Sashe 102
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kwantar da hankalinka Zayyanu. Ni dai na haifi Salame ina mai tabbatar maka babu wani iskancin da zata zo dashi da ban ga wanda ya fishi ba. Zan bi diddgin maganar da kaina. Kai dai ka rufa min asiri kada yayarka taji zancen nan mu duka mu shiga uku. Ka fita hakuri da nutsuwa ka bari muyi komai cikin lumana" Malamijo ya sami kansa da lallaba Emzee.
Ficewa kawai yayi daga dakin a hanya yaci karo da Halifa. Wani mummunan kallo ya maka masa Nene tana biye dashi tace da Halifan allurar soja ce ta motsa saboda Malamijo yayi masa fada. Da yake ba bakon zafi bane sai ya yarda harda tausayawa Emzee din.
Dakin da suka kwana ya shiga ya rinka naushin bango ko zai ragewa kansa fushi. Da ya bar maganar a cikinsa gara ace bai ji ba. Kai dama ace Radhiya ce taji ta gwadawa Salame me ake nufi da uwa. Wai saboda wani can Alh Indararo shine ta makanta musu uwa. Kuma karin abin haushi wai Daada dinsu take so.
"Wallahi sai dai ki mutu amma yafi karfinki"
"Kai da wa?" Yaji Ibrahim yace daga bayansa. Kasa amsawa yayi sai kwanciya da yayi yana ta juya zancen. Abin ya dame shi matuka ya dena walwala ya matsawa Ibrahim suka tafi Kano gidan kakaninsa. Halifa da Hibbah su ma zasu tafi amma kememe Emzee yaki yarda su hada tafiyar saboda baya ko son ganin Halifa. Washegarin tafiyar tasu yaje yace da Malamijo ya basu kudin mota. Dubu goma ya bashi duk da yasan kudin yayi yawa amma gara ya tafi ko hankalinsa ya kwanta. Kullum da zulumin kada Radhiya ta gane yake kwana. Ta shiga damuwa sosai akan yadda kanin nata ya koma sai matsawa Malamijo take yi akan ya tambaye shi ko ta sanar da iyayensu.
**********
Kwanan su Zayyan uku a Sakkwato sai birnin Agadez a kasar Nijar. Da kwatance suka isa unguwar inda gidan Alh Ghoumar da Alh Sidi suke makotaka da juna. Mammee suna Niamey da mijinta tunda dan siyasa ne. Kowa yayi mamakin zuwan Mairama ita kadai tace banda yaran ta tahi lokacin da ta kira kwaya domin a kwatanta musu hanya. Tante Nasara sai da ta kira Radhiya da Emzee taji muryoyinsu ta tabbatar kowa lafiya kafin isowarsu gidan.
Murnarsu kuwa bayan sun ga Zayyan bazata misaltu ba. Masu kuka na yi masu suma suna yi. Dangin Innar Zayyan sun sake nuna bajintarsu da kwarewa wurin rikon zumunci da murnar dawowarshi. Mammee tayi kuka tayi fadan me yasa basu sanar da ita ba sai da suka iso gashi kowa ya rigata ganinsa. Kwanansu biyar 'yan uwa suna faman kokarin kyautata masa da nuna masa cewa shi din dan dangi ne. Tamkar kada ya baro kasar sai dai dole ya koma saboda litinin zaiyi reporting a headquarter ana nemansa.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Radhiya bata kwanta ba sai da ta gama tsara yadda za ta yi da Hajiyayye gobe. Ba'a taba mata kaka a kwana lafiya. Yadda ta rabe mata abinci bata sami ko loma daya ba haka da daren ma dan kadan ta ce Na'e ta zuba musu ita da yaran. Bakinciki yasa Hajiyayye ta kasa komai saboda sau uku tana kokarin zuwa dakin Malamijo sai ta tarar da Ibrahim da Emzee a kofar dakin kamar suna gadinsa.
Bayan kowa yaci abincin safe ne Radhiya ta fito tsakar gida tana tambayar waye mai girki yau. Yadikko ta kama kunnenta ta rike.
"Na fada miki babu mai girki a gidan nan sai amaryar kakanki. Na'e ma da tayi tuwon dare jiya kawaici tayi miki bata ce komai ba"
Hajiyayyen rabewa tayi a jikin kofar dakinta tana jinsu tayi murmushi. Ashe dai Yadikko tasan matsayinta. Idan suka yi kuskuren biyewa wannan yarinyar za ta barsu da jidali ne idan ta tafi don duk wanda ya shiga gonarta sai ya gane kurensa.
