← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 157

Sashe 46

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wata zuciyar tana kwabarta wata tana ingizata har ta mika hannu tayi saurin janyewa "wayo zaka yi min, na tuna me kace dazu"

"Ke dai kina kyankyamin abin bakina kawai"

"Haba dai..." bata rufe bakin ba ya saka mata sauran da ya rage har hannunsa yana taba lebenta. Saurin tashi tsaye yayi ita kuwa ta rasa me zata yi ma.

"Ki rage min kinga kadan na sha"

Lumshe ido tayi tana tsotsar alawar yana kallon yadda bakinta yake motsawa yana jin kamar ya taya shi. Girgiza kai yayi da sauri. Lafiyata kalau kuwa ya tambayi kansa.

"Ahhhh" Radhiya tace ta bude bakin ta mike tsaye yadda zai gano cikin bakin nata sosai. Ta shanye alawar saura yar kadan.

"Cewa nayi ki rage min fa"

"Nima bata isheni ba. Babu kari?"

"Zan gamu dake ne, muje ciki su fito bana jin zamu iya wucewa a yau sai dai mu kwana a Kano" tafiya ciki ya soma yi.

"Hamma gashi" ya juyo ta miko masa yar karamar sweet din ya karba yana kallon cikin kwayar idonunta ya saka a bakinsa. Bata sani ba ko shima yaji amma ita dai wani abu ne ya zarga mata har kasan zuciyarta.

[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Basu dade da fita ba Daddy ya kira Mami yana tambayarta hanya da mai jiki, su ma shigarsu Sakkwato kenan. Ya bukaci gaisawa da Malamijo wanda hakan ba karamin dadi yayi masa ba. Da Mami ta sake karba ne yake bata shawarar me zai hana su kwana washegari su kama hanya da wuri. Banda dare da ya tabbatar sai sunyi a hanya yana ganin ko babu komai itama Mairama sun mutunta ta. Zata ji dadi su kwana yadda itama taje nasu gidajen ta kwana. Mami dama harda tsoron dora musu nauyi da take yi yace duka babu komai kwana daya dai ta sanar da Ummin Awwab yasan zata yi farinciki.

"Ummi yanzu Daddy yake cewa gara mu kwana saboda dare"

Murmushi Mairama tayi da ya nuna jindadinta kamar yadda Major yayi hasashe. Baza a rasa dakunan da za'a sauke su ba. Abinci kuwa bata da matsala tunda da 'yan kudadenta. Zata bayar ne a siyo abinda zata fita kunyarsu.

"Wannan murmushi Ummi to me yasa baki fada min kina so mu kwana ba? Duk daya muke fa"

"Nasan kinyi haka ne don kada ki dora min nauyi. Amma zanfi so ku kwana ko daya ne a gidan da bani da tamkarsa"

Yadikko da Hajjo ta sanarwa Malamijo na ji yasa aka taso kannenta ya bada umarnin a gyara dakuna biyu daya domin mazan dayan kuma na 'yan mata. Ita Hajjo tunda ita ke da girki 'yarta zata gyarawa Mairama da Mami nata dakin. Baki masu alheri irin wannan karramasu ya zama wajibi a wurin Malamijo ko don ya kara samun wani ihsanin kafin su tafi.

"Karami jeka ka fadawa yayanku ya nutsu yaci abincin tunda babu tafiyar"

**********

Kallon kallo suke yi daga bayan Awwab da ya juyawa kofa suka ji ana gyaran murya. Ba kowa bane illa Emzee wanda ya gama ganin musayar sweet. Shi ba abin ya juya ko yace bai gani ba. Murmushi ne ya subuce masa da suka hada ido da Awwab.

"Dama Mami tace na fada maka yanzu Daddy ya kira yace ku hakura da bin hanya yamma tayi"

"Bari naje na sameta, ko Kano muka koma mun rage wani abin"

Tafiya yayi Radhiya ta tsaya dauko kwanukan da tabarma. Emzee ya karbi tray din tana nade tabarmar yace "Allah Sarki bawan Allah"

"Wa?"

