Sashe 114
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Taro ya burge matuka Zayyan ya sami alkhairi fiye da zato da tsammani. Supervisor din Radhiya tazo ta rungumeta su ma sunji dadi domin kuwa a take wani da minister of information ya tura musu ya bukaci su cigaba da bata duk wani training da zai taimaka mata domin su tababbatar da bunkasar wannan shiri.
Sun fito tafiya Arifah tayi gefe ashe mukullin motarta zata karba da tasa dreba ya kawo mata. Yousuf yazo ya shige ya zauna bayan ya radawa Awwab cewa gida kawai zai rakata sai ya dawo.
"Kuma an fada maka zan yarda da wannan zancen ne" yace yana dariya.
Yousuf ya rage murya yana dariya shima "ni dai ko yaya sai na tabbatarwa Arifah ni mijinta ne yau...kada ka rufe min kofa rakiya ce kawai zanyi"
Kusan kowa ya fito ana ta shiga mota. Awwab na kallon Radhiya ta shige motar da suka zo. Wadda ya tuko ya shiga kai tsaye gidan Daada yabi bayansu Bilal yana tambayarsa ina zasu je kuma yace "rakiya zanyi na dawo". Daga bakin gate ya cillawa Bilal key din motar yace shima kada a rufe masa kofa sai ya dawo.
Raji dariya kamar me sun dago angwayen hakurinsu ya kare ne. To su din ma ciki suka shige kowanne ya kira matarsa.
Tana hawa bene a gajiye taji wayar Awwab saboda kidansa daban ne. Da sauri ta dauka ga kuma kunyarsa da take ji.
"Kina ina?"
"Yanzu muka shigo gida"
"Yunwa nake ji Schatzi" taji yace harda marairaicewa.
"Ka karasa gida ne?"
"Na biyo matata ta bani"
Saukowa tayi da sauri tana fita suna karo ya riko hannunta ya ja ta gefe sai da ya gama dube dubensa ya turata wani karamin falo wanda kujeru ne kadai a ciki sai tutar Nigeria a tsaye. Faduwa gabanta yayi da ya tura kofar da kafarsa ya rinka taku a hankali zuwa gabanta. Kasa dago kai tayi sai dai ba shiri ta daga din sakamakon daukan da Awwab yayi mata.
Dagota yayi ta hanyar saka hannuwa daga kasanta yayi sama da ita dole ta saka hannuwanta ta riko wuyansa domin kada ta fadi. Idanunsu cikin na juna ya soma juyi da ita yana dariya itama sai da tayi saboda yadda yake yi mata.
"Nice to meet you Mrs Awwab" yace lokacin da ya direta a gabansa.
Kunyar ce ta motsa saboda yadda ya tsareta da idanu ta kasa magana sai ma juyawa da taso yi ta fita. Hannunta kawai ya janyo ta fado jikinsa ya rungumeta sosai. A tare suke sauke numfashi da ajiyar zuciya yau burinsu ya cika. Kanta yana kirjinsa ya saka hannuwa a bayanta ita kuma nata suna ta wurin cikinsa ya soma magana cikin wani irin salo da shaukin soyayya.
"Alheran don Allah kada mu taba bari fushi ko wata zugar mutane su shiga tsakaninmu. Nasan ni dake are not perfect but we complete each other. Kece zabin Awwab tun kin baby har ranar da zai dena numfashi in sha Allah"
Kalamansa sun kara masa matsayi da kima a idanunta. Batare da ta dago kanta ba ta yi magana don tsokana "har lokacin da aka yi min aski?"
Murmushi yayi "tashinki daga baccin nan da kallon da kika yi min shine lokacin da Awwab ya fara yiwa Alheran soyayyar da yake fatan ta kare a aure"
Murmushin da tayi ne ya janyo shigewar dimple dinta ciki sosai. Abinda Awwab ya dade yana jiran damar yi sai ji tayi ya dora lips dinsa a wurin yayi kissing dinta. Kunya har sai da taji cikinta yana wata irin yamutsewa shi kuwa bai tsaya ba sai pin din da tayi rolling dashi yabi ya zaresu ya zame mayafin. Kansa ya kai gaban goshinta yana shafa gashinta da yake kulle cikin ribbon tayi packing dinsa a tsakiyar kanta ya kuma bata wani kiss din.
