← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 117 OF 157

Sashe 117

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To Ummi" tace a sanyaye ta fita.

Tana cikin hawa benen Emzee na saukowa a gurguje yake tafiya suka kusa karo tayi saurin matsawa gefe. Idanun nan nata ne suka sauka a kan fuskarsa wadda a take murmushi ya maye gurbin bacin ran da ya sauko dashi saboda ganin Salame da yayi a cikin tawagar 'yan Sumaila.

"Kawar Soja daga ina?"

"Ni dai ba kawarka bace"

Murmushi yayi ya nade hannuwansa a kirgi ya tsare hanyar wucewarta "nima ba kawancen kawai nake so ba harda...."

Da sauri ta dago gabanta na faduwa "harda me?"

Kansa ya dukar daidai fuskarta "harda idanun Rahima...zan samu?"

Rikicewa tayi ta samu ya dan matsa ta kwasa a guje yana ta cewa tayi a hankali kada ta fadi. Sai da ya ga ta bace masa ya dan rankwashi kansa "Muhammad Zayyan kalau kake kuwa?" Ya tambayi kansa don ya rasa yadda akayi idan ya ganta daga bugun zuciya sai kasa controlling kansa da bakinsa da yake yi. Kai ya girgiza ya sauka ya dauki mota ya fita.

Bayan magariba kuwa Ummi ta bawa Zayyana dubu ashirin da biyar tunda ita ce babba tace dreba na jiransu su siyowa Khadi kayan sawa kuma kada su manta da takalmi, pants da brush. Sahad ya kaisu suka kwaso kayan da ya dace. Rahima tana da wata dubu daya cikin kudin da Ummi ta basu rannan suka siyo kayan kwalliya ta sayawa Khadi packet din ribbons na dari shida za ta yi mata kitso sai ta saka mata. Gida suka wuce da murnarta bayan sun nunawa Ummi tasa musu albarka ta wuce ta kaiwa Salame. Ba karamin dadi Salame taji ba don bata da komai sai dari uku amma dayake ta saka hassada da kyashi a zuci sai ta kyabe baki.

"Ki fada mata ina komawa gida zan turo mata kudinta don nafi karfin cin arzikinta yanzu ma don na manto jakar ne kuma a ciki kudina yake"

Tashi Rahima tayi zata fita Salamen ta kuma kiranta "ina kuma zaki je? dawo nan ki kwanta kusa dani"

To ai ko numfashin kirki bazata iya ba bare bacci a gabanta a tsorace take sosai Yadikko ta kama hannunta ta kaita bakin kofa ta ce ta wuce wurin yayarta Radhiya ta rufo kofar. Tana dawowa tasa hannu ta dauke Salame da wani gigitaccen mari. A kidime ta dago kai ga kannenta don ma Khadi tayi bacci. Hajjo tace tayi mata daidai.

Rai a bace sosai Yadikko ta nunata da yatsa "ba ni na haifeki ba Salame amma ina tsammanin rikon da nayi miki ya bani matsayin uwar da ta isa dake. Nayi miki rantsuwa daga yau har mu tafi idan kika sake yin wani abu domin cusgunawa Mairama ko Rahima sau naci mutumcinki la'ada waje. Mutuminyar banza wadda bakinciki ya yiwa tsatsa a zuci."

"Shiyasa taki gaba taki baya babu wani cigaba a rayuwarki" Hajjo ta kara da nata. 

Sunyi mata tatas don sai da tayi hawaye Yadikko ta kyaleta tana jin zafin wannan mummunar halayya ta Salame yarinyar da a da can tafi kowa shiru shiru a gidansu ashe macijin sari ka noke ce.

Da rana Ummi ta bawa Yadikko katinsu na shiga wurin taron haka ma ta baiwa Tante wanda zata bawa nasu mutanen. To dayake dama da yawansu sun zo ne akan ainihin na gidan ba wannan ba da gwamnati ko muce sojoji suka shirya ba sai ba'a sami rikici ba. Katin ba yawa garesu ba kuma dai bazasu so suje su bawa kansu kunya ba. An gama hada masu tafiya su Mami suna gidan Emzee tun safe da yasa kafa ya fita basu sake ganinsa ba.

Kafin sallar magariba sai ga Arifah da Mom dinta da gudu suka rungume juma ita da kanwarta Radhiya. Matar Alh Salisu itama ta iso aka fara shirin fita domin karfe takwas za'a fara taron.

Sai da Ummi ta shirya mijinta bayan kyakkyawar kulawar da ya samu tamkar kada ya tashi saboda yadda yake jin matar tasa a rai. Sababbin kayansa da suka dace da mukaminsa ta taimaka masa ya saka ta saka masa sabuwar farar safa da bakin takalminsa tafiyayye cover shoe. Ya sake gyara fuska sai wani annuri yake fitarwa. Sai da ta kammala dashi sannan ta fita itama ta shirya don tare zasu tafi.

