Sashe 121
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Anya banyi garajen aurar dake ba, Fillo yarinyar nan bata girma ba fa"
Ummi sai dariya "kunfi kusa soja da 'yarsa."
"Ni dai ku tsaya nayi muku hoto" tace tana gyara musu tsayuwa "wayyo ni Daada da Ummina sunyi kyau"
Dariya ta basu ta matsa baya zata dauka da wayarta Zayyan ya rungumo Mairama a jikinsa. Ita kunya Radhiya kuma ta kanne ido daya wai a zuwan bata gani ba. Sunyi bala'in kyau ta rinka daukarsu Zayyan yana biye mata suna yi a tsaye ko a zaune. Muryar Arifah da ta jiyo ne ta bar wurin da sauri taje ta karasa shiri.
Hudu da ashirin kowa ya sauko sai fararen kaya kake gani da koren mayafi ko hula. Zayyana gown dinta aikin da farin zare aka hada shiyasa ta saka farin mayafi bayan anyi mata daurin yayi wanda dukkansu matan shi suka yi mai hawa-hawa da dankwalin kayan.
Mutane ke ta fitowa babu wanda ya lura Rahima bata fito ba. Ita kadai take kokonto idan Emzee yaki dawowa ta kade. To amma babbar matsalarta yanzu bai wuce bayanta da yake ciwo saboda dukawa ba don yau ta aikatu.
Irin kayan Arifah sak hatta takalmi da jaka Radhiya ta saka rigar tasu mai high neck. Basu saka sarka ba sai wasu doyayen dankunne green and white masu tsada da daukar ido.
Ta kware da tafiya da heel bata jin wahalarsa ko kadan tana taku daidai ta iso gaban motar. Zagayawa yayi ya bude mata daya gefen gaban yana tsaye zata shiga wani ni'imtaccen kamshi na shigarsa ta ko ina ya rike mata hannu. Kallonsa tayi sau daya ta dauke kanta.
"You look sweet baby"
"Ka fini yin kyau Hammana" tace tana murmushi.
Hannu kawai yasa ya janyota ta fito ya sake matso da ita jikinsa sosai yayi musu selfie.
"Akwai bil adama a bayan mota" cewar Yousuf bayan ya sami chance din kaiwa Arifah kiss a kan hancinta tana rufe idanu.
Dariya Awwab yayi wai yanzu damarsa ce sun gama nasu bai ce komai ba. Zama Radhiya tayi ya gyara mata rigarta ya rufe kofar sannan ya ja suka tafi kana leka motar taurarin soyayya sun mata kawanya.
Wani katafaren events hall suka nufa inda suke iya ganin taron motoci sun cike wurin parking din ciki an fara layi a gefen titi. Suna shiga Emzee yana fita bayan ya karbi mukullin motarsu daga hannun Ibrahim da su suka ajiye su Laila da Zayyana.
"Ina kuma zaka je kasan yanzu su Daada zasu iso a fara"
"Yanzu zan dawo Rahima zan dauko please kace bazan dade ba idan an nemeni"
"Emzee kodai-kodai?" Ibrahim yace yana daga gira.
Cike da shauki Emzee yace "fadi ka kara bros yarinyar nan ta cuceni...ko shiryawa banyi ba kawai na nemi zuciyata na rasa ashe ita ta dauka. Da tayi warning dina kasan kai zan fara sanarwa"
Duka Ibrahim ya kai masa a baya yana kyakyata dariya "shege malamin soyayya ya fada ruwa....tabdi amma har ta bani tausayi ta kwaso Emzee chewing gum"
"Me ka mayar dani?"
"Irin mazan da idan suna son mace zasu iya sadaukar da komai nasu domin kyautata mata mana"
"To kai din ba shi bane?"
Bangaren da Zayyana take Ibrahim ya kallo "I can die for her man"
"I feel you bros nima haka nake ji. Ina bukatar time da ita ne domin in san ko wacece. Na dai fi tunanin tana da alaka da gidansu Halifa maybe cousin dinsu ce tunda ina ganinta da Hibbah."
Gaban Ibrahim ne ya fadi ya soma tunanin yaya akayi Emzee bai san wace Rahima ba. Tunawa yayi da yadda ya tsani Gwaggo Salame yaji jikinsa yayi sanyi. Bai taba ganin Emzee so cheerful ba irin yanzu, gaskiya bazai iya rushe masa wannan sabon farincikin ba. Zai bari ya gano da kansa kila sanadiyar shiryawar iyayensu kenan.
"Na tafi" yaji Emzee yace.