Da wata irin murya yace "rufe idanunki"
Ki tayi sai dai suna hada ido ta runtse nata da sauri saboda bata da kuzarin cigaba da kallon idanunsa. Tana ji yana dan motsi amma bata bude ba taji ya saka hannu ya zame mata ribbon ya cusa yatsunsa cikin gashinta ya sake matso da ita. Bakinsa ya hade da nata a nutse ya jefa mata sweet din bakinsa irin wadda suka taba sha a soron Malamijo. Bata san lokacin da ta bude idanuwanta ba saboda ta gane dandanon alawar. A haka suka sha ta kusa rabi sannan ya bar mata a bakinta ya sake janyota jikinsa.
"Ina jindadi idan muna sharing abu...nafi son ko me naci babyna ma taci. I hope daga yau haka zamu koma yi...it is better than daya ya ragewa daya"
Duk da bakon yanayin da take ji sai da ta tsokane shi "harda abinci ko?"
"Ewww ke fa kazama ce" yana bata fuska da tunanin a tauna abinci daga baki.
Dariya tasa "kaga tuwo zaiyi dadi...."
"Fita, fita ki tafi dirty girl" yace yana nuna mata kofa tare da dora mata mayafinta a ka.
Turjewa tayi "nama fa?"
"Out" ya kuma cewa yana bata fuska ya dago hannu ya biyota ta kara gaba da sauri. Tana bude kofar ya janyota ya rungumeta ta baya kansa na kafadarta "babu abinda zai fito daga bakinki na kyamace shi Schatzi. Idan kin ga dama har kunu musha a haka"
Ita ya bari da bata fuska "shhhh please Hammana dena fada"
"Ko kosai shima zaiyi dadi"
Yatsunta tasa ta toshe kunnuwanta ya sake matseta "juyo kiji last one din"
Kafada ta noke ya juyo da ita da kansa "I love yo baby"
A hankali ta dago kai ta kalle shi idanunta sun kara girma da haske tace "I love you Chèri" tare da shammatarsa ta fice da sauri.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Ita da Arifah suma nasu shirin suka fara inda da sahalewar angwayen nasu suka amince a hada dinner a Abuja bayan kowacce anyi mata nata bikin na gida. Arifah a Jos za'ayi wasu events din bikin 'yar gwamna guda daya tilo ita kuma Radhiya sai da aka yi ta tunanin inda yafi dacewa karshe Mama tace ayi a Abuja amma yini a Sakkwato za'ayi kamar yadda za'ayiwa Arifah a Jos. Ranar kai amarya kowacce a daukota daga garin mahaifinta washegari suyi dinner dinsu. Daga nan kuma tsugunne bata kare ba domin Tante tana can Nijar da sauran 'yan uwa ana shirin bikin 'ya'yanta Yousuf da Radhiya saboda haka ana wannan dinner din can zasu wuce ayi sabon biki sannan amaren su tare. Dama kuma Tante din ta riga ta sanar dasu Ummi kada a dauko wata mai gyaran jiki zata taho da kawarta tun suna 'yan mata idan sun zo taron Zayyan zata barta a nan. Arifah daga Nijar zasu wuce France shi kuma Awwab ya riga yasa an fara nemawa Radhiya visar Germany can zai tafi da ita suyi sati biyu su dawo Nigeria.
Tun yanzu kowa jiki ya fara fada masa saboda shirye shirye. Ana ta kai dinkunan biki na amarya , 'yan uwanta da iyaye. Zahra da Raji sun dawo daga Katsina sai hutu ya kara daga wurin aiki amma fa idan ya koma shekarar kaf bashi da hutu. Fauziyya itama sauki ya samu sun koma Katsina sai daurin auren Bilal zai taho da ita.
