Sashe 21
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hmm ai ba'a cewa komai Haladu. Yaron nan harbi, harbi dai da kake ji da gani a finafinan su Amita Bachan sai da aka sakar masa harsashi kusan goma amma a haka ya rinka kutsa kai cikin abokan gaba yana gamawa dasu. Bawan Allah ya tafi ya barwa Mairama da yaranta komai nasa. Ko sati batayi da haihuwa ba. Shine ma zanje domin na tattaro dukiyar na kawo nan sai na juya mata da kaina saboda duk yadda ka kai da yarda da wani ba kamar naka ba. Nakan ma mahaifi"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Maikudi ne tsaye a ofishin da aka tura shi cikin barikin su Zayyan akan maganar kudi ne dai.
"Jiya Babanku yazo akan zancen nan mun fada masa bamu da komai. Ya bada adireshinsa duk lokacin da kudi yazo zamu nemeku" officer din ya bashi amsa bayan ya gama jero tambayoyi.
Yana hargaginsa na rashin mutumci yace "Ashe cewa yayi shine babanmu don ya ci kudin gado. To wallahi karya yake. Babu wata alaka ta jini tsakaninmu"
Wani sojan ne ya shigo yana tambayar wancan me yake faruwa cikin harshen turanci. Sai da ya sara masa ya bashi amsa da gani ya fishi mukami.
Maikudi yana jin ana bayani duk da bai iya gane duka maganar amma ya dan fahimci me akeyi ya katse wancan "You understant Zayyan Muhammad Tureta is die? Me. Biggggggggg broza. Is me faza dinmu daya ai" ya nuna kansa yana murmushi yana so su fahimci shine babban wan Zayyan.
Mutumin ya hade rai yace a kore shi kuma idan ya kuskura ya sake zuwa ba'a neme shi ba a kulle shi saboda yana mudu hayaniya. Dayan yana soma fassara masa bai tsaya jin karshen ba ya fice yana ta Allah Ya isa an kashe masa kani. A hanyarsa ta komawa ne ya rinka tunanin dole fa akwai abinda Zayyan ya barwa matarsa. Idan ba haka ba da me suke rayuwa duk tsahon lokacin nan? Yafi karfin ita da kwadayayyen babanta suyi masa wayau akan hakkinsa.
Yana zuwa dakin da Malamijo yayi masauki ya shiga. A shirye suke suna jiran dawowar Mairama.
"Dama nazo akan yaran nan ne Radhiya da Zayyan. Nace ko zaka yiwa Mairama magana idan ta yaye shi zan zo na dawo dasu gabanmu saboda gatansu dai bai wuce wurin dangin mahaifinsu. Idan kun tafi yanzu kai ma nauyi ne kawai zai kara hawa kanka. Sannan bazan zuba ido bane tayi aure 'ya'yana su koma agolanci a gidan wani"
Malamijo an tabo inda yake masa kaikayi kuwa. Ina zai kai karin bakuna uku a gidansa. Gara Mairama yana son abarsa, amma yaran nan da aka ha'ince shi yayi ta yiwa babansu kallon kitse ashe rogo ne "indai wannan ne babu damuwa. Zanyi magana da ita kuma dole ta amince don nima bazan so suyi rayuwar agolanci ba azo ana wulakantasu"
Maikudi ya fita da wani mugun murmushi. Soro ya koma ya zauna jiranta. Ilai kuwa babu jimawa sai gata tana ta sauri kada a gaji da jiranta. Dukawa ta danyi ta gaishe shi ya yafito ta da hannu.
"Yaki zo Mairama. Magana nake son yi da ke"
Kanta a kasa ya fada mata yadda ya fadawa Malamijo. Ai tuni ta saka kuka iya karfinta tana rokansa ya rufa mata asiri ita bata da niyar sake aure.
"Kinga da har mun gama magana da babanki"
Gabanta ne ya fadi. Ta san halin Malamijo kuma tas zai bada yaran nata.
"Don Allah kayi hakuri"
"Naji, amma bazaki bar garin nan ba sai kin fito da dukiyar kanina. Dole ne a raba gadonsa saboda a sauke masa nauyi"
Hannunta yana rawa ta zaro envelop dinnan daga jakarta ya warce gabadaya. Sakar masa tayi kafin ya hada da hannunta.
"Daren jiya na gansu shine nace dama yanzu zan fito dasu ayi abinda ya kamata"
Kankance idanu yayi yana kallonta bayan ya zaro takardun gidan da kuma damin kudi da aka nannade da kyauro "ashe ke mutuniyar banza ce ban sani ba? Wato da guduwa zakiyi da komai saboda tsabar mugunta da bakin hali kamar na tsohonki"
Ta shiga girgiza kai tana hawaye "a'a wallahi"
Wasikarta ta hango ta fadi ta mika hannu ya taketa da sauri da kafa "meye a ciki?"
