aurenta sannan na aureki?"
Runtse idanunta tayi wasu zafafan hawaye na gudu ta gyada kai don babu bakin amsawa.
Ajiyar zuciya ya saki yana hamdala. Daga Ghazalatu har Alheran yasan babu wata saliha a cikinsu. Ko yasha giyar wake bazai ajiyesu a gida daya ba ma. Rigima ce gagaruma ya hadawa kansa amma baya jin akwai yadda zaiyi ya sabule ko daya a cikinsu. Dukkansu akwai babban al'amari tsakanin iyayensu da nasa kuma babu wadda aka tura masa. Da kansa ya nemi soyayyarsu saboda haka dolensa ya tattaro duk wani karfin hali na maza ya dorawa kansa idan yana son zaman lafiya dasu.
"A yau zan koma Katsina in sha Allah babban kakanmu ya dawo jiya bamu hadu ba na taho. Ina komawa zan fadawa Daddy komai don ya fada masa"
"To" yaji tace muryarta tana rawa. Tun ba'aje ko ina ba tasan cewa tana da kishiya.
Zoben da yake karamin yatsansa na farar azurfa mai matukar kyau da harafin A an rubuta cikin kayataccen rubutu ya cire ya dora mata a tafin hannunta "a hannuna yana nufin Alheran, da sunanki na saye shi da albashina na farko. Amma yanzu sunansa Awwab. Don Allah ina rokonki kada ki bawa kowa chance din neman aurenki. I know naso kaina da yawa amma nayi haka ne don kada wata rigima ta tashi da zata shafi iyayenmu."
Son zuciya daban, zahirin rayuwa daban. Tana da kaifin tunanin taya shi hango faruwar abu mara dadi a danginsu idan ya guji 'yar uwarsa ta jini saboda ita. Wani girma ne na musamman taji ya bakunceta ta kara karfafa zuciyarta. Murmushi tayi masa bayan ta goge hawayenta duk ta dame idanunta da hijab din da kwalli.
"Kin amince?" Ya sake tambayarta yana kallon kwayar idonta da nasa jajayen idanun da damuwar tsoron rashin amincewarta ta haddasa.
"Eh"
"Zaki jirani?"
"Eh"
"Babu ke babu Kawu Zakari da sauran sojoji da likitoci fa"
Dariya suka sa a tare ta sake cewa "eh"
"Do you love me?"
Nauyin maganar taji ta dukar da kanta "eh"
"Say it" yace cikin muryar umarni.
Kafada ta noke tana dariya kasa-kasa "ni dai bazan iya ba"
"Zan kira ki fada min a waya"
"Idan Ummi taki bani fa"
"Rufe idonki ki ga wani abu"
Rufewa tayi ya fito da wayar da ya saya mata taji karamar kara ta bude ido daya a daidai lokacin da ya sake daukarta a hoto.
"Mu gani, nayi kyau?" tace a kagauce tana son ganin yadda hoton yayi.
"Kin bata min hoton da kuka. Da a haka zakiyi sojan abu kadan kuka?"
"Kaine kake sani kukan nan amma ni bana kuka"
"Na soyayya ne so ba damuwa, bazan baki hakuri ba ma" yace yana dariya.
Kallonta yayi ta sanya zoben a yatsan kusa da karamin ta dago masa hannunta tana tambayarsa ko yayi mata kyau. Ya yaba sosai ya ja mata kunne akan kada ta taba cire shi wai na alkawari ne. Wayar ya mika mata taki karba wai Ummi zata yi fada.
"Kinsan da ita na fake na taho garin nan da kunya mu koma tare. Muje na kaiwa Ummin da kaina a baki. Daga nan har na koma aiki sai kunnenki yayi ciwo da wayata"
"Idan baka kira ba ma kuka zanyi"
"Seriously? Kina sona haka"
Bata iya amsa masa da baki ba sai kai da ta daga cikin farinciki mara misaltuwa.