SANNU SANNU BATA HANA ZUWA
Saura kwana uku daurin auren Arifah hakan na nufi kwanaki hudu ya rage na Radhiya amma har yanzu Awwab bai dawo ba sai bata hakuri yake yi al'amura sun zo ba yadda yayi zato ba. Radhiya tun tana daurewa sai da tayi masa kuka da daddare akan bata fatan a daura auren baya nan. Hakuri ya bata domin wani training aka saka yake jagoranta. Ainihi bashi bane da tuni ma ya dawo gida sai matar wanda zaiyi ta haihu sati biyar kafin ainihin lokacin haihuwarta. Abu yazo da tangarda dole ya dauki hutu. Gashi daga shi sai Awwab ne suka yi wannan course din a Ukraine. Tunda sunsan aure zaiyi shine aka daga masa kafa zai taho ana gobe daurin auren Yousuf.
Ga abu ya dame shi ga fushin Alheran dinsa sannan Mami da Daddy sun kira shi a lokuta mabambanta kowanne baisan dayan ya kira ba suna jaddada masa idan ya bari aka daura aure babu shi zai ga fushinsu.
Ya gama shirinsa tsaf ranar da zai taho ana gobe daurin auren su Arifah yayi ta kiran Radhiya taki dauka tana ta kunkuni. Text yayi mata mai dauke da dadadan kalamai ya sanar da ita yana hanya zai sauka shadayan dare. Bata yi masa reply ba sai sai kowa ya ga sauyi da walwalarta da ta karu. Tante ta fadawa ya taho tace to maza ta tanadar masa abinci a kai gidan Mami. Yousuf da suka zo da sauran mutanen Nijar shi acan yayi masauki dakin Awwab tare da Raji. Gidan Major General Zayyan kuwa babu masaka tsinke saboda 'yan uwansa na Nijar iyaye su Alh Sidi da Alh Ghoumar. Alh Mousa dai da mijin Mammee da sauran tawagarsu hotel aka kama musu. 'Yan uwa ne aka taru ko ta ina. Emzee ma ya da safe ya iso sai dai gidan Mama ya wuce kai tsaye ga mamakinsa Halifa ma ya riga shi zuwa suna tare da Ibrahim. Sakin fuska yayi kamar babu komai a ransa ya rungumi dan uwansa sai dai har ransa yana jin babu dadi da kuma hangen me zai faru idan gaskiya tayi halinta.
Sun fito tafiya Arifah tayi gefe ashe mukullin motarta zata karba da tasa dreba ya kawo mata. Yousuf yazo ya shige ya zauna bayan ya radawa Awwab cewa gida kawai zai rakata sai ya dawo.
"Kuma an fada maka zan yarda da wannan zancen ne" yace yana dariya.
Yousuf ya rage murya yana dariya shima "ni dai ko yaya sai na tabbatarwa Arifah ni mijinta ne yau...kada ka rufe min kofa rakiya ce kawai zanyi"
Kusan kowa ya fito ana ta shiga mota. Awwab na kallon Radhiya ta shige motar da suka zo. Wadda ya tuko ya shiga kai tsaye gidan Daada yabi bayansu Bilal yana tambayarsa ina zasu je kuma yace "rakiya zanyi na dawo". Daga bakin gate ya cillawa Bilal key din motar yace shima kada a rufe masa kofa sai ya dawo.
Raji dariya kamar me sun dago angwayen hakurinsu ya kare ne. To su din ma ciki suka shige kowanne ya kira matarsa.
Tana hawa bene a gajiye taji wayar Awwab saboda kidansa daban ne. Da sauri ta dauka ga kuma kunyarsa da take ji.
"Kina ina?"
"Yanzu muka shigo gida"
"Yunwa nake ji Schatzi" taji yace harda marairaicewa.
"Ka karasa gida ne?"
"Na biyo matata ta bani"
Saukowa tayi da sauri tana fita suna karo ya riko hannunta ya ja ta gefe sai da ya gama dube dubensa ya turata wani karamin falo wanda kujeru ne kadai a ciki sai tutar Nigeria a tsaye. Faduwa gabanta yayi da ya tura kofar da kafarsa ya rinka taku a hankali zuwa gabanta. Kasa dago kai tayi sai dai ba shiri ta daga din sakamakon daukan da Awwab yayi mata.
