Sashe 128
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Banda ceto rayuwarmu da yayi kudin da gwamnatin tarayya ta bashi a matsayin diyyar wahalar da yasha wallahi yake ta bin mutane da alheri. Nasan ana cewa ka haifi mutum baka haifi halinshi ba amma ina kyautata zato akan cewa Radhiya a cikin namu dangin alkhairi ce. Ban taba kin Awwab da Ghazalatu ba. Duk abinda nayi nayi shi ne domin kulawa da bayan wanda ya sadaukar da rayuwarsa dominmu. Nasan gabadaya rigimar nan ta samo asali ne akan auren da na nema masa saboda haka ina mai rokonku da ku yafe min"
Kowa yace ya yafe duk da ba laifi yayi ba. Hasali ma yayi abin yabawa ne sosai saboda bai kasance mai manta alkhairi ba.
A hankali hira ta barke a tsakanin 'yan uwan inda su Zahra sosai suke jin zafin Nura da abinda ya yiwa Ghazalatu. Ana haka ta hango Awwab a kan kujera can gefe a cikin falon yayi nesa dasu. Murmushi tayi ta karasa inda yake wata sabuwar wutar sonsa tana ruri a zuciyarta. Chatting yake da Radhiya yana ta murmushi ta zo ta zauna a kujerar gefensa.
"Ango kasha kamshi" tace tana rausayar da kai da murmushi.
Hankalinsa na kan wayar yana yiwa Radhiya reply yace "Kamshi sai mata"
Murya ta karyar alamun kuka take shirin yi "kaji irin zaman da muka yi da Nura ko?"
Wayar yasa a aljihu ya maida hankali gareta "naji Ghazalatu sai dai ince kiyi hakuri komai mukaddari ne."
Gwauron numfashi ta sauke tana tararrabin abinda za ta fada. Hannu ta ga ya mayar zai dauko wayar tayi saurin cewa "Yanzu shikenan tsakaninmu Ya Awwab?"
Karo na biyu ya kuma mayar da wayar "ban fahimceki ba"
Sunkuyar da kai tayi kafin ta bashi amsa "nasan cewa ban kyauta ba amma kayi hakuri idan da hali zan jiraka"
Ya fara gane me take son cewa sai dai baya son zumuncin da ake kokarin fardadowa dashi ya kuma sake sumewa a dalilinsa "Ghazalatu mun riga mun wuce wannan matakin. I am happily married matata ko tarewa bata yi ba so please kada ma mu komawa abinda ya wuce"
Hawaye ne ya zubo mata "yanzu baka tausayin halin da na shiga? Ban taba cireka daga zuciyata ba kuma a shirye nake na zauna da kai ko a ta biyun ne"
Ransa yaji ya soma baci amma baya son janyo hankalin kowa garesu "Allah zai baki wanda ya fini amma bani da niyar mata biyu yanzu"
Wani irin murmushi tayi "wato nice baka so wancan lokacin shiyasa har ka iya amincewa wata kuma ka fada da bakinka kana sonta ba wai don Daddy Mustapha ya nema maka aurenta ba"
"Wai ni Ghazalatu Nura ya sakeki ne kike min wannan zancen?"
Da murnarta ta amsa "ya hakura yayi min saki daya"
"Idan dai ba lissafina ya baci ba ina tunanin har yanzu kina cikin kwanakin iddah ko"
"Nasan da wannan amma bazai hana na fada maka abinda yake raina ba"
Neman abinda zai fada mata yake yi wayar Radhiya ta shigo. Yana dauka ta soma kukan shagwaba wai baiyi mata reply ba. Dama hirar tafiya honeymoon suke yi ya bata zabin kasashe uku yace ta zabi daya shine ta tura masa inda take so bai duba ba.
Hakuri ya soma bata Ghazalatu sai ta daga murya tana cewa wai yace gata zasu gaisa. Gudun kada ta zargi wani abu tunda ta riga taji muryar mace a wurin yace mata ga Ghazalatu zasu gaisa.
Mika mata wayar yayi ta koma kan kujera ta zauna tana magana a gayance kamar bata so "amaryarmu ko ince uwargida sarautar mata yaya shirye shiryen biki?"
Zuciyar Radhiya har ta fara tafasa da kishi musamman saboda yanayin yadda Ghazalatu ke fitar da harufa daki daki tana wani yauki.
"Lafiya kalau" ta daure tace.