**********
A cikin gidan Alh Baba mahaifin Ghazalatu ya danyi karamin gini mai daki biyu, toilet biyu da kitchen saboda iyalinsa idan sun zo gari. Ana gobe zasu dawo daga Umara Gambo da sauran yaran nasu suka iso. Ghazalatu ma komawa tayi ta tayata gyare-gyare. Ana gobe Awwab zai taho wurin Radhiya cikin dare suna hira da mijinta ya sako zancen Ghazalatu.
"Ki duba ki gani sa'ar Fauziyya ce gashi suna shirin aure ita sai taron abokai babu wani tsayayye. Tafiyar nan Alhaji kusan kullum sai yayi min fadan wai mun sangartasu gashi bai ji wata magana game da aure ba"
Murmushi ya ga matar tasa tayi ya tsaya yana bin ta da kallon mamaki.
"Ki jirani a wurin zaman nan ina zuwa"
Wani salihanci ne ya saukar mata a yau din, babu musu ta koma ta zauna akan tudun nan tana jiransa. Hamma Awwab ne ya tambayeta ko zata aure shi. Tunanin maganar kawai sai da ya sanya zuciyarta kadawa tsigar jikinta ta tashi. Kankame jikinta tayi tana jin yadda farinciki ke mamayarta.
Magana take yiwa kanta ita kadai tana murmushi "lallai ta kare min, dreba kuma nake so"
Shagon babu nisa bata dade ba Awwab ya shigo da katan din ruwan roba mai manyan robobi. Za ta tashi yace ta bari ya kaiwa Ummi ya dawo.
Gabanta ke dukan uku-uku wannan karon da ya kuma dawowa. Zaman me zasuyi take tambayar zuciyarta. Zance!
Bai dauke idonsa daga kallonta ba har sai da ya zo gabanta ya durkusa a tsugunne. Kallon kofofi biyun da za'a iya shigowa wurin a same su take yi ta shiga gidan da ta fita tana addu'ar kada Allah Ya kawo kowa.
"Amsar tambayata nake jira"
Rufe fuskarta tayi da hannu sai murmushi da yake manne akan kyakkyawar fuskarta.
Ba burinsa bane ta chanja daga Alheran din da ya sani don kawai matsayinta a wurinsa ya chanja.
"Na takuraki ko?"
"A'a"
Tsoro ne ya dan darsu a zuciyarsa da sauri yace "Baki amince ba ne?"
"A'a"
"To menene?"
Kofofin ya ga tana bi da kallo kafin tace "Hamma ni kunya nake ji kada wani ya shigo"
"Sai ki bani amsar da nake jira in tashi. Nima bakiji kafafuna ba sun fara sagewa" ya kare maganar yana marairaice mata.
Tsokanarsa ta fara yi kawai don ta ja nasa rai "kasan sojoji an sanmu da dauriya ya kamata kaima ka gwada jarumta ko na rabin awa ne"
Idan ta kara minti daya yana jin kila zama zaiyi kawai a wurin ya lankwashe kansa gefe "habaaa mana"
"Na amince" din da yake jira ta fada kamar mai rada ta rufe kanta tsaf baya ganin komai a fuskarta.
Tashi yayi ya zauna a gefenta a kan tudun "wahhhsh, da kin kara jan lokaci sai dai ki daukeni idan mun tashi"
"Kai" ta waro ido tana dariya. Ta ina za ta dauke shi.
"Seriously, sai ya tuna min da punishment din primary dinmu a Sokoto. Frog jump haka kawai don a wahalar da mutane mu kasa tafiya"
Da yake taji mugunta ta sami abinda take so sai dariya "yanzu harda zaman babur akeyi yafi frog jump wahala"
"Bana fatan sanin yaya yake tunda ya saka ki wannan dariyar nasan ba abin kirki bane"
Gyara zama yayi sosai ya kira sunanta domin yana son suyi magana ta nutsuwa da fahimtar juna "abinda zan fada miki ina so kiyi masa kyakkyawar fahimta kinji" ya kafa mata ido.
"To Hamma"
Nannauyan numfashi ya sauke saboda mahimmancin maganar da yadda ta rinka cin ransa har ya kasa zama dole ya biyota ayita ta kare.