A gurguje ya tada motar ya koma gida. Minti goma ya kaishi saboda babu nisa da gidansu. Sai yanzu ya tuna bashi da nambar wayarta to ta yaya zai kirata. Idan kuma ta tafi wurin bata jira shi ba fa. Tambayoyin da yake ta yiwa kansa kenan sai ga mai aikinsu 'yar budurwar ta fito itama a shirye fes da ita.
"Yauwa don Allah kirawo min Rahima a dakin Adda Radhiya."
"Kowa ya tafi fa muma Ummi tace yanzu dreba zai dawo daukarmu shine na fito dubawa da ka shigo"
Gwiwarsa ce tayi sanyi ya koma motar sai ya sake dawowa zuciyarsa na fada masa Rahima na jiransa "daure ki duba min nasan tana nan"
Ba musu ta shiga gidan. Dakin kasa da suke ta shiga tayi sa'ar ganin Rahima a shirye cikin nata kayan kamar kowa Ummi ta dinka mata sai dai ita dasu Zahra dankwalin kayan suka saka. Arifah da Radhiya ne kawai masu ashoke manyan amare. Mayafinta daidai da ita har ka ta lulluba shi yadda ta saba tayi kyau sosai.
"Karami ke kiranki a waje"
Da faduwar gaba ta tashi tana tunanin karfin halinta na zama don yace ta zauna. Sai dai bata jin akwai ranar da za ta yi fatan yi masa musu saboda babban matsayin da ya kwata ta karfin tsiya a zuciyarta don itama bata shirya ba.
Kayansa hatta hula sak na mahaifinsa yana tsaye a bakin kofa ta fito. Ido suka hada ya sakar mata murmushi ta janyo mayafin ta rufe rabin fuskarta.
"Hey kada ki cuceni ki hanani ganin fuskarki yau ba kawance"
Langabe kai tayi suna tafiya wurin motar "sai me?"
"Muhammad da Rahima"
Sake rufe fuska tayi komai nata yana burge shi matuka ya dora hannunsa a saitin zuciyarsa "my God, she is so adorable"
Sun kusa kaiwa motar yaji an kwala masa kira daga cikin gidan "kai Karami ku jirani wannan dreban da za'a turo ban ga ranar zuwansa ba"
Ba kowa bace illa Salame ta taho buguzum cikin wata kodaddiyar shadda wadda take yiwa kallon mai kyau har yanzu tana goye da Khadi kamar wata jaririya.
Gaban Rahima ya fadi zuciyar Emzee kuma tamkar ta fito ta baki saboda bacin rai har ta iso bakin motar ta bude gaba ta shige kwam abinta.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Dan duka kanta tayi tana lekensa ta sake daga murya "kai shigo mu tafi mana" ta kuma lekawa ta daya bangaren "kema shiga kin yiwa mutane wani kikam"
Emzee alama ya yiwa Rahima da ta tsaya don bai ga dalilin daukarta da makiyar Ummi a mota daya ba. Sannan abu na biyu baya son a matsayinta na yayar Ummi tayi abin zubar da mutumci a gaban Rahimansa.
Khadi da ke kan cinyar Salame kuma duk maganar da take kusan akan fuskarta tayi sai sa hannu tayi ta toshe hanci babu kunya tana yiwa babarta wani irin kallon haushi "hmmm Umma hmmm wali-wali a bacinci"
Da sauri Emzee ya fitar da kansa kafin ya shaka yayin da Salame ta dage ta zabgawa Khadi duka a gadon baya ta fashe da kuka. Rahima ta tafi da sauri ta bude kofar ta daukota Emzee ya yiwa Salame wani disgusting look. Gaban motar ya riga ya fara wani abu sama-sama mara dadin ji ga hakoranta masu kore daga samansu. Sannan abin haushi dubi yadda ta daki karamar yarinya haka. Kayan jikinta kuwa ya rasa abib fada. Shi dai ya tabbatar Ummi ta sasu sayen kaya ready made na mutan Sumaila shi da Ibrahim da Laila suka je. Haushin abinda Ummin ta yi mata dazu shine yasa taki saka kayan wai tafi karfinsu.
Khadi 'yar banza ta tasha hannu ba musu ta gudu wurin yayarta ta lafe tana kuka. Jikin Rahima na rawa dreban ya dawo. Ajiyar zuciya Emzee yayi yana kallota ta saman motar.
