← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 157

Sashe 87

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kowa yana son jin yadda ta kasance dashi su duka suna zaune a falon. Emzee da Radhiya kusan danne masa kafafu suka yi kowannensu yana so ya rabi jikinsa. 

Dagawa yayi suka hada ido da Ummi da take ta kallonsa sai taji kunya sosai ta kama ta. Major ne yayi gyaran murya yace a yiwa Annabi SAW salati. A tare suke yi da karfi suka karanta Fatiha, Ayatul Kursiyyu da Amanar Rasul sannan ya dade yana jan su da addu'a duka domin godiya ga Allah SWT.

"Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah...wannan rana ce da bazamu taba mantawa da ita ba har mu bar duniya. Amma kafin mu zauna jin yadda al'amura suka kasance  Zayyan ka zauna kaci abinci ka huta. Ku kuma kowa ya tashi mu bashi wuri ya huta"

Dukkaninsu suka fita Ummi ta tashi tayi kitchen tana godewa dabara irin ta Mama aka bar Zayyan da 'ya'yansa an rasa wanda zai fara tashi cikinsu.

Emzee yasan ya kamata su tashi amma Radhiya ita ta ga wurin kwana. Kallon babanta kawai take yi tana cewa Daadaa yana amsawa da murmushi. Ta kira yafi sau goma bai gajiya da amsawa.

"Emzee kuma wai nan ba mafarki nake yi ba ko?" Tace tana lumshe ido tana sake budewa a kansa.

"Ko in mintsineki ne?"

"A gabana Zayyan?"

Wani dadi yaji ya kama shi mahaifinsa ga kira sunansa da sunan raba gardama tsakaninsa da Addarsa. Kai wannan abu da me zai kwatanta shi. Muryar Umminsu suka ji tana cewa "in fara kawo maka abinci ko tea?"

"Duk wanda kika kawo zanci Fillo. Saboda jiran abincinki rabona da saka wani abu a bakina tun safiyar jiya"

Wai da irin dabarar nan Emzee sai ya yiwa yayarsa alama da ta tashi su ma su fita. Shiru bata gane rangwada kan da yake yi ba sai da yace "Adda taso muje muma Daada yaci abinci"

Hannunsa da ya riko nata ta ture "kai kyaleni ka tafi idan kana so. Ni ban gaji da ganinsa ba." Matsowa ta sake yi jikin kafar Zayyan tana murmushi  "Daada na chanja kama daga yadda ka sanni ko?" 

"Kin koma tamkar Innata"

"Bani labarinta"

Emzee sai ya shiga kada kai. Idan abin Addarsa ya motsa fa bata dogon tunani. Yanzu ace daga dawowarsa zai fara bata labari. Ita kuma neman abinda zai zaunar da ita wurinsa take yi kada ta tashi ta dawo ace ya koma inda ya fito.

"Kin yiwa Hamma Awwab godiya ne? Dashi aka je dauko Daada fa naji Mama tana fada"

An tuno mata da Hammanta sai ta tashi tana murmushi "Daada bari naje na dawo kafin nan kaci abincin"

"Sai kun dawo Alheran"

Wani abin ta tuno zata taambayeshi Emzee ya turata waje ta karfi ya rufe kofar.

Ummi tana ajiye tray a gaban Mijinta taji gabanta ya fadi da aka rufe kofar ga kunya kamar wata sabuwar amarya.

Dariya taji Zayyan yayi yana kallon kofar "ina kika samo min wadannan yaran Fillo? Nan fa dabara yayi mata don su bamu wuri"

Sai da tayi murmushi yaji zuciyarsa tana kadawa da tasowar dadaddiyar soyayyarta tace "sakamakon tureni da Tureta yayi ne" ya sake yin dariya.