Hankalinta yayi matukar tashi "wallahi Allah wasika ce ya bar min. Ba takardar komai bace"
Sai ta ga yayi murmushi saboda ya fuskanci yadda ta rude "soyayya manya" yatsansa ya kada mata "kalli nan, zan cire takardun gidan saboda dama ina binsa bashi da bai biya ba. Ina jin gidan ma bazai isa ya biyani ba amma dai su kadai zan dauka. Muje ciki idan munafukan dattijan nan sun zo ki basu kudin a rabawa wanda aka ga damar bawa. Ni kuma nayi miki alkawarin babu wanda ya isa ya rabaki da 'ya'yanki kuma zaki koma Kano da wasikar masoyinki"
Mairama kallon mugunta irin ta Maikudi ta tsaya yi ta rasa shawarar yankewa. A zatonta zaa raba gado a barwa yaranta gidan sai su zauna a ciki. Ita kuma a cikin kudin ta nemi abinyi domin kula dasu. Wani hawaye ke bin kuncinta tana jin zafinsu har zuciyarta "hakan yayi maka?"
Ya dage gira "yayi...ki sani idan kina tunanin juya magana ko Jume tayi kadan tasa na bar miki yaran nan balle kuma wancan tsohon Mal. Aminu. Mahaifinki kuma a yadda na fahimta ko sadakarki na nema zai iya hada min"
Share idanunta tayi tabi bayansa. Kowa yayi zaton kukan tafiya ne take yi da mutuwar mijinta. Su Mal.Aminu sun zo ta dauko kudi ta mika masa. A take aka kira wani malami ya kasafta da aukinsu kuwa aka bata nata aka ware na yaran yace batun bashi fa Mairama tace ya tabbatar mata babu msi binsa komai kafin ya tafi. Maikudi ko tari baiyi ba ganin babu mai gadon nashi sai su kadai. Jume har dadi taji yayi hankali.
Nasiha da ban hakuri aka sake yiwa juna sannan Mal.Aminu ya roki alfarmar kada ta tafi ta yanke zumunci dasu albarkarcin 'ya'ya "mu kuma nan babban kalubale ne a garemu mu da gwamnati. Mu dubi marayun yaran nan da mahaifiyarsu kafin mu ga me Allah Ya tsara musu. Haka ma gwamnatin ta dubi rayuwar sojojin da take takama da sadaukarwarsu. A dubi masu ran wanda suke a bakin aiki, a dubi masu rauni da nakasa sannan a dubi iyalan mamatan domin a gaskiya akwai nakasu mai girma a rayuwar iyalan bayin Allahn nan"
Sun fara fitowa mata ana ta kuka Maikudi ya samu ya tarar da Malamijo shi kadai iska tana ta kada yalolon yadin jikinsa yana manne masa ramar tana kara nunawa. Takardun gidan ya nuna masa yana murmushin samun nasara.
"Naga ka kawo idanu ka dora akan dukiyar da baka da alaka da taruwarta shine nace bari dai na nuna maka waye Maikudi."
Ware ido Malamijo yayi ya karewa takardun kallo "na meye?"
"Na gidan Zayyan ne wanda yanzu ya zama nawa. Kana iya kaini kotu don a kwatarwa 'yarka da jikoki hakkinsu amma ka sani kana yin hakan zan rabata da yaran nan ni kuma. Ta fada min akan ta baka dukiyarta gara kowa ya rasa don baka ragawa kowa akan kudi"
Kallon Mairama yayi zuciyarsa tana tafarfasa. Wato Zayyan yana da gida shine ta dauka ta bawa wan mijinta tana tunanin zata dawo masa gida ta jabe ya ciyar dasu. Lallai Mairama bata gama saninsa bane shiyasa har taje tana tona masa asiri. Har shi zata ha'inta yana mahaifinta. Kwafa yayi yana jiran su kebe don bashi da bukatar magana a gaban mutanen da ya kula bakinsu duka daya.
Maikudi kuwa dariya yayi bayan ya tafi. Alamun Malamijo da ya gani ne yasa shi wannan magana sai gashi tazo daidai da halin nasa. Mairama da Zayyan ma ta kasa tonawa mahaifinta asiri a gabansa me zai kaita fada a gaban Maikudi?