"To ga amanar Yayana nan dai ki kula mana dashi sosai...idan kina bukatar shawarwari game da hanyoyin sace zuciyarsa ki karbi numberta a wurinsa." Wata shu'umar dariya tayi "kinsan na karance shi kamar tafin hannuna"
"Abinda ba'a sani ba ake karantawa, ni da Hammana kuwa warin takalmi ne komai namu iri daya....how do I put it?" Radhiya tace muryarta na fita cikin nutsuwa. Dariya tayi a hankali saboda samo kalmar da ta dace ta fada "Alheran is the female version of Awwab...amma duk da haka nagode da tayin da kika yi min"
Awwab tsabar mamakin abinda Ghazalatu tace kasa yi mata magana yayi sai jinjina kai yake da halin mata. Kallonsa tayi ta saki murmushi duk da ranta in yayi dubu ya baci da amaar Radhiya amma ai ba'a fara komai ba ma "Ga angon namu.....Yayana sauran maganar tamu fa?"
Fizgar wayarsa yayi ransa a hade ta sake maimaita tambayar da dan karfi yace zasu karasa daga baya. Da sauri ya saka wayar a kunne yana cewa hello Radhiya ta katse kiran. Yasan za'a rina sai dai yana sake kira yaji ta kashe wayar gabadaya.
***********
Ko sati ba'ayi ba da taji Mami tana fadawa su Ummi matsalar gidan Ghazalatu da mutuwar auren shine daga zuwansa Katsina yau zasu tada tsohuwar soyayya. Allah Ya bada sa'a tace a zuci ranta yana kuna tayi jifa da wayar ta kifa kai tana kuka.
Kamar wasa ta kwashe yafi awa guda tana zubar da hawaye. A haka Rahima tazo ta sameta sai dai bata ga fuskar ba tayi zaton bacci kawai take yi. Awwab tun yana daukar abin wasa har ya fuskanci fushin nata na gaske ne. Bai san sau nawa yana gwada wayarta ba amma duk kira a kashe. Gashi layi daya gareta bare ya nemi wani. A ranar su biyun da kyar suka yi bacci saboda tunani. Asubar fari yana dawowa daga masallaci ya sake gwadawa nan ma shiru har bayan azahar. Bashi da kwanciyar hankali lokacin kana kallonsa za ka gane akwai abinda ke damunsa. Mami tana ta yi masa magana akan cewa su Umma da sauran matan kakanin sun ce lallai idan an dauko Radhiya daga Sakkwato nan Katsina za'a kawota ayi budar kai kafin su wuce Nijar.
Sama-sama yake jin muryar Zahra tana cewa gaskiya tana tausayin Radhiyan saboda zasu sha yawo. Wayarsa a hannu yana yi mata text bai amsa ba Mami ta kira shi da dan karfi "wai meye yake damunka ne ana magana ka kasa amsawa? Ka ji abinda nake fada ma kuwa?"
Saurin kallonta yayi "Mami naji, gajiya ce dai kowa sai yayi a tanadi maganin ciwon jiki kawai"
Murmushi tayi tana cigaba da fadawa Zahra ta rubuta abubuwan bukata na walimar da za suyi ranar budar kan "tunda wahalar saboda ku ne ai kai ya dace ka siyo mana maganin"
Murmushi kawai yayi ya tashi kamar jira suke Mami da Zahra su ka tambayi juna me yake damunsa ne.
Kasa hakuri yayi ya kira Ummi saboda ba karamin kewar Radhiya yake yi ba ga damuwa tunda yasan fushi take yi dashi. Lokutan da ya sami damar kasancewa da ita kadai idan ya tuna sai yaji kamar ya budi ido ya ganshi tare da ita. Sun gaisa da Ummi lafiya kalau yadda su ka saba ya rasa da yadda zai nemi Radhiya. Ita da kanta ta fuskanci me yake damunsa.
"Awwab kaima ka kira kanwarka baka samu ko?"
Da sauri yace "eh"
Murmushi tayi "Jiya Karami sai da ya kirani na hadasu, dazu ma ya sake cewa na bata su gaisa wai ya kirata shiru kuma bata kira shi ba. Ban san me yake damunta ba sai aikin kwanciya...."
Rahima ta bawa wayar ta kai mata. Har ta mika hannu tana tambayarta ko Emzee ne Rahima tace ba shi bane. Tunda taji haka tasan ko waye sai cewa tayi ta mayarwa da Ummi wayarta yanzu za ta kunna tata ta kira shi. Awwab yana jin duk abinda tace kamar yayi ihu saboda yadda ya matsu ta amsa masa taki.