"Tunda babu mai girkin dole ni zanyi kenan da kaina. Bari na leka Malamijo ya bada shanu uku ma sun isa da za'ayi yanka"
"Yanka kuma? Radhiya idan kika zo gidan nan bakya zama kiyi ta mana jaye jaye. Nama kuma kema kin sani ba'a kawowa gidan nan har kike kiran yanka."
Bata ankara ba sai ga Malamijo ya fito yau dai sanyi ya saka shi saka kayan kirki ya rufe kasusuwan jikinsa. Daure fuska yayi yana hararar Yadikko.
"Kinji nace bazan bada shanun bane da zaki yanke min hukunci? 'Yar Soja guda nawa kuke bukata?"
"Uku tace" inji Emzee da suka gama sanin me take da niyar yi.
"Amma shanu uku 'Yar Soja waye zai taya ku aikin naman? Yayi yawa. In baku daya dai yau kowa yaci"
Murmushin mugunta tayi da Ibrahim yayi mata alama cewa fa Hajiyayye ta leko daga dakinta tana sauraronsu. Haka take so taji ko wani nata yaji a kai mata rahoto.
"Kada ka damu naman nan ba mune zamu ci ba. Wadanda za'ayiwa yankan kuma danye suke so"
Idanu Malamijo ya zaro "Hajiyayye zaki yiwa yanka?"
Sai da ta kula kowa ita yake sauraro ta dare kan turmi ta zauna "Bakina dai da zasu zo. Jiya da na ga yadda gidan nan ya koma shine na kira Sarkin mayun Faransa...can inda nake karatu. Dayake muna mutumci da 'ya'yansa sai ya daukeni kamar 'yar cikinsa. To shine nayi masa maganarka na cewa ka auro mayya. Yayi ta mamaki tunda yasan ni ba mayyar bace. Shine fa yau da sassafe ya kirani wai ya kai maganar can ofishin majalisar dinkin duniya akan harkar mayu sun ce zasu turo wakilai azo ayi bincike ke"
Idanun Malamijo tuni suka raina fata ya hau rawar jiki "ni nace kiyi zancena da wasu ne? Haba Radhiya ashe baki da hankali ban sani ba. Mayun Najeriya basu cinyeni ba sai na Faransa"
Yadikko tana ji tasan sharrin Radhiya ne amma yadda idanun Malamijo suka kada suka yi ja sai ta kyale ko banza ta rinka tunawa tana dariya.
Cikinsu Ibrahim ne ya iya daure dariyarsa yace "Turawan mayu inajin kince basa cin mutane sai mayu 'yan uwansu ko"
"Eh mana, matsalar dai bincike zasu zo yi. Wai ashe daga last year aka haramtawa duk wanda ba maye ba auren maye saboda gudun rigingimu da suke tasowa." Ta yi kamar ta rage murya za ta yi rada bayan ta san sarai kowa yana ji "yace zasu kama duka mayun gidannan ne a tafi dasu. Hukuncin take dokar shine kisa ta hanyar babbakaraisin din mayun a baiwa oganninsu su ci da bredi"
Tsuuuu zawo ya nemi saukowa daga jikin Hajiyayye cikinta na murdawa tana matse shi da kyar saboda tsabar kaduwa. Babban yaron da tazo dashi gidan ashe shima yaji ko takalmi bai saka ba ya fito daga dakin nata a guje Radhiya tana a kamo shi. Dayake ba niyar kama shi da gaske suka yi ba da gangan suka bari ya gudu. Ragowar yaran nata ta kalla tace kowa ya tashi tana uban gumi kamar wadda tayi tsere. Muryar Radhiya taji tana magana da yaren da bata ganewa.
Wayar karya ta gama da French ta juya ta kalli Halifa da yake jindadin wannan drama yayi ta dariya kamar cikinsa zai kulle "ka rufe kofar nan. Yanzu suka kirani wai ashe sun ga fitar daya kuma sauran ma sun gama shiri yace idan wani ya sake fita daga gidannan harda mu za'a ci da bredin"
Hajiyayye da gudu ta saki mayafinta hankalinta gabadaya ya tashi. Ta ma rasa da me zata ji. Talle da yaki daukar wayarta tun safe taji ya ake ciki game da shannun ko kuwa wakilan majalisar mayu da za'a turo su kama ta. Acinyeki da bredi wata zuciyar ta tuna mata. Harda guntun hawaye sai da tayi bata ankara ba kafin ta daure ta fito inda suke.
