Sashe 4
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tsorace Mairama ta hada kayan saboda gudun kada ya hanata tafiya. Basu dade ba a dakin Yadikko ta kwala musu kira suka tafi dakinta.
“Ni da Nene mun roka muku alfarma ya bari kuyi kwana goma. Idan kunje ku tabbatarwa da kanku bazaku wuce lokacin da aka dibar muku ba”
Murna a wurin Mairama kai kace bikin na dangin tata mahaifiyar ne. Salame kuwa har ta gama tsoro bai bata damar sakin jiki ba.
Da zasu tafi kashedi Malamijo ya rinka yanka musu kusan minti goma yana abu daya. Nene da Yadikko sunyi masa shigar sauri sun kuma hade masa kai ba don haka ba Ta Madina bata isa ya bata Salame harda karin Mairama ba.
**********
Kano ta Dabo tumbin giwa, birnin na Kano a yau yayi manyan baki daga garin Sumaila wato Salame da Mairama. Wata unguwa da basu san sunanta ba suka wuce zuga guda ta ‘yan biki daga Sumaila. Yadda Mairama ta saki jiki cikin mutanen sai ta baka mamaki da tausayi. Tun tasowarsu ita dai bata taba zuwa wani wuri da zata ji dadi da sa’anninta ba sai makaranta. A can ma ba wani sakin jiki gareta ba saboda tana ganin kowa yafi karfinsu. Gasu dai da uba mai kudi amma daga kayan makaranta da akwati baya basu komai. Dan siyayyar nan ta provision sai dai su gani a kwanar wasu. Shiyasa an rainasu sosai musamman Salame da sunanta ya dace da halinta.
Anyi Kamu a ranar da suka sauka da daddare inda amare aka kunshesu a daki tsakiyar ‘yan mata kawayensu da ‘yan uwa, dangin angwayen su ka zo aka feshesu da turare.
Washegari kuwa lanchin (luncheon) za’ayi a filin wani katon gida mallakar kanin baban amaren biyu.
Salame ta sami kaya kala biyar sababbi, biyu daga yayar innarta uwar amare sai uku daga Ta Madinan. Guda ta cire a ciki ta baiwa Mairama tace ta saka kada ta fita daban tunda su dai ba wasu suturun arziki na shiga taro garesu ba. Mairama sai murna da godiya ta sanya atampar da akayi mata dinkin riga da zani buba anyiwa rigar cin baki da irin lace dinnan na adon kaya a wuya da hannaye. Tayi kyau abinta gwanin sha’awa haka itama Salamen. Motoci bus bus ne aka haya suka rinka kwasarsu aka kaisu wurin bikin.
Salame tana manne da kanwarta duk da cewa dai tana sakin jiki da ‘yan uwanta suna hira. Teburinsu su bakwai ne da yake a zagaye yake suna fuskantar juna ana ta tsokanar wata cikinsu da tayi saurayi daidai kofar shigarsu gidan. Karaf idanun Salame suka sauka akan Zayyan ya nisa suna magana mai matukar mahimmanci da Hadir. Daya daga cikin angwayen dan uwa ne ga Hadir din.
Iyayensu maza ciki daya suka fito. Shiyasa da Zayyan ya iso Kano aka sanya shi cikin abokan ango. Cinikin fili suka gama kafin zuwansu nan a unguwar gandun albasa. Shi dai Zayyan ya ga wurin babu gidaje sosai amma dillalin yana ta cika masa baki cewa nan gaba kadan unguwar zata hade harma a rasa filin saidawa. Shima da yake ba mazauni ba sai ya amince ya biya kudi bisa shawarar Hadir. Zancen gini kuma a hankali zasu yi tunda har yanzu ko rabin kudin da aka bashi bai taba ba.
Takardun filin ne kwafi biyu da sa hannayensu ya mikawa Hadir daya yace gata nan ya ajiye masa shi kuma zai aje daya a wurinsa. Sai da suka gama komai duk motsinsa akan idon Salame sannan su ka koma cikin samari ‘yan uwansu. Ba karamin tafiya yayi da imanin Salame ba lokaci guda taji sonsa ya game zuciyarta.