Dagota yayi ta hanyar saka hannuwa daga kasanta yayi sama da ita dole ta saka hannuwanta ta riko wuyansa domin kada ta fadi. Idanunsu cikin na juna ya soma juyi da ita yana dariya itama sai da tayi saboda yadda yake yi mata.
"Nice to meet you Mrs Awwab" yace lokacin da ya direta a gabansa.
Kunyar ce ta motsa saboda yadda ya tsareta da idanu ta kasa magana sai ma juyawa da taso yi ta fita. Hannunta kawai ya janyo ta fado jikinsa ya rungumeta sosai. A tare suke sauke numfashi da ajiyar zuciya yau burinsu ya cika. Kanta yana kirjinsa ya saka hannuwa a bayanta ita kuma nata suna ta wurin cikinsa ya soma magana cikin wani irin salo da shaukin soyayya.
"Alheran don Allah kada mu taba bari fushi ko wata zugar mutane su shiga tsakaninmu. Nasan ni dake are not perfect but we complete each other. Kece zabin Awwab tun kin baby har ranar da zai dena numfashi in sha Allah"
Kalamansa sun kara masa matsayi da kima a idanunta. Batare da ta dago kanta ba ta yi magana don tsokana "har lokacin da aka yi min aski?"
Murmushi yayi "tashinki daga baccin nan da kallon da kika yi min shine lokacin da Awwab ya fara yiwa Alheran soyayyar da yake fatan ta kare a aure"
Murmushin da tayi ne ya janyo shigewar dimple dinta ciki sosai. Abinda Awwab ya dade yana jiran damar yi sai ji tayi ya dora lips dinsa a wurin yayi kissing dinta. Kunya har sai da taji cikinta yana wata irin yamutsewa shi kuwa bai tsaya ba sai pin din da tayi rolling dashi yabi ya zaresu ya zame mayafin. Kansa ya kai gaban goshinta yana shafa gashinta da yake kulle cikin ribbon tayi packing dinsa a tsakiyar kanta ya kuma bata wani kiss din.
Da wata irin murya yace "rufe idanunki"
Ki tayi sai dai suna hada ido ta runtse nata da sauri saboda bata da kuzarin cigaba da kallon idanunsa. Tana ji yana dan motsi amma bata bude ba taji ya saka hannu ya zame mata ribbon ya cusa yatsunsa cikin gashinta ya sake matso da ita. Bakinsa ya hade da nata a nutse ya jefa mata sweet din bakinsa irin wadda suka taba sha a soron Malamijo. Bata san lokacin da ta bude idanuwanta ba saboda ta gane dandanon alawar. A haka suka sha ta kusa rabi sannan ya bar mata a bakinta ya sake janyota jikinsa.
"Ina jindadi idan muna sharing abu...nafi son ko me naci babyna ma taci. I hope daga yau haka zamu koma yi...it is better than daya ya ragewa daya"
Duk da bakon yanayin da take ji sai da ta tsokane shi "harda abinci ko?"
"Ewww ke fa kazama ce" yana bata fuska da tunanin a tauna abinci daga baki.
Dariya tasa "kaga tuwo zaiyi dadi...."
"Fita, fita ki tafi dirty girl" yace yana nuna mata kofa tare da dora mata mayafinta a ka.
Turjewa tayi "nama fa?"