A hankali yayi mata magana yana kallon yadda ta rikice sosai "ki bisu zan taho yanzu okay"
Kai ta gyada da sauri ta tafi daya motar tana tsoron kada Salame tayi mata wata maganar ko tace su koma gida. Ita kuma zuciya a baka saboda bacin rai yau rashin m din na Khadi akanta ya kare a gaban wannan yaron na Mairama. Muryarsa taji ya gama goga hannuwansa da juna.
"Lets get going Gwaggo"
Dauke kai tayi yana ganin dreban yayi waje kawai ya cire hularsa da riga daga shi sai wando da vest. Bayan motar ya ajiye rigarsa da kyau ya dora hular a kanta don kada ta fado ya shiga ya zauna ya daura belt. Salame ta kalle shi tana tunanin dalilinsa na tube riga bata gama sannin me ake ciki ba ya fizgi motar a guje ya fita da ribas sai da cikinta ya kada. Wata irin cin taya yayi da burki yayi kwana tamkar mai shirin zuwa Sumaila a awa guda daga Abuja ya kwashi motar ya hau titi. Gudu yake na karshen rashin hankali sai dai kaji qeeeyyyyy quuuuu....yaci taya ko ya taka burki sai motar tayi kamar za ta hantsila. Salame tana kallon yadda ya murtuke fuska kuma jikinsa baya motsawa amma ita sai dai tayi gaba yif ta dawo baya yif jikinta yana ta mazari.
"Kai dan ubanka tafi a hankali ko ka saukeni"
Idan motar za ta amsa to Emzee ya amsa. Salame sai da ta kai ta daga hannu za ta doke shi yayi mata wani razanannen kallo tare da taka burkin gaggawa sai ga kanta ya tafi saura kiris ta doki glass. Hannunsa yasa ya tareta don ba jini yake son fitar mata ba. Burinsa ko ta halin kaka ya fanshi wani abu na makantar Ummi na shakara goma. Tsanar Salame ke kara ruri a zuciyarsa zai bincika ya tabbatar da sa hannunta. Idan akwai ko su Ummi basu sani ba da shi da Addarsa sai sun yi mata abinda zata ji rayuwarta tayi kunci. Yanzu haka ranar zuwa Sakkwato biki suke jira shi da Radhiya su barwa Maikudi abinda bazai manta ba. Ba wani abu bane kuma yafi taba zukatansu sai wulakancin da ya yiwa Umminsu ga wahalar haihuwa ga radadin mutuwar miji da taji.
Ummi sai dariya "kunfi kusa soja da 'yarsa."
"Ni dai ku tsaya nayi muku hoto" tace tana gyara musu tsayuwa "wayyo ni Daada da Ummina sunyi kyau"
Dariya ta basu ta matsa baya zata dauka da wayarta Zayyan ya rungumo Mairama a jikinsa. Ita kunya Radhiya kuma ta kanne ido daya wai a zuwan bata gani ba. Sunyi bala'in kyau ta rinka daukarsu Zayyan yana biye mata suna yi a tsaye ko a zaune. Muryar Arifah da ta jiyo ne ta bar wurin da sauri taje ta karasa shiri.
Hudu da ashirin kowa ya sauko sai fararen kaya kake gani da koren mayafi ko hula. Zayyana gown dinta aikin da farin zare aka hada shiyasa ta saka farin mayafi bayan anyi mata daurin yayi wanda dukkansu matan shi suka yi mai hawa-hawa da dankwalin kayan.
Mutane ke ta fitowa babu wanda ya lura Rahima bata fito ba. Ita kadai take kokonto idan Emzee yaki dawowa ta kade. To amma babbar matsalarta yanzu bai wuce bayanta da yake ciwo saboda dukawa ba don yau ta aikatu.
Irin kayan Arifah sak hatta takalmi da jaka Radhiya ta saka rigar tasu mai high neck. Basu saka sarka ba sai wasu doyayen dankunne green and white masu tsada da daukar ido.
Ta kware da tafiya da heel bata jin wahalarsa ko kadan tana taku daidai ta iso gaban motar. Zagayawa yayi ya bude mata daya gefen gaban yana tsaye zata shiga wani ni'imtaccen kamshi na shigarsa ta ko ina ya rike mata hannu. Kallonsa tayi sau daya ta dauke kanta.
"You look sweet baby"
"Ka fini yin kyau Hammana" tace tana murmushi.
Hannu kawai yasa ya janyota ta fito ya sake matso da ita jikinsa sosai yayi musu selfie.
"Akwai bil adama a bayan mota" cewar Yousuf bayan ya sami chance din kaiwa Arifah kiss a kan hancinta tana rufe idanu.