Radhiya ta dauka Hajjo ta goya Zayyan suka tafi tashar da zasu sami motar Kano. Sai da suka dau hanya don Salisu ya biya su kadai ne a ciki Mairama tana hawayenta Nene Marka na bata baki kawai Malamijo ya soma fada akan bayar da takardun gida da tayi. Kai, ita kam da me zata ji ne a rayuwarta. Tana kuka tayi musu bayanin yadda abin ya kasance.
"Ko dai mu koma ne a karbo takardun? Duk tsiyarsa baifi karfin hukuma ba fa Mairama" Salisu yace nasa ran a bace.
Tsorata tayi "don Allah ku kyale shi. Yaran nan zai karbe, babansu ma baiji dadin zama dashi ba"
Nene tace "Duk da haka Mairama mu zamu tsaya miki. Gidan a ina yake?"
"A Kano ne"
Salisu ya tabo dreban "Malam don Allah kayi hakuri ko zamu koma"
"Babu inda zamu je. Idan kuma sai kun koma to ni a ajiyeni a nan."
Nene Marka tace "haba Malamijo meye hakan?"
Rufe idanu yayi yana ta fada don sosai yaji haushin maganar Maikudi da rasa gidan da yayi. Ace 'yarsa da yafi so da tausayi a cikin 'ya'yansa ita ce tayi masa haka.
"Ina nan kan baka na bazan koma ba sannan kuma ki shirya tunda dangin miji sunfi uba ni bazan dauki nauyin kowa ba. Gida dai gaki gashi kuje a baku daki. Sai yanzu na raina waye Zayyanun ma. Har me yayi miki wanda ni ban miki dubunsa ba. Ji gidan da ya ajiyeki...."
Ta daure matuka amma bata jin zata taba jurewa wani ko da kuwa Malamijo ne ya zagi Zayyan. Ko bata aure shi ba yanzu ta san daraja da kimar soja....wallahi yafi karfin raini.
"Yayi min komai Malamijo" tace cikin kuka tana rungume Nene iya karfinta har Radhiya sai da ta tsorata "ko a kango muka zauna dashi har abada bani da tamkarsa. Wayyo ni ashe haka mutuwa take da daci da tona asiri? Lokacin da nayi maraicin uwa bansan ciwon rashi ba saboda bamu saba ba. Allah Ka jikan Zayyan ko Ka dauki raina nima na huta"
Zubar hawayenta ya taba Malamijo bare da ya ga ta rike kirjinta da yake mata mugun zafi. Dreban yace wa su juya ta dago rinannun jajayen idanunta.
"Allah Ya kaimu masu gidan su girma zasu karbi abinsu da izinin Allah. Amma a yanzu tunda yace yaji ya gani zai ci haram bazan shiga tsakaninsu ba"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Maikudi ne tsaye a ofishin da aka tura shi cikin barikin su Zayyan akan maganar kudi ne dai.
"Jiya Babanku yazo akan zancen nan mun fada masa bamu da komai. Ya bada adireshinsa duk lokacin da kudi yazo zamu nemeku" officer din ya bashi amsa bayan ya gama jero tambayoyi.
Yana hargaginsa na rashin mutumci yace "Ashe cewa yayi shine babanmu don ya ci kudin gado. To wallahi karya yake. Babu wata alaka ta jini tsakaninmu"
Wani sojan ne ya shigo yana tambayar wancan me yake faruwa cikin harshen turanci. Sai da ya sara masa ya bashi amsa da gani ya fishi mukami.
Maikudi yana jin ana bayani duk da bai iya gane duka maganar amma ya dan fahimci me akeyi ya katse wancan "You understant Zayyan Muhammad Tureta is die? Me. Biggggggggg broza. Is me faza dinmu daya ai" ya nuna kansa yana murmushi yana so su fahimci shine babban wan Zayyan.
Mutumin ya hade rai yace a kore shi kuma idan ya kuskura ya sake zuwa ba'a neme shi ba a kulle shi saboda yana mudu hayaniya. Dayan yana soma fassara masa bai tsaya jin karshen ba ya fice yana ta Allah Ya isa an kashe masa kani. A hanyarsa ta komawa ne ya rinka tunanin dole fa akwai abinda Zayyan ya barwa matarsa. Idan ba haka ba da me suke rayuwa duk tsahon lokacin nan? Yafi karfin ita da kwadayayyen babanta suyi masa wayau akan hakkinsa.
Yana zuwa dakin da Malamijo yayi masauki ya shiga. A shirye suke suna jiran dawowar Mairama.