Ta gama ajiye komai a gabansa zata fara zuba masa tea din domin ya gasa cikinsa ya riko hannunta bai zaunar da ita ko ina ba sai cinyarsa. Kunya matsananciya ta kama ta yayi mata wani irin riko da yaji tana neman tashi.  Rungume tayi ya dora kansa a tsakiyar kirjinta. A hankali taji hawayensa yana jika mata gaban riga. Tallabo shi tayi ta sake rike shi itama nata hawayen yana sauka a kansa da ya cire hularsa.

Sunyi kusan minti biyar a haka sai ajiyar zuciya kawai da take yi. Da taji yana neman dago kansa ne ta sassauta rikon "ga tea ka fara sha sai na zuba maka tuwo"

Bai bata damar tashi ba sai lebbanta da ya shiga zanawa da karamin yatsansa ya soma magana a hankali "ban taba dena sonki ba Mairama, ban manta ki ba da kyautatawarki gareni. Idan kunci yayi min yawa sai na cika zuciyata da ranar da na fara kamaki kin saci mirinda"

Murmushi tayi mai hade da hawaye shi kuwa ya cigaba da abinda yake yi "a duk lokacin da zan ganmu cikin wannan yanayin nasan mafarki ne wanda nake kwadayin cikarsa idan mun hadu a aljannah. Ashe zan sake ganinki matata. Ashe da rabon na sake samun kaina cikin farincikin zama miji a gareki..." hannu yasa yayo kasa da kanta daidai fuskarsa "ban sani ba ko na manta ko zan iya tunawa"

"Me?" Ta tambayeshi gabanta yana lugude wai yau ita ce tare da Zayyan.

"Wannan" ya karasa fada da hade lebenshi da nata. Lumshe idanu kawai suka yi kowannensu hawayen farincikin cikar buri yana saukowa daga idonsa suka sake rungume juna tightly.

**********

Gidan Mami suka tafi saboda Emzee ya hango shigar bakon da suka zo da su Awwab din Mama yasan manyan nasu can suka je. Ilai kuwa sun taru can dinne Excellency ya gabatar musu da Chibuzor wanda ya fada musu sanadin haduwarsu da Zayyan. Wannan ake kira al'ajabi su Major sun koka sun murmusa sun dara duk a lokaci guda. Yayin da matansu suke dakin Mama su ma suna nasu mamakin.

A gidan Mami suma a falo aka baje hirar murna ta kaure sun saka Awwab a gaba sai ya fada musu yaya akayi. 

"I am exhausted ku bari ayi komai a tsanake"

Sallamar Radhiya yaji ya dago idanunsa da suka soma ja saboda muguwar gajiya da yunwa. Jin kansa yake kamar yana yawo a iska babu kuzari ko kadan. 

Emzee ne a gaba ko da ya shigo kai tsaye yaje ya rungume shi.

"Allah Ya baka abinda kake so duniya da lahira Hamma. Thank you"

"Kada kayi min kuka dai bani da karfin rarrashinka" Awwab ya zolaye shi.

Yana sake kallon Radhiya sai ga nata hawayen kamar famfo ya tashi da sauri. Wani irin sonsa take ji ta kuma rasa da wace kalma zatayi amfani domin ya gane girman farincikin da ya saka ta a ciki. Kofa ya nuna mata dama ko zama batayi ba ta fita yana take mata baya suna jin shakiyancin Ibrahim da Raji wai love is in the air.

Wurin tsayuwa yake nema inda zasu samu su kadaice babu yayi gajeren tsaki. Da sunyi aure fa shikenan duk inda yaso zai kaita. Yanzu anbi an  cika ko ina an hana mutane sakewa. Ta kula da yadda yake ta kalle kalle tayi murmushi.

"Hammana"

Dama ya lafiyar kura. Ya gaji tilis wannan kira da tayi masa yasa zuciya da gangar jikinsa duka amsawa.

"Nagod..."