Fitar Rahiman ke da wuya ta sake fashewa da wani kukan ko abinci ta kasa ci sai tunanin yana can suna soyayya da Ghazalatu.
Zuwa dare jikinta yayi mugun zafi da ciwon kai saboda ita dama ba mutum bace mai sa abu a rai. Wannan karon da tayi shiru sai yake neman yi mata illa. Ummi ta gaji da wannan zaman daki da tsura da ga jiya zuwa yau take tambayar Aishatou mai gyaran jiki ko ta ga wani chanji game da ita.
"Shiru shirun da take yi ne ke damuna dai Ummin Radhiya. Kuma kamar kuka tayi ma shiyasa jiya da yau aikin namu bamu dade ba. Ina jin fargabar aure ce ta fara taba ta. Kinsan fa ance aure yakin mata"
Ummi ta soma dariya "yakin matan zamaninmu ko, yanzu budurwa ko ita ce ta hudu banda rawar kai me su ka sani"
Hira suke abinsu akan bambancin matan da da na yanzu Mami ta kira suke zancen walimar da dole yanzu sai tayi a Katsina. Ummi ma tace dalilin da yasa ta kira dazu kenan Malamijo yace kafin su fara bikinsu a kawo masa jikarsa suyi nasu taron tunda ya kula wannan bikin ba na zama bane yawo za'ayi ta yi.
"Yaran nan zasu wahala musamman Radhiya da take mace ko dai mu matso da bikin kada mu cure komai cikin sati guda muzo ana 'ya kwance uwa kwance" inji Mami.
"Ke da 'yarki ne zaku kwanta ni kam garau zaku ganni don ko suyar albasa bazan tayaku dashi ba" Ummi ta bata amsa da dariya.
"Kyale wannan 'yar rabona da ita tun jiya"
Sai yanzu Ummi ta fara damuwa "Mami bari na dubo yarinyar nan. Jiya da yau a daki ta wuni muna cewa ko fargabar aure ne amma dai bari na duba" tace tana hawa sama zuwa dakin Radhiya.
Bata ajiye wayar ba ta shiga ta same kwance a kasa ta rike kai da hannu biyu. Da sauri ta durkusa a gabanta tana dora hannu a kan goshinta da yayi zafi ga idanu a kumbure anci kuka an gode Allah.
"Ke me ya sameki?" Ummi tace a tsorace tana ajiye wayar a gefe. Tayar da ita tayi ta koma kan gado.
"Kaina zai tsage Ummi" tace a wahale.
Kowa yace ya yafe duk da ba laifi yayi ba. Hasali ma yayi abin yabawa ne sosai saboda bai kasance mai manta alkhairi ba.
A hankali hira ta barke a tsakanin 'yan uwan inda su Zahra sosai suke jin zafin Nura da abinda ya yiwa Ghazalatu. Ana haka ta hango Awwab a kan kujera can gefe a cikin falon yayi nesa dasu. Murmushi tayi ta karasa inda yake wata sabuwar wutar sonsa tana ruri a zuciyarta. Chatting yake da Radhiya yana ta murmushi ta zo ta zauna a kujerar gefensa.
"Ango kasha kamshi" tace tana rausayar da kai da murmushi.
Hankalinsa na kan wayar yana yiwa Radhiya reply yace "Kamshi sai mata"
Murya ta karyar alamun kuka take shirin yi "kaji irin zaman da muka yi da Nura ko?"
Wayar yasa a aljihu ya maida hankali gareta "naji Ghazalatu sai dai ince kiyi hakuri komai mukaddari ne."
Gwauron numfashi ta sauke tana tararrabin abinda za ta fada. Hannu ta ga ya mayar zai dauko wayar tayi saurin cewa "Yanzu shikenan tsakaninmu Ya Awwab?"
Karo na biyu ya kuma mayar da wayar "ban fahimceki ba"
Sunkuyar da kai tayi kafin ta bashi amsa "nasan cewa ban kyauta ba amma kayi hakuri idan da hali zan jiraka"
Ya fara gane me take son cewa sai dai baya son zumuncin da ake kokarin fardadowa dashi ya kuma sake sumewa a dalilinsa "Ghazalatu mun riga mun wuce wannan matakin. I am happily married matata ko tarewa bata yi ba so please kada ma mu komawa abinda ya wuce"
Hawaye ne ya zubo mata "yanzu baka tausayin halin da na shiga? Ban taba cireka daga zuciyata ba kuma a shirye nake na zauna da kai ko a ta biyun ne"
Ransa yaji ya soma baci amma baya son janyo hankalin kowa garesu "Allah zai baki wanda ya fini amma bani da niyar mata biyu yanzu"
Wani irin murmushi tayi "wato nice baka so wancan lokacin shiyasa har ka iya amincewa wata kuma ka fada da bakinka kana sonta ba wai don Daddy Mustapha ya nema maka aurenta ba"
"Wai ni Ghazalatu Nura ya sakeki ne kike min wannan zancen?"