"Dama nazo akan yaran nan ne Radhiya da Zayyan. Nace ko zaka yiwa Mairama magana idan ta yaye shi zan zo na dawo dasu gabanmu saboda gatansu dai bai wuce wurin dangin mahaifinsu. Idan kun tafi yanzu kai ma nauyi ne kawai zai kara hawa kanka. Sannan bazan zuba ido bane tayi aure 'ya'yana su koma agolanci a gidan wani"
Malamijo an tabo inda yake masa kaikayi kuwa. Ina zai kai karin bakuna uku a gidansa. Gara Mairama yana son abarsa, amma yaran nan da aka ha'ince shi yayi ta yiwa babansu kallon kitse ashe rogo ne "indai wannan ne babu damuwa. Zanyi magana da ita kuma dole ta amince don nima bazan so suyi rayuwar agolanci ba azo ana wulakantasu"
Maikudi ya fita da wani mugun murmushi. Soro ya koma ya zauna jiranta. Ilai kuwa babu jimawa sai gata tana ta sauri kada a gaji da jiranta. Dukawa ta danyi ta gaishe shi ya yafito ta da hannu.
"Yaki zo Mairama. Magana nake son yi da ke"
Kanta a kasa ya fada mata yadda ya fadawa Malamijo. Ai tuni ta saka kuka iya karfinta tana rokansa ya rufa mata asiri ita bata da niyar sake aure.
"Kinga da har mun gama magana da babanki"
Gabanta ne ya fadi. Ta san halin Malamijo kuma tas zai bada yaran nata.
"Don Allah kayi hakuri"
"Naji, amma bazaki bar garin nan ba sai kin fito da dukiyar kanina. Dole ne a raba gadonsa saboda a sauke masa nauyi"
Hannunta yana rawa ta zaro envelop dinnan daga jakarta ya warce gabadaya. Sakar masa tayi kafin ya hada da hannunta.
"Daren jiya na gansu shine nace dama yanzu zan fito dasu ayi abinda ya kamata"
Kankance idanu yayi yana kallonta bayan ya zaro takardun gidan da kuma damin kudi da aka nannade da kyauro "ashe ke mutuniyar banza ce ban sani ba? Wato da guduwa zakiyi da komai saboda tsabar mugunta da bakin hali kamar na tsohonki"
Ta shiga girgiza kai tana hawaye "a'a wallahi"
Wasikarta ta hango ta fadi ta mika hannu ya taketa da sauri da kafa "meye a ciki?"
Hankalinta yayi matukar tashi "wallahi Allah wasika ce ya bar min. Ba takardar komai bace"
Sai ta ga yayi murmushi saboda ya fuskanci yadda ta rude "soyayya manya" yatsansa ya kada mata "kalli nan, zan cire takardun gidan saboda dama ina binsa bashi da bai biya ba. Ina jin gidan ma bazai isa ya biyani ba amma dai su kadai zan dauka. Muje ciki idan munafukan dattijan nan sun zo ki basu kudin a rabawa wanda aka ga damar bawa. Ni kuma nayi miki alkawarin babu wanda ya isa ya rabaki da 'ya'yanki kuma zaki koma Kano da wasikar masoyinki"
Mairama kallon mugunta irin ta Maikudi ta tsaya yi ta rasa shawarar yankewa. A zatonta zaa raba gado a barwa yaranta gidan sai su zauna a ciki. Ita kuma a cikin kudin ta nemi abinyi domin kula dasu. Wani hawaye ke bin kuncinta tana jin zafinsu har zuciyarta "hakan yayi maka?"
Ya dage gira "yayi...ki sani idan kina tunanin juya magana ko Jume tayi kadan tasa na bar miki yaran nan balle kuma wancan tsohon Mal. Aminu. Mahaifinki kuma a yadda na fahimta ko sadakarki na nema zai iya hada min"
Share idanunta tayi tabi bayansa. Kowa yayi zaton kukan tafiya ne take yi da mutuwar mijinta. Su Mal.Aminu sun zo ta dauko kudi ta mika masa. A take aka kira wani malami ya kasafta da aukinsu kuwa aka bata nata aka ware na yaran yace batun bashi fa Mairama tace ya tabbatar mata babu msi binsa komai kafin ya tafi. Maikudi ko tari baiyi ba ganin babu mai gadon nashi sai su kadai. Jume har dadi taji yayi hankali.