"Shhhhh kada ma ki fara. Idan kina da wani abin cewa dai ki fada"

Idanunta fal kwalla tace "ni me zan ce Hamma"

"Ni ina da abin fada Alheran." Da wata irin siga mai shiga rai yake kara hargitsa ta da muryarsa "I am not a soldier kuma bani da zuciyar da zan taba zama. Kuma ni ba likita bane, bana jurar ganin jini....But I love you so much kin hana min nutsuwa tun daga ranar da na fara ganinki"

Kifta ido kawai tayi hawayenta ya sauko "nima haka Hammana"

Ya ce "wayo ko?" Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi "ina fata kin shirya aurena yanzu?"

Ba shiri ta rufe fuskarta da gefen mayafi tana neman komawa gidan Mami.

Marairaicewa yayi sosai ya koma kalar tausayi ya shagwabe mata yadda take yi ita ma "Come ooon na gaji fa. I need a wife, a friend....uhummm.... I need you." 

Murmushi take yi sosai ta kasa dagowa ta kalle shi ma. Ya duka saitin fuskarta yana neman hada ido da ita tana kaucewa "kin gani ba, ba don kin mayar dani gwauron dole ba da yanzu I have Alheran to hug when I am happy or sad. My Schatzi to kiss when love is in the air right?"

Gabadaya ta rikice masa ta ma kasa gudun ta barshi shi kadai yake ta zuba hirarsa.

"Kinsan me? I am so tired ga yunwa. Mu koma ciki?"

Tausayinsa taji kana ganinsa kasan a gajiye yake sosai kuwa.

"Muje na zuba maka"

"Baki bani amsa ba fa. Na dage ina ta debo zance duk don na burgeki"

Ya bata dariya ta gama kayarta sannan tace "I am all yours Hammana kai nake jira tuntuni"

Amsar tayi masa dadi suka shiga falon tare. Babu kowa su Zahra sun shige dakin Mami su Ibrahim suna dakin Awwab. Zama yayi akan doguwar kujera ta wuce kitchen zuba masa abinci. Akan tray ta hado komai ta dawo sai dai me...Awwab ya mike abinsa wani nannauyan bacci yayi awon gaba dashi abin tausayi. Kallonsa tayi tana jin soyayyarsa tana dada zama sabuwa a zuciyarta.

***********

A kasa Mairama ta zauna Zayyan yana jingine da kujera ta saka plate  din abincin a tsakaninsu sannan ta tashi.

"Ina zaki?"

"Hannu zan wanke" ta amsa tana sunkuyar da kai saboda tunanin abinda yayi mata mintuna kadan da suka wuce. Tasowa yayi shima yace zai wanke nasa hannun.

"Yi zamanka ina zuwa"

Bata dade ba ta dawo yayi zaton ruwa zata kawo masa a roba na wanke hannu sai gani yayi ta zauna ta debo tuwon ta kawo bakinsa.

Yau kam bashi da karfin zuciya ko kadan. Yau daya dai a Zayyan mijin Mairama yake wanda ya kwashi dimbin shekaru yana muradin sake ganinta ko da daga nesa ne. Hannun nata ya kama ya karasa dashi bakinsa.

"Ashe haka tuwo yake da dadi muka rinka cewa bama so da muna yara" taji yace ta soma dariya ya fara bin yatsunta daya bayan daya yana sudewa.

Fillo sarkin kunya sai ta kasa kara diban wani ta bashi. Ya sanya hannu ya dago kanta idanunta a rufe "alfarma nake nema Fillo"

"Babu alfarma a tsakaninmu kaima ka sani"

"Yau daya don Allah ki tattaro duka kunyar nan ko Alheran ce ki bawa ajiya. Mairama kadai nake bukata in nuna mata yadda shekaru ashirin da biyu suka galabaitar da Sojanta"
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: A haka ta gama bashi abincin yaci mai yawa. Yaushe rabonsa da tuwo ko abinci mai dadi? Miya tasha nama da bushasshen kifi yaci son ransa duk loma yana binta da addu'a da kalmomi masu nuni da kewarta da yayi.
Chapter 87 · 0% Book details