Da murnarta ta amsa "ya hakura yayi min saki daya"
"Idan dai ba lissafina ya baci ba ina tunanin har yanzu kina cikin kwanakin iddah ko"
"Nasan da wannan amma bazai hana na fada maka abinda yake raina ba"
Neman abinda zai fada mata yake yi wayar Radhiya ta shigo. Yana dauka ta soma kukan shagwaba wai baiyi mata reply ba. Dama hirar tafiya honeymoon suke yi ya bata zabin kasashe uku yace ta zabi daya shine ta tura masa inda take so bai duba ba.
Hakuri ya soma bata Ghazalatu sai ta daga murya tana cewa wai yace gata zasu gaisa. Gudun kada ta zargi wani abu tunda ta riga taji muryar mace a wurin yace mata ga Ghazalatu zasu gaisa.
Mika mata wayar yayi ta koma kan kujera ta zauna tana magana a gayance kamar bata so "amaryarmu ko ince uwargida sarautar mata yaya shirye shiryen biki?"
Zuciyar Radhiya har ta fara tafasa da kishi musamman saboda yanayin yadda Ghazalatu ke fitar da harufa daki daki tana wani yauki.
"Lafiya kalau" ta daure tace.
"To ga amanar Yayana nan dai ki kula mana dashi sosai...idan kina bukatar shawarwari game da hanyoyin sace zuciyarsa ki karbi numberta a wurinsa." Wata shu'umar dariya tayi "kinsan na karance shi kamar tafin hannuna"
"Abinda ba'a sani ba ake karantawa, ni da Hammana kuwa warin takalmi ne komai namu iri daya....how do I put it?" Radhiya tace muryarta na fita cikin nutsuwa. Dariya tayi a hankali saboda samo kalmar da ta dace ta fada "Alheran is the female version of Awwab...amma duk da haka nagode da tayin da kika yi min"
Awwab tsabar mamakin abinda Ghazalatu tace kasa yi mata magana yayi sai jinjina kai yake da halin mata. Kallonsa tayi ta saki murmushi duk da ranta in yayi dubu ya baci da amaar Radhiya amma ai ba'a fara komai ba ma "Ga angon namu.....Yayana sauran maganar tamu fa?"
Fizgar wayarsa yayi ransa a hade ta sake maimaita tambayar da dan karfi yace zasu karasa daga baya. Da sauri ya saka wayar a kunne yana cewa hello Radhiya ta katse kiran. Yasan za'a rina sai dai yana sake kira yaji ta kashe wayar gabadaya.
***********
Ko sati ba'ayi ba da taji Mami tana fadawa su Ummi matsalar gidan Ghazalatu da mutuwar auren shine daga zuwansa Katsina yau zasu tada tsohuwar soyayya. Allah Ya bada sa'a tace a zuci ranta yana kuna tayi jifa da wayar ta kifa kai tana kuka.
Kamar wasa ta kwashe yafi awa guda tana zubar da hawaye. A haka Rahima tazo ta sameta sai dai bata ga fuskar ba tayi zaton bacci kawai take yi. Awwab tun yana daukar abin wasa har ya fuskanci fushin nata na gaske ne. Bai san sau nawa yana gwada wayarta ba amma duk kira a kashe. Gashi layi daya gareta bare ya nemi wani. A ranar su biyun da kyar suka yi bacci saboda tunani. Asubar fari yana dawowa daga masallaci ya sake gwadawa nan ma shiru har bayan azahar. Bashi da kwanciyar hankali lokacin kana kallonsa za ka gane akwai abinda ke damunsa. Mami tana ta yi masa magana akan cewa su Umma da sauran matan kakanin sun ce lallai idan an dauko Radhiya daga Sakkwato nan Katsina za'a kawota ayi budar kai kafin su wuce Nijar.