Nasiha da ban hakuri aka sake yiwa juna sannan Mal.Aminu ya roki alfarmar kada ta tafi ta yanke zumunci dasu albarkarcin 'ya'ya "mu kuma nan babban kalubale ne a garemu mu da gwamnati. Mu dubi marayun yaran nan da mahaifiyarsu kafin mu ga me Allah Ya tsara musu. Haka ma gwamnatin ta dubi rayuwar sojojin da take takama da sadaukarwarsu. A dubi masu ran wanda suke a bakin aiki, a dubi masu rauni da nakasa sannan a dubi iyalan mamatan domin a gaskiya akwai nakasu mai girma a rayuwar iyalan bayin Allahn nan"
Sun fara fitowa mata ana ta kuka Maikudi ya samu ya tarar da Malamijo shi kadai iska tana ta kada yalolon yadin jikinsa yana manne masa ramar tana kara nunawa. Takardun gidan ya nuna masa yana murmushin samun nasara.
"Naga ka kawo idanu ka dora akan dukiyar da baka da alaka da taruwarta shine nace bari dai na nuna maka waye Maikudi."
Ware ido Malamijo yayi ya karewa takardun kallo "na meye?"
"Na gidan Zayyan ne wanda yanzu ya zama nawa. Kana iya kaini kotu don a kwatarwa 'yarka da jikoki hakkinsu amma ka sani kana yin hakan zan rabata da yaran nan ni kuma. Ta fada min akan ta baka dukiyarta gara kowa ya rasa don baka ragawa kowa akan kudi"
Kallon Mairama yayi zuciyarsa tana tafarfasa. Wato Zayyan yana da gida shine ta dauka ta bawa wan mijinta tana tunanin zata dawo masa gida ta jabe ya ciyar dasu. Lallai Mairama bata gama saninsa bane shiyasa har taje tana tona masa asiri. Har shi zata ha'inta yana mahaifinta. Kwafa yayi yana jiran su kebe don bashi da bukatar magana a gaban mutanen da ya kula bakinsu duka daya.
Maikudi kuwa dariya yayi bayan ya tafi. Alamun Malamijo da ya gani ne yasa shi wannan magana sai gashi tazo daidai da halin nasa. Mairama da Zayyan ma ta kasa tonawa mahaifinta asiri a gabansa me zai kaita fada a gaban Maikudi?
Radhiya ta dauka Hajjo ta goya Zayyan suka tafi tashar da zasu sami motar Kano. Sai da suka dau hanya don Salisu ya biya su kadai ne a ciki Mairama tana hawayenta Nene Marka na bata baki kawai Malamijo ya soma fada akan bayar da takardun gida da tayi. Kai, ita kam da me zata ji ne a rayuwarta. Tana kuka tayi musu bayanin yadda abin ya kasance.
"Ko dai mu koma ne a karbo takardun? Duk tsiyarsa baifi karfin hukuma ba fa Mairama" Salisu yace nasa ran a bace.
Tsorata tayi "don Allah ku kyale shi. Yaran nan zai karbe, babansu ma baiji dadin zama dashi ba"
Nene tace "Duk da haka Mairama mu zamu tsaya miki. Gidan a ina yake?"
"A Kano ne"
Salisu ya tabo dreban "Malam don Allah kayi hakuri ko zamu koma"
"Babu inda zamu je. Idan kuma sai kun koma to ni a ajiyeni a nan."
Nene Marka tace "haba Malamijo meye hakan?"
Rufe idanu yayi yana ta fada don sosai yaji haushin maganar Maikudi da rasa gidan da yayi. Ace 'yarsa da yafi so da tausayi a cikin 'ya'yansa ita ce tayi masa haka.
"Ina nan kan baka na bazan koma ba sannan kuma ki shirya tunda dangin miji sunfi uba ni bazan dauki nauyin kowa ba. Gida dai gaki gashi kuje a baku daki. Sai yanzu na raina waye Zayyanun ma. Har me yayi miki wanda ni ban miki dubunsa ba. Ji gidan da ya ajiyeki...."
Ta daure matuka amma bata jin zata taba jurewa wani ko da kuwa Malamijo ne ya zagi Zayyan. Ko bata aure shi ba yanzu ta san daraja da kimar soja....wallahi yafi karfin raini.
"Yayi min komai Malamijo" tace cikin kuka tana rungume Nene iya karfinta har Radhiya sai da ta tsorata "ko a kango muka zauna dashi har abada bani da tamkarsa. Wayyo ni ashe haka mutuwa take da daci da tona asiri? Lokacin da nayi maraicin uwa bansan ciwon rashi ba saboda bamu saba ba. Allah Ka jikan Zayyan ko Ka dauki raina nima na huta"
Zubar hawayenta ya taba Malamijo bare da ya ga ta rike kirjinta da yake mata mugun zafi. Dreban yace wa su juya ta dago rinannun jajayen idanunta.
"Allah Ya kaimu masu gidan su girma zasu karbi abinsu da izinin Allah. Amma a yanzu tunda yace yaji ya gani zai ci haram bazan shiga tsakaninsu ba"