Mairama kuwa an sami sake hira tayi hira an kawo abinci kowa plate dinta shake da jallof din shinkafa da yankan naman sa da aka soya sai salad, tumatir da albasa. Wayyo dadi jikinta har tsuma yake kuma wai aka kirga su aka sake ajiye musu ledar tsire ga kuma lemon kwalba. Kar kaso ka ga idanun Mairama hankalinta yayi kwano na Salame kuma yayi kan Zayyan da bai san da zamanta a wurin ba.
Police band suna wakarsu amma kusan kowa abinci yake ci babu ‘yan rawa. Kwalbar fanta chapman Mairama ta faki ido ta daga tana kwankwada asalin dadi da sanyi yana ratsata ta manta da kunyar idanun jama’a. Bata samu ta sauke kwalbar mai 35cl ba sai da ta shanye shi tas. Daga lokacin da ta soma waige ta tabbatar babu mai kallonta har zuwa sanda ta ajiye kwalbar Zayyan yana gani. Baki ya rike yana kallon yadda ko da ta shanye sai da ta sake daga kwalbar ta kwakkwafeta a bakinta. Kasa cin nasa abincin yayi komai tayi sai yaji ya burge shi shi kadai ya rinka murmushi. Teburin kusa da nasu Mairama ne duka matan dama su uku ne su ka tashi a tare. Mairama tana ji suna cewa sallama zasu yiwa amaren su tafi. Tana ganin sun bace cikin jama’a ta wayance ta tashi da kwalbar lemonta ta ajiye a wurin ta dauki wata mirinda da ko rabinta ba’a sha ba. Plate din nasu ma basu wani ci sosai ba ga nama sun bari. Kamar ta dauka shima sai dai ta hakura lemon yafi mahimmaci a gareta.
[7/4, 7:38 PM] +234 806 334 4334: D
Banda wanda ta dauka sai da ta dan kurbi na kusa dashi sannan ta juya da sauri da taji ana kiran sunanta.
Hadir ya tabo Zayyan da yake kyakyata dariya shi kadai da ya hango Mairama tana zaro idanu. Matan da suka bar teburin ne suka dawo daya ta soma cigiyar lemon da ta bari. Mairama tayi tsit don kuwa saura kadan ma ta shanye mirindar.
“Kai lafiyarka kuwa?”
Idanu ya lumshe yana kallon kyakkyawar bafulatanar ta tsure karshe ta kuma rungume kwalbar ta boye cikin lullubinta.
“Mata nayi”
Hadir ya tura kujera baya da sauri “nuna min ita muje mu tsarata wallahi”
Zayyan ya mike da sauri “naki din, kai fa satar budurwa kake yi”
Sauran mazan wurin suka sa dariya shi kuma ya kwashe lemuka uku da ba’a bude ba yayi gaba.
Salame tana ganin ya nufosu ta tattaro dukkan nutsuwarta tana murmushi don tun dazu suke hada ido yana murmushi a zatonta ita yake yiwa yayin da hankalinsa kacokan yana kan Mairama ne.
Sallama yayi musu matan teburin gefen ana ta masifar rashin ganin lemo ya mika musu biyu sanna ya dubi Mairama da tsoro ya hanata motsi ya mika mata chapman irin wadda ta fara sha. Dan rausayo kai yayi ya duku wurin kanta.
“Kanwata ga wannan ki kara”
Sai lokacin ta dena jin mitar wadancan matan ta tsuke baki batare da ta juya ba
“rike kayanka bana so”
“Haka ma zaki ce? To ki shirya kuwa don zan tona” yace yana rage murya sosai daidai kunnenta.
A firgice ta waiga idanunta suka sauka cikin nashi. Ko ma me tayi niyar cewa makalewa yayi a wuyanta ta sami kanta da manta a ina ma take na ‘yan dakiku. Lallausan murmushi ya sakar mata wanda ya sake fito da kyaunsa da cikar sa.