"I love you Alheran Radhiya, I miss you a duk lokacin da kika bacewa ganina. Da zan iya da na dora hannunki kinji yadda kike hana zuciyata samun nutsuwa saboda tunaninki"
Tamkar ana zubawa jikinta ruwan dumi haka take jin saukar kalamansa suna kwantar da duk wani abu da yake yawo a ranta sai shi kadai da tunaninsa.
"A cikin kwanakin nan da na kara saninki na fahimci kina da kishi" gefensa ta dan kalla kamar zata yi magana sai ta fasa. Tabbas tana kishinsa, kishi ba na wasa ba kuwa "gashi ni kuma na hadawa kaina zafi ina zaman zamana. Ban san inda zan kai mata biyu ba amma Alheran bazan iya rabuwa da Ghazalatu ba don ina sonki"
Sake kallonsa tayi sai ya ga kwalla ta soma taruwa a idonta. Har cikin zuciyarsa yake jin komai na kanwar tasa. A zahiri zai iya boyewa amma a zuciyarsa yasan soyayyar gaskiyarsa tana hannun Alheran "kada kiyi kuka please. Ban zo gareki ba sai da nayi ta tunanin what will be the best for the three of us. Look at me!"
Umarnin yayi mata tsauri a yanzu da ya gama da zuciyarta amma bata iya ketarewa ba ta dago idanunta hawayen zuna zubowa batare da sauti ba. Da zai iya da ya rungumeta sai dai ko da suka tashi nesa da gida Mami na aiki sauran tarbiyarsu ta koma ga mahaifinsu baiyi musu da wasa ba. Bai bar yaransa dabi'un nasara sunyi galaba a kansu ba ta hanyar yawan kulawa, tsawatarwa, ja a jiki da kaiwa Allah kuka.
"I love you! I love you!! I love you!!!....kafin komai ki bar wannan ya zauna a zuciyarki. Kin tuna ranar da nace idan kin sha abin bakina zan tambayeki wani abu?"
Jikinta a sanyaye ta gyada kai "kiyi hakuri amma alfarma zan rokeki da wannan damar. ALHERAN DON ALLAH KI YARJE MIN NA FARA AUREN GHAZALATU."
Jin maganar tashi tayi tamkar saukar aradu a tsakar kanta. Tsiwa take son tayi masa ko tayi bore ko dai tayi wani abin domin nuna masa cewa bata yarda ba, zuciyarta ma bazata barta ba sai ta kasa sakamakon raunin da take iya karanta a idanunsa da suka soma chanja launi.
"Mummyn Ghazalatu sister din Mami ce iyayensu daya. Daddy dinsu kuma cousin din Mami ne kuma cousin din Daddy. Iyayensu maza duka ukun brothers ne. Shekararmu biyu tare da ita sai yanzu muka yanke shawarar fada a gida bayan bikin su Zahra. Kina ganin na kyauta idan nace mata na fasa saboda ke?"
Roko ne yake yi duk da bai furta yadda zata gane a magana ba amma ta gane a yanayinsa. Duk kishinta tana da hankali kuma tasan daidai. Indai zata zama mallakinsa itama wallahi zata iya hakura ya fara aurenta. Da dai ace da ita ya fara haduwa da labari ya sha bambam amma tunda ita ce tazo daga baya hakuri ya zame mata dole.
"A'a" tace a nutse don ta bashi kwarin gwiwa.
Farinciki ne ya bayyana a fuskarsa ma'abociyar yawan murmushi "Don Allah kin yarda zaki jirani ko na shekara daya ne na fara aurenta sannan na aureki?"
Runtse idanunta tayi wasu zafafan hawaye na gudu ta gyada kai don babu bakin amsawa.
Ajiyar zuciya ya saki yana hamdala. Daga Ghazalatu har Alheran yasan babu wata saliha a cikinsu. Ko yasha giyar wake bazai ajiyesu a gida daya ba ma. Rigima ce gagaruma ya hadawa kansa amma baya jin akwai yadda zaiyi ya sabule ko daya a cikinsu. Dukkansu akwai babban al'amari tsakanin iyayensu da nasa kuma babu wadda aka tura masa. Da kansa ya nemi soyayyarsu saboda haka dolensa ya tattaro duk wani karfin hali na maza ya dorawa kansa idan yana son zaman lafiya dasu.