Sama-sama yake jin muryar Zahra tana cewa gaskiya tana tausayin Radhiyan saboda zasu sha yawo. Wayarsa a hannu yana yi mata text bai amsa ba Mami ta kira shi da dan karfi "wai meye yake damunka ne ana magana ka kasa amsawa? Ka ji abinda nake fada ma kuwa?"
Saurin kallonta yayi "Mami naji, gajiya ce dai kowa sai yayi a tanadi maganin ciwon jiki kawai"
Murmushi tayi tana cigaba da fadawa Zahra ta rubuta abubuwan bukata na walimar da za suyi ranar budar kan "tunda wahalar saboda ku ne ai kai ya dace ka siyo mana maganin"
Murmushi kawai yayi ya tashi kamar jira suke Mami da Zahra su ka tambayi juna me yake damunsa ne.
Kasa hakuri yayi ya kira Ummi saboda ba karamin kewar Radhiya yake yi ba ga damuwa tunda yasan fushi take yi dashi. Lokutan da ya sami damar kasancewa da ita kadai idan ya tuna sai yaji kamar ya budi ido ya ganshi tare da ita. Sun gaisa da Ummi lafiya kalau yadda su ka saba ya rasa da yadda zai nemi Radhiya. Ita da kanta ta fuskanci me yake damunsa.
"Awwab kaima ka kira kanwarka baka samu ko?"
Da sauri yace "eh"
Murmushi tayi "Jiya Karami sai da ya kirani na hadasu, dazu ma ya sake cewa na bata su gaisa wai ya kirata shiru kuma bata kira shi ba. Ban san me yake damunta ba sai aikin kwanciya...."
Rahima ta bawa wayar ta kai mata. Har ta mika hannu tana tambayarta ko Emzee ne Rahima tace ba shi bane. Tunda taji haka tasan ko waye sai cewa tayi ta mayarwa da Ummi wayarta yanzu za ta kunna tata ta kira shi. Awwab yana jin duk abinda tace kamar yayi ihu saboda yadda ya matsu ta amsa masa taki.
Fitar Rahiman ke da wuya ta sake fashewa da wani kukan ko abinci ta kasa ci sai tunanin yana can suna soyayya da Ghazalatu.
Zuwa dare jikinta yayi mugun zafi da ciwon kai saboda ita dama ba mutum bace mai sa abu a rai. Wannan karon da tayi shiru sai yake neman yi mata illa. Ummi ta gaji da wannan zaman daki da tsura da ga jiya zuwa yau take tambayar Aishatou mai gyaran jiki ko ta ga wani chanji game da ita.
"Shiru shirun da take yi ne ke damuna dai Ummin Radhiya. Kuma kamar kuka tayi ma shiyasa jiya da yau aikin namu bamu dade ba. Ina jin fargabar aure ce ta fara taba ta. Kinsan fa ance aure yakin mata"
Ummi ta soma dariya "yakin matan zamaninmu ko, yanzu budurwa ko ita ce ta hudu banda rawar kai me su ka sani"
Hira suke abinsu akan bambancin matan da da na yanzu Mami ta kira suke zancen walimar da dole yanzu sai tayi a Katsina. Ummi ma tace dalilin da yasa ta kira dazu kenan Malamijo yace kafin su fara bikinsu a kawo masa jikarsa suyi nasu taron tunda ya kula wannan bikin ba na zama bane yawo za'ayi ta yi.
"Yaran nan zasu wahala musamman Radhiya da take mace ko dai mu matso da bikin kada mu cure komai cikin sati guda muzo ana 'ya kwance uwa kwance" inji Mami.
"Ke da 'yarki ne zaku kwanta ni kam garau zaku ganni don ko suyar albasa bazan tayaku dashi ba" Ummi ta bata amsa da dariya.
"Kyale wannan 'yar rabona da ita tun jiya"
Sai yanzu Ummi ta fara damuwa "Mami bari na dubo yarinyar nan. Jiya da yau a daki ta wuni muna cewa ko fargabar aure ne amma dai bari na duba" tace tana hawa sama zuwa dakin Radhiya.
Bata ajiye wayar ba ta shiga ta same kwance a kasa ta rike kai da hannu biyu. Da sauri ta durkusa a gabanta tana dora hannu a kan goshinta da yayi zafi ga idanu a kumbure anci kuka an gode Allah.
"Ke me ya sameki?" Ummi tace a tsorace tana ajiye wayar a gefe. Tayar da ita tayi ta koma kan gado.
"Kaina zai tsage Ummi" tace a wahale.