“Muje can na fada miki me da me na gani” ya nuna can jikin katanga wurin wata katuwar bishiyar darbejiya.
Ko dogon nazari bata tsaya yi ba ta bi bayansa kuwa don ta gama tsorata kaddai ace ya ga lokacin da ta dauke musu lemon. Wani mugun daci ne ya taso ya tokare wuyan Salame har suka isa bakin bishiyar tana binsu da kallo. Me yake shirin faruwa tsakanin kanwarta da mutumin da take jin bata taba son wani abu makamancinsa ba a rayuwarta. Kallon da yake yiwa Mairama kadai ya isheta amsa. Sauran ‘yan mata kuwa sai shewa itama zasu kwana suna tsokanarta kenan.
Suna isa wurin bishiyar yace “da farko dai sunana Zayyan, ni soja ne”
Idanunta suka yi kwalkwal da hawaye suna barazanar saukowa. Murya na rawa ta fito da kwalbar da ta boye cikin mayafinta “me yayi zafi ni ‘yasu. Daga shan lemo sai dauko sojoji. Ni wallahi nayi zaton sun tashi kenan. Don Allah kuyi hakuri kada ka kamani” tace tana kallon Hadir da ya iso inda suke.
Maganarta dariya ta bashi ya mikawa abokinsa hannu da nufin gabatar dashi a gareta “Zayyan Tureta…”
Wani kallo ta watsa masa tsoron yayi nasa wuri ta yatsina fuska za ta gwada musu tsiwarta “ya tureni? To Bismillah dan halak ka fasa. Mutum ya tabani ba hakura zanyi ba”
Kasa cewa komai suka yi sai dariyar da suke yi mata tana karkada hannuwa. A ranta tana jin tsoronsu zaratan samari irin haka amma kuma bata so ta basu damar cutar da ita.
“Kinga ‘yan mata sunansa Zayyan Muhammad Tureta ba tuureta na hankadewa ba, garinsu ne a Sakkwato”
Kunya taji sosai ta rufe fuska “lahhhhh”
Shima Zayyan sai ya biye mata yace “lahhhhh”
Hadir yana dariya ya basu wuri Zayyan ya kura mata ido “yaya sunanki”
“Mairama” ta amsa da karamar murya.
“Kamar Maryam yake?”
“Haka dai aka saka min a gida ni”
“To fillo ni dai Mairam zan ce. Ina ne gidanku?”
Kallonsa tayi na dan lokaci tana son yin nazari shin kamata zaiyi ko kuwa dai wani abin ne daban.
“Ba kamani kazo yi ba?”
“Kwantar da hankalinki babu mai sanin kin saci mirinda”
Yadda yayi maganar yana kasha mata ido ya sanya hankalinta ya kwanta itama harda dariya. Kwatancen gidansu ya nema daga gareta da bayanin kansa sannan yace duk da karancin lokaci yana son ganawa da mahifinta domin ya nemi aurenta. Kunya sosai ta lullube Mairama don itama a ‘yar hirar tasu har ya shige zuciyarta. Ta fada masa gidan da suke yanzu da kuma kwatancen gidansu yace zai zo da daddare su sake fahimtar juna.
Kusan da gudu-gudu ta koma teburinsu ‘yan matan suka soma zuba mata tambayoyi. Jiki na rawa ta fada jikin Salame tana dariya.
“Bazaku ji komai ba sai ma gama shawara da Addata”
Wani murmushin yake Salame tayi a ranta tana nadamar tahowarsu da Mairama. Ita kuwa dadi ya cikata ta fada mata yadda suka yi.