"Out" ya kuma cewa yana bata fuska ya dago hannu ya biyota ta kara gaba da sauri. Tana bude kofar ya janyota ya rungumeta ta baya kansa na kafadarta "babu abinda zai fito daga bakinki na kyamace shi Schatzi. Idan kin ga dama har kunu musha a haka"
Ita ya bari da bata fuska "shhhh please Hammana dena fada"
"Ko kosai shima zaiyi dadi"
Yatsunta tasa ta toshe kunnuwanta ya sake matseta "juyo kiji last one din"
Kafada ta noke ya juyo da ita da kansa "I love yo baby"
A hankali ta dago kai ta kalle shi idanunta sun kara girma da haske tace "I love you Chèri" tare da shammatarsa ta fice da sauri.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Ita da Arifah suma nasu shirin suka fara inda da sahalewar angwayen nasu suka amince a hada dinner a Abuja bayan kowacce anyi mata nata bikin na gida. Arifah a Jos za'ayi wasu events din bikin 'yar gwamna guda daya tilo ita kuma Radhiya sai da aka yi ta tunanin inda yafi dacewa karshe Mama tace ayi a Abuja amma yini a Sakkwato za'ayi kamar yadda za'ayiwa Arifah a Jos. Ranar kai amarya kowacce a daukota daga garin mahaifinta washegari suyi dinner dinsu. Daga nan kuma tsugunne bata kare ba domin Tante tana can Nijar da sauran 'yan uwa ana shirin bikin 'ya'yanta Yousuf da Radhiya saboda haka ana wannan dinner din can zasu wuce ayi sabon biki sannan amaren su tare. Dama kuma Tante din ta riga ta sanar dasu Ummi kada a dauko wata mai gyaran jiki zata taho da kawarta tun suna 'yan mata idan sun zo taron Zayyan zata barta a nan. Arifah daga Nijar zasu wuce France shi kuma Awwab ya riga yasa an fara nemawa Radhiya visar Germany can zai tafi da ita suyi sati biyu su dawo Nigeria.
Tun yanzu kowa jiki ya fara fada masa saboda shirye shirye. Ana ta kai dinkunan biki na amarya , 'yan uwanta da iyaye. Zahra da Raji sun dawo daga Katsina sai hutu ya kara daga wurin aiki amma fa idan ya koma shekarar kaf bashi da hutu. Fauziyya itama sauki ya samu sun koma Katsina sai daurin auren Bilal zai taho da ita.
SANNU SANNU BATA HANA ZUWA
Saura kwana uku daurin auren Arifah hakan na nufi kwanaki hudu ya rage na Radhiya amma har yanzu Awwab bai dawo ba sai bata hakuri yake yi al'amura sun zo ba yadda yayi zato ba. Radhiya tun tana daurewa sai da tayi masa kuka da daddare akan bata fatan a daura auren baya nan. Hakuri ya bata domin wani training aka saka yake jagoranta. Ainihi bashi bane da tuni ma ya dawo gida sai matar wanda zaiyi ta haihu sati biyar kafin ainihin lokacin haihuwarta. Abu yazo da tangarda dole ya dauki hutu. Gashi daga shi sai Awwab ne suka yi wannan course din a Ukraine. Tunda sunsan aure zaiyi shine aka daga masa kafa zai taho ana gobe daurin auren Yousuf.
Ga abu ya dame shi ga fushin Alheran dinsa sannan Mami da Daddy sun kira shi a lokuta mabambanta kowanne baisan dayan ya kira ba suna jaddada masa idan ya bari aka daura aure babu shi zai ga fushinsu.
Ya gama shirinsa tsaf ranar da zai taho ana gobe daurin auren su Arifah yayi ta kiran Radhiya taki dauka tana ta kunkuni. Text yayi mata mai dauke da dadadan kalamai ya sanar da ita yana hanya zai sauka shadayan dare. Bata yi masa reply ba sai sai kowa ya ga sauyi da walwalarta da ta karu. Tante ta fadawa ya taho tace to maza ta tanadar masa abinci a kai gidan Mami. Yousuf da suka zo da sauran mutanen Nijar shi acan yayi masauki dakin Awwab tare da Raji. Gidan Major General Zayyan kuwa babu masaka tsinke saboda 'yan uwansa na Nijar iyaye su Alh Sidi da Alh Ghoumar. Alh Mousa dai da mijin Mammee da sauran tawagarsu hotel aka kama musu. 'Yan uwa ne aka taru ko ta ina. Emzee ma ya da safe ya iso sai dai gidan Mama ya wuce kai tsaye ga mamakinsa Halifa ma ya riga shi zuwa suna tare da Ibrahim. Sakin fuska yayi kamar babu komai a ransa ya rungumi dan uwansa sai dai har ransa yana jin babu dadi da kuma hangen me zai faru idan gaskiya tayi halinta.