"Dr Kawu Zakari mana"

Gabadaya daburcewa tayi "me...me..ya same shi?"

Dariyar da bai fiye yi ba ya yi mata ganin duk ta rude irin na marasa gaskiya "babu komai na tuna irin son da kike yi masa ne a raina nace dan gata. Idan ku ka yi aure alawa zaki rinka bashi"

Borin kunya ya kamata ta fara fadan da babu gaira babu dalili. Dariya ta sake bawa Emzee ya sakalo hannunsa a wuyanta "kinga dai bance komai ba, idan kika tona kanki ba ruwana"

Baki ta bude tana harararsa, wai me yake nufi ne. 

Aljihunsa ya rinka lalubawa ya zazzagesu yana cewa "rufe bakin mai alawar ya shiga ciki ni kuma ko kuli babu a jikina"

"Kwana biyu jikinka bai karbi sako ba shiyasa kake damuna" tace tana daga hannu za ta kai masa duka ya gudu tana jiyo dariyarsa.

Har yanzu babu wanda ya tashi daga tsakar gidan. Awwab ta nemo da ido ya dan durkusa a gaban Mami yana rokonta ko Kano ne su tafi. Mairama tana jinsa tace wato bazai iya kwanan kauye ba.

"Ba haka bane Ummi, bana so ki bawa kanki wahala ne kawai"

"Wace wahala ga kannenka ko ta ina, yanzu Karami zai gyara muku dakin da zaku kwana. Yau kowa zai dana kauyenmu"

"Ko don kada kice ina gudun kauye dole na kwana."

Matsawa yayi gefen Malamijo da yake ta bawa Zayyana da Ibrahim labaran kiriniyar Radhiya. Awwab yaso su tafi da gaske. Ya rasa gane kansa da zuciyarsa akan kanwar tasa. Zuciyarsa ta gaza nutsuwa balle ya fahimci me yake damunsa. Har yanzu dandanon sweet din da ta bashi yake ji a bakinsa na daban da lokacin da ya fara sha. Shi kadai yake murmushi yana satar kallonta tana wurin wanke-wanke tana magana da karamar Antinta cikin amaren da za'ayi bikinsu su hudu. Hajjo ta yiwa Mami da 'yan matan tayin ganin lefen kannen Mairama. A lokacin Mairama tace tunda bikin haka yake kurkusa gaskiya ta fasa komawa Rugar Barkindo. Zata jira ayi bikin a gama nan da kwanaki sha biyu sai su wuce Katsina kuma. Idan an gama biki kaf su tattara su tafi. Tasan Innawuro da matan Baffaninta ma zasu zo idan an aika musu. Dakin Hajjo suka tafi su duka kafin a gama gyara inda zasu kwana. Radhiya ta biyo bayansu zata shiga kenan Malamijo ya kwalawa Emzee da ya zage abinsa yana shara kira yana hura hanci shi mai arziki.

"Zayyanu yaka zo, bar wannan aikin zan sa a karasa. Ka raka wannan samarin gonata su gani" 

Da baya da baya Radhiya ta dawo "ai wallahi tunda naji muma sai munje. Bari naje na kira su Adda Zahra"

"Ban gayyaceki ba fitinanniya, idan sai kinje ne na fasa kowa ya shiga daki ya kwanta dama kun kwaso gajiya"

"Ni din? Ashe yau rabon kosashiyar saniya za ta kasa ne"

"Buhun ubaki mai idanu a tsakar ka, Qur'anin Allah kika yi min barna a gona sai an biyani" yunkurin tashi yake don ya riga yasan hali. Muddin tace zata yi to da wahala idan basu dawo gida da nama ba. Shi yadda yake tsoronta ma yana tsammanin da kanta zata iya yiwa shanunsa rauni kawai don a yanka.