"Uhmm nace Malamijo yau me za'a dafa da rana ne? Naga ana ta hira shine baku kirawoni ba" wai ita nan za ta bagarar kamar bata san me suke yi ba. Daga nan ta samu ta arce. Ofishin 'yan sanda zata je ta shigar da kara kafin turawan mayun su iso azo a fitar mata da yaranta.
To shima ba wai yana cikin hayyacinsa bane duk ya gama tsorata ya fara danasanin kiran Radhiya. Yarinyar nan da ya gama sanin halinta me ya kaishi kiranta da kansa. Wayarta ce tayi kara a lokacin taken wakar Celine Dion ta film din Titanic wanda ta sanyawa Awwab. A wurinta wakar bata tsufa sai ma nishadin da take saka ta idan ta tuna masoyinta.
Idanun Malamijo da na Hajiyayye basu da na biyun kwatance a lokacin. Tsoro ne karara ya bayyana ita kuwa tana dauka da turance tace masa "Chèri please follow my lead i'll explain everything later. Say something in German" (ka biyewa duk yadda kaji nayi, zanyi maka bayani daga baya. Ka yi magana da yaren Jamus)
Yana cikin office dinsu a lokacin ya kirata. Abinda tace kawai ya isa ya saka shi gane cewa akwai abinda take yi. Alheran dinsa bata ji, sai dai kuma idan ta canja daga yadda take ta tashi daga yarinyar da ya fara so daga haduwar farko kenan. Fitinanniyar dai ita ce tashi mai sanya shi nishadi a kowane lokaci.
Speaker ta sanya kowa na ji ya rinka yi mata kalaman soyayyar da yasan cewa ba fahimta take yi ba ita ma.
"Amaryar Malamijo kin dai ji me yace. Wai ku jeru a daki ke da yaran naki yanzu zasu shigo. Idan anyi binciken sun ware mayu a cikinku sai su saki sauran"
"Inji uban wa akace mu mayu ne? Garin nan waye bai san gidan iyayena ba? Malamijo kace wani abu mana" ta fada a raunane hawaye na zuba.
"Ince me? Na auro mayya tayi sanadin da majalisar dinkin duniya ta mayu zata zo gidana" ya ce gumi na karyo masa. Gidan gabadaya yayi masa zafi dari bisa dari ya yarda da zancen Radhiya.
Wayar ta dan kara a bakinta "ranka ya dade ko za ka danyi mata hausa ta fahimta. Mayyar da ta auri kakan nawa ce ta fito" ta kalle su "shine wakilinsu da yake kula da hausawan mayu"
"Bata wayar" Awwab yace dariya na ciwo shi. Wace mai tsautsayin ce wannan ta shiga tarkon Alheran?
Ficewa kawai yayi daga dakin a hanya yaci karo da Halifa. Wani mummunan kallo ya maka masa Nene tana biye dashi tace da Halifan allurar soja ce ta motsa saboda Malamijo yayi masa fada. Da yake ba bakon zafi bane sai ya yarda harda tausayawa Emzee din.
Dakin da suka kwana ya shiga ya rinka naushin bango ko zai ragewa kansa fushi. Da ya bar maganar a cikinsa gara ace bai ji ba. Kai dama ace Radhiya ce taji ta gwadawa Salame me ake nufi da uwa. Wai saboda wani can Alh Indararo shine ta makanta musu uwa. Kuma karin abin haushi wai Daada dinsu take so.
"Wallahi sai dai ki mutu amma yafi karfinki"
"Kai da wa?" Yaji Ibrahim yace daga bayansa. Kasa amsawa yayi sai kwanciya da yayi yana ta juya zancen. Abin ya dame shi matuka ya dena walwala ya matsawa Ibrahim suka tafi Kano gidan kakaninsa. Halifa da Hibbah su ma zasu tafi amma kememe Emzee yaki yarda su hada tafiyar saboda baya ko son ganin Halifa. Washegarin tafiyar tasu yaje yace da Malamijo ya basu kudin mota. Dubu goma ya bashi duk da yasan kudin yayi yawa amma gara ya tafi ko hankalinsa ya kwanta. Kullum da zulumin kada Radhiya ta gane yake kwana. Ta shiga damuwa sosai akan yadda kanin nata ya koma sai matsawa Malamijo take yi akan ya tambaye shi ko ta sanar da iyayensu.
**********
Kwanan su Zayyan uku a Sakkwato sai birnin Agadez a kasar Nijar. Da kwatance suka isa unguwar inda gidan Alh Ghoumar da Alh Sidi suke makotaka da juna. Mammee suna Niamey da mijinta tunda dan siyasa ne. Kowa yayi mamakin zuwan Mairama ita kadai tace banda yaran ta tahi lokacin da ta kira kwaya domin a kwatanta musu hanya. Tante Nasara sai da ta kira Radhiya da Emzee taji muryoyinsu ta tabbatar kowa lafiya kafin isowarsu gidan.