Dariya Awwab yayi wai yanzu damarsa ce sun gama nasu bai ce komai ba. Zama Radhiya tayi ya gyara mata rigarta ya rufe kofar sannan ya ja suka tafi kana leka motar taurarin soyayya sun mata kawanya.
Wani katafaren events hall suka nufa inda suke iya ganin taron motoci sun cike wurin parking din ciki an fara layi a gefen titi. Suna shiga Emzee yana fita bayan ya karbi mukullin motarsu daga hannun Ibrahim da su suka ajiye su Laila da Zayyana.
"Ina kuma zaka je kasan yanzu su Daada zasu iso a fara"
"Yanzu zan dawo Rahima zan dauko please kace bazan dade ba idan an nemeni"
"Emzee kodai-kodai?" Ibrahim yace yana daga gira.
Cike da shauki Emzee yace "fadi ka kara bros yarinyar nan ta cuceni...ko shiryawa banyi ba kawai na nemi zuciyata na rasa ashe ita ta dauka. Da tayi warning dina kasan kai zan fara sanarwa"
Duka Ibrahim ya kai masa a baya yana kyakyata dariya "shege malamin soyayya ya fada ruwa....tabdi amma har ta bani tausayi ta kwaso Emzee chewing gum"
"Me ka mayar dani?"
"Irin mazan da idan suna son mace zasu iya sadaukar da komai nasu domin kyautata mata mana"
"To kai din ba shi bane?"
Bangaren da Zayyana take Ibrahim ya kallo "I can die for her man"
"I feel you bros nima haka nake ji. Ina bukatar time da ita ne domin in san ko wacece. Na dai fi tunanin tana da alaka da gidansu Halifa maybe cousin dinsu ce tunda ina ganinta da Hibbah."
Gaban Ibrahim ne ya fadi ya soma tunanin yaya akayi Emzee bai san wace Rahima ba. Tunawa yayi da yadda ya tsani Gwaggo Salame yaji jikinsa yayi sanyi. Bai taba ganin Emzee so cheerful ba irin yanzu, gaskiya bazai iya rushe masa wannan sabon farincikin ba. Zai bari ya gano da kansa kila sanadiyar shiryawar iyayensu kenan.
"Na tafi" yaji Emzee yace.
A gurguje ya tada motar ya koma gida. Minti goma ya kaishi saboda babu nisa da gidansu. Sai yanzu ya tuna bashi da nambar wayarta to ta yaya zai kirata. Idan kuma ta tafi wurin bata jira shi ba fa. Tambayoyin da yake ta yiwa kansa kenan sai ga mai aikinsu 'yar budurwar ta fito itama a shirye fes da ita.
"Yauwa don Allah kirawo min Rahima a dakin Adda Radhiya."
"Kowa ya tafi fa muma Ummi tace yanzu dreba zai dawo daukarmu shine na fito dubawa da ka shigo"
Gwiwarsa ce tayi sanyi ya koma motar sai ya sake dawowa zuciyarsa na fada masa Rahima na jiransa "daure ki duba min nasan tana nan"
Ba musu ta shiga gidan. Dakin kasa da suke ta shiga tayi sa'ar ganin Rahima a shirye cikin nata kayan kamar kowa Ummi ta dinka mata sai dai ita dasu Zahra dankwalin kayan suka saka. Arifah da Radhiya ne kawai masu ashoke manyan amare. Mayafinta daidai da ita har ka ta lulluba shi yadda ta saba tayi kyau sosai.
"Karami ke kiranki a waje"
Da faduwar gaba ta tashi tana tunanin karfin halinta na zama don yace ta zauna. Sai dai bata jin akwai ranar da za ta yi fatan yi masa musu saboda babban matsayin da ya kwata ta karfin tsiya a zuciyarta don itama bata shirya ba.
Kayansa hatta hula sak na mahaifinsa yana tsaye a bakin kofa ta fito. Ido suka hada ya sakar mata murmushi ta janyo mayafin ta rufe rabin fuskarta.
"Hey kada ki cuceni ki hanani ganin fuskarki yau ba kawance"
Langabe kai tayi suna tafiya wurin motar "sai me?"
"Muhammad da Rahima"
Sake rufe fuska tayi komai nata yana burge shi matuka ya dora hannunsa a saitin zuciyarsa "my God, she is so adorable"
Sun kusa kaiwa motar yaji an kwala masa kira daga cikin gidan "kai Karami ku jirani wannan dreban da za'a turo ban ga ranar zuwansa ba"
Ba kowa bace illa Salame ta taho buguzum cikin wata kodaddiyar shadda wadda take yiwa kallon mai kyau har yanzu tana goye da Khadi kamar wata jaririya.