Awwab da Ibrahim sai dariya suke yadda ta dage sai taje Malamijo ma ya dage.

"Malamijo da dai ka kyaleta tunda kasan ko ka hana sai taje" Emzee yace da sigar laluma.

Malamijo ya tamke fuska yana kallon Awwab "yaro ga amana, idan kuka je ko kaza ce ta sami matsala sai kun biyani."

"An gama Malamijo" Awwab yace yana murmushi. Tsohon burge shi yake kamar yadda Zayyan Tureta yaji farkon haduwarsu.

"Ni nafi zargin ita wannan ce ya kamata ta fito a namijin shi kuma salihin nan ya fito a mace sai aka sami mushkila. Yasin duk mai auren 'Yar soja sai yayi shiri da gaske"

Murmushin Emzee ya fadada ya saci kallon Awwab da duk motsin Radhiya sai ya kalleta a ransa fata kawai yake ya ga ranar da za'a ce sunyi aure. 

"Kirawo su idan basu gaji ba" Malamijo yace yana binta da harara. Fatansa Allah Yasa suje su dawo lafiya kada yaji labarin da zuciyarsa bazata iya dauka ba.

Da murnarta taje ta fada musu zasu je gonar Malamijo ganin dabbabinsa. Ghazalatu tana kashingide akan gadon Hajjo tace ita babu inda zata je. Gabadaya ranta ya gama baci da kwanan garin nan. Kana ganin gidan duk girmansa kasan gidan talakawa ne sai wani so ake a burge su. Tana ji lokacin da Yadikko ta tunawa Malamijo kajin da ya bayar ya hadiyi yawu don yayi zaton kajinsa sun sha kafin a sake shawarar kwana. Ba don yaso ba yace a dauka ayi miyar tuwon dare dasu.

Zayyana da Fauziyya tuni suka tashi aka gyara fuska suna murna zasu je. Zahra ma tace bazata iya zuwa ba kan ta ya soma ciwo. Ita dama bata da juriyar tafiyar mota daga amai sai ciwon kai.

Zasu fita Mairama ta dakatar da Radhiya "don Allah kada kije ki yiwa Malamijo barna kinji ko, kuma ana magariba ku dawo"

Dariyar shakiyanci tayi tana kissima me zata yi don babu yadda za'ayi taje ta fito sikau basu ci nama ba. Jama'ar gidan dashi kansa mara lafiyan da amarensa da ta gani kowa yana bukatar protein. 

"Haka fa ya cewa Hamma wai ga amanata kada na taba komai. Ni yanzu Ummi da girmana me zanje in taba a gonar nan?"

Da yake Mami ta san waye Malamijo yanzu tun bayan labarin gidan da Mairama ta basu ga kuma sanin da ta yiwa 'yar tata sai ta rinka dariya ita ma. Ghazalatu na jin Radhiya tace Hamma ta diro daga kan gadon tana cewa ita ma zata bisu.

Radhiya ta tabe baki bata manta me tayi mata ba dazu "ba yanzu kika ce bazaki ba?"

"Iska nake son sha" tace fuska ba annuri. Indai Awwab zaije kuma Radhiya ma zata dole ne ta bisu. Bata son wannan likewar da take yi masa daga gani irin abin nan ne na 'yan kauye an ga dan birni ana so a cusa kai ko Allah zaisa yace yana so.

Emzee yace gonar a bayan gari take da 'yar tafiya shiyasa Awwab yace gara su je a mota tunda yamma tayi. Da sauri sauri Ghazalatu ta riga kowa fitowa. Awwab na bude mazaunin dreba lock din ko ina ya bude ta kama kofar gaban mota ta bude ta shige kamar wadda take tsere da wani. Burinta ta riga Radhiya shiga. Awwab na zaunawa ta kalle shi tana murmushi ya daure ya mayar mata. Ji yayi yafi son Alheran dinsa ta zauna ko da irin zaman dazu ne ta juya masa baya.
Chapter 46 · 0% Book details