Murnarsu kuwa bayan sun ga Zayyan bazata misaltu ba. Masu kuka na yi masu suma suna yi. Dangin Innar Zayyan sun sake nuna bajintarsu da kwarewa wurin rikon zumunci da murnar dawowarshi. Mammee tayi kuka tayi fadan me yasa basu sanar da ita ba sai da suka iso gashi kowa ya rigata ganinsa. Kwanansu biyar 'yan uwa suna faman kokarin kyautata masa da nuna masa cewa shi din dan dangi ne. Tamkar kada ya baro kasar sai dai dole ya koma saboda litinin zaiyi reporting a headquarter ana nemansa.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Radhiya bata kwanta ba sai da ta gama tsara yadda za ta yi da Hajiyayye gobe. Ba'a taba mata kaka a kwana lafiya. Yadda ta rabe mata abinci bata sami ko loma daya ba haka da daren ma dan kadan ta ce Na'e ta zuba musu ita da yaran. Bakinciki yasa Hajiyayye ta kasa komai saboda sau uku tana kokarin zuwa dakin Malamijo sai ta tarar da Ibrahim da Emzee a kofar dakin kamar suna gadinsa.
Bayan kowa yaci abincin safe ne Radhiya ta fito tsakar gida tana tambayar waye mai girki yau. Yadikko ta kama kunnenta ta rike.
"Na fada miki babu mai girki a gidan nan sai amaryar kakanki. Na'e ma da tayi tuwon dare jiya kawaici tayi miki bata ce komai ba"
Hajiyayyen rabewa tayi a jikin kofar dakinta tana jinsu tayi murmushi. Ashe dai Yadikko tasan matsayinta. Idan suka yi kuskuren biyewa wannan yarinyar za ta barsu da jidali ne idan ta tafi don duk wanda ya shiga gonarta sai ya gane kurensa.
"Tunda babu mai girkin dole ni zanyi kenan da kaina. Bari na leka Malamijo ya bada shanu uku ma sun isa da za'ayi yanka"
"Yanka kuma? Radhiya idan kika zo gidan nan bakya zama kiyi ta mana jaye jaye. Nama kuma kema kin sani ba'a kawowa gidan nan har kike kiran yanka."
Bata ankara ba sai ga Malamijo ya fito yau dai sanyi ya saka shi saka kayan kirki ya rufe kasusuwan jikinsa. Daure fuska yayi yana hararar Yadikko.
"Kinji nace bazan bada shanun bane da zaki yanke min hukunci? 'Yar Soja guda nawa kuke bukata?"
"Uku tace" inji Emzee da suka gama sanin me take da niyar yi.
"Amma shanu uku 'Yar Soja waye zai taya ku aikin naman? Yayi yawa. In baku daya dai yau kowa yaci"
Murmushin mugunta tayi da Ibrahim yayi mata alama cewa fa Hajiyayye ta leko daga dakinta tana sauraronsu. Haka take so taji ko wani nata yaji a kai mata rahoto.
"Kada ka damu naman nan ba mune zamu ci ba. Wadanda za'ayiwa yankan kuma danye suke so"
Idanu Malamijo ya zaro "Hajiyayye zaki yiwa yanka?"
Sai da ta kula kowa ita yake sauraro ta dare kan turmi ta zauna "Bakina dai da zasu zo. Jiya da na ga yadda gidan nan ya koma shine na kira Sarkin mayun Faransa...can inda nake karatu. Dayake muna mutumci da 'ya'yansa sai ya daukeni kamar 'yar cikinsa. To shine nayi masa maganarka na cewa ka auro mayya. Yayi ta mamaki tunda yasan ni ba mayyar bace. Shine fa yau da sassafe ya kirani wai ya kai maganar can ofishin majalisar dinkin duniya akan harkar mayu sun ce zasu turo wakilai azo ayi bincike ke"
Idanun Malamijo tuni suka raina fata ya hau rawar jiki "ni nace kiyi zancena da wasu ne? Haba Radhiya ashe baki da hankali ban sani ba. Mayun Najeriya basu cinyeni ba sai na Faransa"
Yadikko tana ji tasan sharrin Radhiya ne amma yadda idanun Malamijo suka kada suka yi ja sai ta kyale ko banza ta rinka tunawa tana dariya.