"A yau zan koma Katsina in sha Allah babban kakanmu ya dawo jiya bamu hadu ba na taho. Ina komawa zan fadawa Daddy komai don ya fada masa"
"To" yaji tace muryarta tana rawa. Tun ba'aje ko ina ba tasan cewa tana da kishiya.
Zoben da yake karamin yatsansa na farar azurfa mai matukar kyau da harafin A an rubuta cikin kayataccen rubutu ya cire ya dora mata a tafin hannunta "a hannuna yana nufin Alheran, da sunanki na saye shi da albashina na farko. Amma yanzu sunansa Awwab. Don Allah ina rokonki kada ki bawa kowa chance din neman aurenki. I know naso kaina da yawa amma nayi haka ne don kada wata rigima ta tashi da zata shafi iyayenmu."
Son zuciya daban, zahirin rayuwa daban. Tana da kaifin tunanin taya shi hango faruwar abu mara dadi a danginsu idan ya guji 'yar uwarsa ta jini saboda ita. Wani girma ne na musamman taji ya bakunceta ta kara karfafa zuciyarta. Murmushi tayi masa bayan ta goge hawayenta duk ta dame idanunta da hijab din da kwalli.
"Kin amince?" Ya sake tambayarta yana kallon kwayar idonta da nasa jajayen idanun da damuwar tsoron rashin amincewarta ta haddasa.
"Eh"
"Zaki jirani?"
"Eh"
"Babu ke babu Kawu Zakari da sauran sojoji da likitoci fa"
Dariya suka sa a tare ta sake cewa "eh"
"Do you love me?"
Nauyin maganar taji ta dukar da kanta "eh"
"Say it" yace cikin muryar umarni.
Kafada ta noke tana dariya kasa-kasa "ni dai bazan iya ba"
"Zan kira ki fada min a waya"
"Idan Ummi taki bani fa"
"Rufe idonki ki ga wani abu"
Rufewa tayi ya fito da wayar da ya saya mata taji karamar kara ta bude ido daya a daidai lokacin da ya sake daukarta a hoto.
"Mu gani, nayi kyau?" tace a kagauce tana son ganin yadda hoton yayi.
"Kin bata min hoton da kuka. Da a haka zakiyi sojan abu kadan kuka?"
"Kaine kake sani kukan nan amma ni bana kuka"
"Na soyayya ne so ba damuwa, bazan baki hakuri ba ma" yace yana dariya.
Kallonta yayi ta sanya zoben a yatsan kusa da karamin ta dago masa hannunta tana tambayarsa ko yayi mata kyau. Ya yaba sosai ya ja mata kunne akan kada ta taba cire shi wai na alkawari ne. Wayar ya mika mata taki karba wai Ummi zata yi fada.
"Kinsan da ita na fake na taho garin nan da kunya mu koma tare. Muje na kaiwa Ummin da kaina a baki. Daga nan har na koma aiki sai kunnenki yayi ciwo da wayata"
"Idan baka kira ba ma kuka zanyi"
"Seriously? Kina sona haka"
Bata iya amsa masa da baki ba sai kai da ta daga cikin farinciki mara misaltuwa.
**********
A cikin gidan Alh Baba mahaifin Ghazalatu ya danyi karamin gini mai daki biyu, toilet biyu da kitchen saboda iyalinsa idan sun zo gari. Ana gobe zasu dawo daga Umara Gambo da sauran yaran nasu suka iso. Ghazalatu ma komawa tayi ta tayata gyare-gyare. Ana gobe Awwab zai taho wurin Radhiya cikin dare suna hira da mijinta ya sako zancen Ghazalatu.
"Ki duba ki gani sa'ar Fauziyya ce gashi suna shirin aure ita sai taron abokai babu wani tsayayye. Tafiyar nan Alhaji kusan kullum sai yayi min fadan wai mun sangartasu gashi bai ji wata magana game da aure ba"
Murmushi ya ga matar tasa tayi ya tsaya yana bin ta da kallon mamaki.