Cikin gatse tace “kice dai wannan tafiyar taki ce”
Bata fahimta ba shiyasa tayi murmushi “gaskiya tawa ce, yace zai tambayi gidan da muke sai yazo anjima. Ai tare zamu fito ki ganshi da kyau. Hmmm Hausarsa sai ta baki dariya, sakkwatanci yake”
“Ni da Nene mun roka muku alfarma ya bari kuyi kwana goma. Idan kunje ku tabbatarwa da kanku bazaku wuce lokacin da aka dibar muku ba”
Murna a wurin Mairama kai kace bikin na dangin tata mahaifiyar ne. Salame kuwa har ta gama tsoro bai bata damar sakin jiki ba.
Da zasu tafi kashedi Malamijo ya rinka yanka musu kusan minti goma yana abu daya. Nene da Yadikko sunyi masa shigar sauri sun kuma hade masa kai ba don haka ba Ta Madina bata isa ya bata Salame harda karin Mairama ba.
**********
Kano ta Dabo tumbin giwa, birnin na Kano a yau yayi manyan baki daga garin Sumaila wato Salame da Mairama. Wata unguwa da basu san sunanta ba suka wuce zuga guda ta ‘yan biki daga Sumaila. Yadda Mairama ta saki jiki cikin mutanen sai ta baka mamaki da tausayi. Tun tasowarsu ita dai bata taba zuwa wani wuri da zata ji dadi da sa’anninta ba sai makaranta. A can ma ba wani sakin jiki gareta ba saboda tana ganin kowa yafi karfinsu. Gasu dai da uba mai kudi amma daga kayan makaranta da akwati baya basu komai. Dan siyayyar nan ta provision sai dai su gani a kwanar wasu. Shiyasa an rainasu sosai musamman Salame da sunanta ya dace da halinta.
Anyi Kamu a ranar da suka sauka da daddare inda amare aka kunshesu a daki tsakiyar ‘yan mata kawayensu da ‘yan uwa, dangin angwayen su ka zo aka feshesu da turare.
Washegari kuwa lanchin (luncheon) za’ayi a filin wani katon gida mallakar kanin baban amaren biyu.
Salame ta sami kaya kala biyar sababbi, biyu daga yayar innarta uwar amare sai uku daga Ta Madinan. Guda ta cire a ciki ta baiwa Mairama tace ta saka kada ta fita daban tunda su dai ba wasu suturun arziki na shiga taro garesu ba. Mairama sai murna da godiya ta sanya atampar da akayi mata dinkin riga da zani buba anyiwa rigar cin baki da irin lace dinnan na adon kaya a wuya da hannaye. Tayi kyau abinta gwanin sha’awa haka itama Salamen. Motoci bus bus ne aka haya suka rinka kwasarsu aka kaisu wurin bikin.
Salame tana manne da kanwarta duk da cewa dai tana sakin jiki da ‘yan uwanta suna hira. Teburinsu su bakwai ne da yake a zagaye yake suna fuskantar juna ana ta tsokanar wata cikinsu da tayi saurayi daidai kofar shigarsu gidan. Karaf idanun Salame suka sauka akan Zayyan ya nisa suna magana mai matukar mahimmanci da Hadir. Daya daga cikin angwayen dan uwa ne ga Hadir din.
Iyayensu maza ciki daya suka fito. Shiyasa da Zayyan ya iso Kano aka sanya shi cikin abokan ango. Cinikin fili suka gama kafin zuwansu nan a unguwar gandun albasa. Shi dai Zayyan ya ga wurin babu gidaje sosai amma dillalin yana ta cika masa baki cewa nan gaba kadan unguwar zata hade harma a rasa filin saidawa. Shima da yake ba mazauni ba sai ya amince ya biya kudi bisa shawarar Hadir. Zancen gini kuma a hankali zasu yi tunda har yanzu ko rabin kudin da aka bashi bai taba ba.
Takardun filin ne kwafi biyu da sa hannayensu ya mikawa Hadir daya yace gata nan ya ajiye masa shi kuma zai aje daya a wurinsa. Sai da suka gama komai duk motsinsa akan idon Salame sannan su ka koma cikin samari ‘yan uwansu. Ba karamin tafiya yayi da imanin Salame ba lokaci guda taji sonsa ya game zuciyarta.