Cikinsu Ibrahim ne ya iya daure dariyarsa yace "Turawan mayu inajin kince basa cin mutane sai mayu 'yan uwansu ko"
"Eh mana, matsalar dai bincike zasu zo yi. Wai ashe daga last year aka haramtawa duk wanda ba maye ba auren maye saboda gudun rigingimu da suke tasowa." Ta yi kamar ta rage murya za ta yi rada bayan ta san sarai kowa yana ji "yace zasu kama duka mayun gidannan ne a tafi dasu. Hukuncin take dokar shine kisa ta hanyar babbakaraisin din mayun a baiwa oganninsu su ci da bredi"
Tsuuuu zawo ya nemi saukowa daga jikin Hajiyayye cikinta na murdawa tana matse shi da kyar saboda tsabar kaduwa. Babban yaron da tazo dashi gidan ashe shima yaji ko takalmi bai saka ba ya fito daga dakin nata a guje Radhiya tana a kamo shi. Dayake ba niyar kama shi da gaske suka yi ba da gangan suka bari ya gudu. Ragowar yaran nata ta kalla tace kowa ya tashi tana uban gumi kamar wadda tayi tsere. Muryar Radhiya taji tana magana da yaren da bata ganewa.
Wayar karya ta gama da French ta juya ta kalli Halifa da yake jindadin wannan drama yayi ta dariya kamar cikinsa zai kulle "ka rufe kofar nan. Yanzu suka kirani wai ashe sun ga fitar daya kuma sauran ma sun gama shiri yace idan wani ya sake fita daga gidannan harda mu za'a ci da bredin"
Hajiyayye da gudu ta saki mayafinta hankalinta gabadaya ya tashi. Ta ma rasa da me zata ji. Talle da yaki daukar wayarta tun safe taji ya ake ciki game da shannun ko kuwa wakilan majalisar mayu da za'a turo su kama ta. Acinyeki da bredi wata zuciyar ta tuna mata. Harda guntun hawaye sai da tayi bata ankara ba kafin ta daure ta fito inda suke.
"Uhmm nace Malamijo yau me za'a dafa da rana ne? Naga ana ta hira shine baku kirawoni ba" wai ita nan za ta bagarar kamar bata san me suke yi ba. Daga nan ta samu ta arce. Ofishin 'yan sanda zata je ta shigar da kara kafin turawan mayun su iso azo a fitar mata da yaranta.
To shima ba wai yana cikin hayyacinsa bane duk ya gama tsorata ya fara danasanin kiran Radhiya. Yarinyar nan da ya gama sanin halinta me ya kaishi kiranta da kansa. Wayarta ce tayi kara a lokacin taken wakar Celine Dion ta film din Titanic wanda ta sanyawa Awwab. A wurinta wakar bata tsufa sai ma nishadin da take saka ta idan ta tuna masoyinta.
Idanun Malamijo da na Hajiyayye basu da na biyun kwatance a lokacin. Tsoro ne karara ya bayyana ita kuwa tana dauka da turance tace masa "Chèri please follow my lead i'll explain everything later. Say something in German" (ka biyewa duk yadda kaji nayi, zanyi maka bayani daga baya. Ka yi magana da yaren Jamus)
Yana cikin office dinsu a lokacin ya kirata. Abinda tace kawai ya isa ya saka shi gane cewa akwai abinda take yi. Alheran dinsa bata ji, sai dai kuma idan ta canja daga yadda take ta tashi daga yarinyar da ya fara so daga haduwar farko kenan. Fitinanniyar dai ita ce tashi mai sanya shi nishadi a kowane lokaci.
Speaker ta sanya kowa na ji ya rinka yi mata kalaman soyayyar da yasan cewa ba fahimta take yi ba ita ma.
"Amaryar Malamijo kin dai ji me yace. Wai ku jeru a daki ke da yaran naki yanzu zasu shigo. Idan anyi binciken sun ware mayu a cikinku sai su saki sauran"
"Inji uban wa akace mu mayu ne? Garin nan waye bai san gidan iyayena ba? Malamijo kace wani abu mana" ta fada a raunane hawaye na zuba.
"Ince me? Na auro mayya tayi sanadin da majalisar dinkin duniya ta mayu zata zo gidana" ya ce gumi na karyo masa. Gidan gabadaya yayi masa zafi dari bisa dari ya yarda da zancen Radhiya.
Wayar ta dan kara a bakinta "ranka ya dade ko za ka danyi mata hausa ta fahimta. Mayyar da ta auri kakan nawa ce ta fito" ta kalle su "shine wakilinsu da yake kula da hausawan mayu"
"Bata wayar" Awwab yace dariya na ciwo shi. Wace mai tsautsayin ce wannan ta shiga tarkon Alheran?