Gaban Rahima ya fadi zuciyar Emzee kuma tamkar ta fito ta baki saboda bacin rai har ta iso bakin motar ta bude gaba ta shige kwam abinta.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Dan duka kanta tayi tana lekensa ta sake daga murya "kai shigo mu tafi mana" ta kuma lekawa ta daya bangaren "kema shiga kin yiwa mutane wani kikam"
Emzee alama ya yiwa Rahima da ta tsaya don bai ga dalilin daukarta da makiyar Ummi a mota daya ba. Sannan abu na biyu baya son a matsayinta na yayar Ummi tayi abin zubar da mutumci a gaban Rahimansa.
Khadi da ke kan cinyar Salame kuma duk maganar da take kusan akan fuskarta tayi sai sa hannu tayi ta toshe hanci babu kunya tana yiwa babarta wani irin kallon haushi "hmmm Umma hmmm wali-wali a bacinci"
Da sauri Emzee ya fitar da kansa kafin ya shaka yayin da Salame ta dage ta zabgawa Khadi duka a gadon baya ta fashe da kuka. Rahima ta tafi da sauri ta bude kofar ta daukota Emzee ya yiwa Salame wani disgusting look. Gaban motar ya riga ya fara wani abu sama-sama mara dadin ji ga hakoranta masu kore daga samansu. Sannan abin haushi dubi yadda ta daki karamar yarinya haka. Kayan jikinta kuwa ya rasa abib fada. Shi dai ya tabbatar Ummi ta sasu sayen kaya ready made na mutan Sumaila shi da Ibrahim da Laila suka je. Haushin abinda Ummin ta yi mata dazu shine yasa taki saka kayan wai tafi karfinsu.
Khadi 'yar banza ta tasha hannu ba musu ta gudu wurin yayarta ta lafe tana kuka. Jikin Rahima na rawa dreban ya dawo. Ajiyar zuciya Emzee yayi yana kallota ta saman motar.
A hankali yayi mata magana yana kallon yadda ta rikice sosai "ki bisu zan taho yanzu okay"
Kai ta gyada da sauri ta tafi daya motar tana tsoron kada Salame tayi mata wata maganar ko tace su koma gida. Ita kuma zuciya a baka saboda bacin rai yau rashin m din na Khadi akanta ya kare a gaban wannan yaron na Mairama. Muryarsa taji ya gama goga hannuwansa da juna.
"Lets get going Gwaggo"
Dauke kai tayi yana ganin dreban yayi waje kawai ya cire hularsa da riga daga shi sai wando da vest. Bayan motar ya ajiye rigarsa da kyau ya dora hular a kanta don kada ta fado ya shiga ya zauna ya daura belt. Salame ta kalle shi tana tunanin dalilinsa na tube riga bata gama sannin me ake ciki ba ya fizgi motar a guje ya fita da ribas sai da cikinta ya kada. Wata irin cin taya yayi da burki yayi kwana tamkar mai shirin zuwa Sumaila a awa guda daga Abuja ya kwashi motar ya hau titi. Gudu yake na karshen rashin hankali sai dai kaji qeeeyyyyy quuuuu....yaci taya ko ya taka burki sai motar tayi kamar za ta hantsila. Salame tana kallon yadda ya murtuke fuska kuma jikinsa baya motsawa amma ita sai dai tayi gaba yif ta dawo baya yif jikinta yana ta mazari.
"Kai dan ubanka tafi a hankali ko ka saukeni"
Idan motar za ta amsa to Emzee ya amsa. Salame sai da ta kai ta daga hannu za ta doke shi yayi mata wani razanannen kallo tare da taka burkin gaggawa sai ga kanta ya tafi saura kiris ta doki glass. Hannunsa yasa ya tareta don ba jini yake son fitar mata ba. Burinsa ko ta halin kaka ya fanshi wani abu na makantar Ummi na shakara goma. Tsanar Salame ke kara ruri a zuciyarsa zai bincika ya tabbatar da sa hannunta. Idan akwai ko su Ummi basu sani ba da shi da Addarsa sai sun yi mata abinda zata ji rayuwarta tayi kunci. Yanzu haka ranar zuwa Sakkwato biki suke jira shi da Radhiya su barwa Maikudi abinda bazai manta ba. Ba wani abu bane kuma yafi taba zukatansu sai wulakancin da ya yiwa Umminsu ga wahalar haihuwa ga radadin mutuwar miji da taji.