Mairama kuwa an sami sake hira tayi hira an kawo abinci kowa plate dinta shake da jallof din shinkafa da yankan naman sa da aka soya sai salad, tumatir da albasa. Wayyo dadi jikinta har tsuma yake kuma wai aka kirga su aka sake ajiye musu ledar tsire ga kuma lemon kwalba. Kar kaso ka ga idanun Mairama hankalinta yayi kwano na Salame kuma yayi kan Zayyan da bai san da zamanta a wurin ba.
Police band suna wakarsu amma kusan kowa abinci yake ci babu ‘yan rawa. Kwalbar fanta chapman Mairama ta faki ido ta daga tana kwankwada asalin dadi da sanyi yana ratsata ta manta da kunyar idanun jama’a. Bata samu ta sauke kwalbar mai 35cl ba sai da ta shanye shi tas. Daga lokacin da ta soma waige ta tabbatar babu mai kallonta har zuwa sanda ta ajiye kwalbar Zayyan yana gani. Baki ya rike yana kallon yadda ko da ta shanye sai da ta sake daga kwalbar ta kwakkwafeta a bakinta. Kasa cin nasa abincin yayi komai tayi sai yaji ya burge shi shi kadai ya rinka murmushi. Teburin kusa da nasu Mairama ne duka matan dama su uku ne su ka tashi a tare. Mairama tana ji suna cewa sallama zasu yiwa amaren su tafi. Tana ganin sun bace cikin jama’a ta wayance ta tashi da kwalbar lemonta ta ajiye a wurin ta dauki wata mirinda da ko rabinta ba’a sha ba. Plate din nasu ma basu wani ci sosai ba ga nama sun bari. Kamar ta dauka shima sai dai ta hakura lemon yafi mahimmaci a gareta.
[7/4, 7:38 PM] +234 806 334 4334: D
Banda wanda ta dauka sai da ta dan kurbi na kusa dashi sannan ta juya da sauri da taji ana kiran sunanta.
Hadir ya tabo Zayyan da yake kyakyata dariya shi kadai da ya hango Mairama tana zaro idanu. Matan da suka bar teburin ne suka dawo daya ta soma cigiyar lemon da ta bari. Mairama tayi tsit don kuwa saura kadan ma ta shanye mirindar.
“Kai lafiyarka kuwa?”
Idanu ya lumshe yana kallon kyakkyawar bafulatanar ta tsure karshe ta kuma rungume kwalbar ta boye cikin lullubinta.
“Mata nayi”
Hadir ya tura kujera baya da sauri “nuna min ita muje mu tsarata wallahi”
Zayyan ya mike da sauri “naki din, kai fa satar budurwa kake yi”
Sauran mazan wurin suka sa dariya shi kuma ya kwashe lemuka uku da ba’a bude ba yayi gaba.
Salame tana ganin ya nufosu ta tattaro dukkan nutsuwarta tana murmushi don tun dazu suke hada ido yana murmushi a zatonta ita yake yiwa yayin da hankalinsa kacokan yana kan Mairama ne.
Sallama yayi musu matan teburin gefen ana ta masifar rashin ganin lemo ya mika musu biyu sanna ya dubi Mairama da tsoro ya hanata motsi ya mika mata chapman irin wadda ta fara sha. Dan rausayo kai yayi ya duku wurin kanta.
“Kanwata ga wannan ki kara”
Sai lokacin ta dena jin mitar wadancan matan ta tsuke baki batare da ta juya ba
“rike kayanka bana so”
“Haka ma zaki ce? To ki shirya kuwa don zan tona” yace yana rage murya sosai daidai kunnenta.
A firgice ta waiga idanunta suka sauka cikin nashi. Ko ma me tayi niyar cewa makalewa yayi a wuyanta ta sami kanta da manta a ina ma take na ‘yan dakiku. Lallausan murmushi ya sakar mata wanda ya sake fito da kyaunsa da cikar sa.
“Muje can na fada miki me da me na gani” ya nuna can jikin katanga wurin wata katuwar bishiyar darbejiya.
Ko dogon nazari bata tsaya yi ba ta bi bayansa kuwa don ta gama tsorata kaddai ace ya ga lokacin da ta dauke musu lemon. Wani mugun daci ne ya taso ya tokare wuyan Salame har suka isa bakin bishiyar tana binsu da kallo. Me yake shirin faruwa tsakanin kanwarta da mutumin da take jin bata taba son wani abu makamancinsa ba a rayuwarta. Kallon da yake yiwa Mairama kadai ya isheta amsa. Sauran ‘yan mata kuwa sai shewa itama zasu kwana suna tsokanarta kenan.
Suna isa wurin bishiyar yace “da farko dai sunana Zayyan, ni soja ne”
Idanunta suka yi kwalkwal da hawaye suna barazanar saukowa. Murya na rawa ta fito da kwalbar da ta boye cikin mayafinta “me yayi zafi ni ‘yasu. Daga shan lemo sai dauko sojoji. Ni wallahi nayi zaton sun tashi kenan. Don Allah kuyi hakuri kada ka kamani” tace tana kallon Hadir da ya iso inda suke.
Maganarta dariya ta bashi ya mikawa abokinsa hannu da nufin gabatar dashi a gareta “Zayyan Tureta…”
Wani kallo ta watsa masa tsoron yayi nasa wuri ta yatsina fuska za ta gwada musu tsiwarta “ya tureni? To Bismillah dan halak ka fasa. Mutum ya tabani ba hakura zanyi ba”
Kasa cewa komai suka yi sai dariyar da suke yi mata tana karkada hannuwa. A ranta tana jin tsoronsu zaratan samari irin haka amma kuma bata so ta basu damar cutar da ita.
“Kinga ‘yan mata sunansa Zayyan Muhammad Tureta ba tuureta na hankadewa ba, garinsu ne a Sakkwato”
Kunya taji sosai ta rufe fuska “lahhhhh”
Shima Zayyan sai ya biye mata yace “lahhhhh”
Hadir yana dariya ya basu wuri Zayyan ya kura mata ido “yaya sunanki”
“Mairama” ta amsa da karamar murya.
“Kamar Maryam yake?”
“Haka dai aka saka min a gida ni”
“To fillo ni dai Mairam zan ce. Ina ne gidanku?”
Kallonsa tayi na dan lokaci tana son yin nazari shin kamata zaiyi ko kuwa dai wani abin ne daban.
“Ba kamani kazo yi ba?”
“Kwantar da hankalinki babu mai sanin kin saci mirinda”
Yadda yayi maganar yana kasha mata ido ya sanya hankalinta ya kwanta itama harda dariya. Kwatancen gidansu ya nema daga gareta da bayanin kansa sannan yace duk da karancin lokaci yana son ganawa da mahifinta domin ya nemi aurenta. Kunya sosai ta lullube Mairama don itama a ‘yar hirar tasu har ya shige zuciyarta. Ta fada masa gidan da suke yanzu da kuma kwatancen gidansu yace zai zo da daddare su sake fahimtar juna.
Kusan da gudu-gudu ta koma teburinsu ‘yan matan suka soma zuba mata tambayoyi. Jiki na rawa ta fada jikin Salame tana dariya.
“Bazaku ji komai ba sai ma gama shawara da Addata”
Wani murmushin yake Salame tayi a ranta tana nadamar tahowarsu da Mairama. Ita kuwa dadi ya cikata ta fada mata yadda suka yi.
Cikin gatse tace “kice dai wannan tafiyar taki ce”
Bata fahimta ba shiyasa tayi murmushi “gaskiya tawa ce, yace zai tambayi gidan da muke sai yazo anjima. Ai tare zamu fito ki ganshi da kyau. Hmmm Hausarsa sai ta baki dariya, sakkwatanci yake”