Lace ne ta saka army green da digon gold a jiki. Mai kwalliya Mama ta dauko amma aka ce tayi mata matured kwalliya ba mai cika fuska ba kamar karamar yarinya. Tayi kyau matuka ta fito a Mairama Fillon Zayyan babu wata makusa sai hassadar makiya. Mayafinta gold ne sai takalmi heel da wata karamar dinner pause itama gold ga farin gilashinta ya sake fito da kyakkyawar fuskarta, hannuwa da kafafu sun sha jan lalle mai kyau da tasa 'yarta Rahima tayi mata. Matan manya ne suka fito ita da Mami, Mama, Tante, Mom din Arifah da Matar Alh Salisu. 

Fita suka yi kowacce ta shiga motar mijinta abin gwanin ban sha'awa sojoji na mara musu baya. Mutum biyu aka kara daga Nijar sai kuma Mubaraka yayar Zayyan da  matar Badaru. Yadikko kuma ta bawa Salame, Ayuba da Bature kati don Laila ita dama tuni Ummi ta bata nata tana tare dasu Radhiya ana ta shiri. 

Kowa ya gama nasa shirin suka fito Radhiya ta saka wata abaya mai masifar kyau da daukar ido ja da bakaken stones. Covershoe mai madauri ta saka baki sai purse da ta saka wayarta da hoda. Duka dama abayar suka zabi sakawa sai dai kowa tata daban. Ummi ta fito da 'yarya Rahima don itama ta saya mata wata baka mai duwatsu pink.

Idan kaga matan sai ka juya ka kara babu wadda bata yi kyau ba. Jawad da Femi a gida aka barsu saboda taron babu yara suka fito aka shiga motocin da suke jiransu.

Mazan ma ba'a barsu a baya ba sun hade duka cikin suits kamshi na dukan kamshi su ma suna gamawa sai Nicon Hilton inda za'ayi taron a wani babban dakin taro da yake cikin hotel din.

Decoration din wurin komai green ne da white an kawata shi fiye da zato ga ma'aikata a tsaye suna jira a shigo su nunawa kowa seat dinsa saboda akwai number a jiki. Awwab da Yousuf a matse suke da ganin amarensu abin takaici number din seat dinsu ya nesanta su da juna. Radhiya wata faduwar gaba taji da suka hada ido yana zaune kusa da Yousuf rike da waya a hannu. Ya hade cikin three piece armani suit khaki color da coffee coloured necktie ga brown din cover shoe. Daga inda yake a zaune ya daga wayarsa ya dauketa a hoto ta sadda kanta kasa a kunyace su Zahra suna mata dariya. 

Bayan an zazzauna kamar minti goma MC KDM sunan mai gabatar da taron wanda baya zuwa kowane irin taro dama sai na manya yace kowa ya tashi shugaban kasa zai shigo da first lady. Wurin zamansu daban aka zauna bayan national anthem da akayi. Ummi duk ta damu ina Karami sai da Zayyan yace ta kwantar da hankalinta dan nata yana nan za ta ganshi. An shiga taro ka in da na in hankula suka karkata suka koma ga MC da abubuwan da ake gabatarwa. Salame kallo daya ta yiwa Zayyan bata kara ba domin zuciyarta sai da tayi barazanar ballo mata kirji kuma abin takaici ga Alh Salisu a gefe sai taji duk ta muzanta a cikin mutane saboda kayan da ta saka na taron gidan Malamijo ne ganin kanta tayi wata koma baya a cikinsu.

Duhu hall din yayi a take hasken screen da za'a gabatar da tarihin Zayyan ya mamaye wurin. An fara da nuna hotunansa yana matakin farko a soja sai dariyar manyan baki kake ji kadan kadan saboda daga hoton kadai zaka iya gane cewa Zayyan Tureta ba karamin fitinanne bane. A hankali aka zo kan aurensa duka ana nunawa ne KDM yana bayani. An tsayar da hoton akan shi da Daddy da Baba Hadir ranar tafiyarsu Liberia. Daga nan ya cigaba da narrating rayuwar da Zayyan yayi sai da gwamnoni biyu suka zubar da hawaye musamman da aka zo video din fitowarsa daga motar da ta kaishi Nigerian Embassy lokacin da ya hadu da Excellency da Awwab. Su Ummi sai hawaye yasa hannu ya rike nata a hankali tace "I love you Sojana"

"I love you too Fillo" ya maida mata iya jin kunnenta.

An kare video din da wani hotonsa ne shi da Ummi, Radhiya da Emzee a falon gidansa bayan sun koma. Fitilu aka kunna mutane sai sharbar hawayen jin labarin al'ajabi na wannan soja.

MC yace kowa ya shirya domin ganin wasan da sojoji suka shirya domin murnar dawowar jan gwarzo jarumin jarumai.

Wata murya suka ji inda mai ita yake commanding Cadets 'yan uwansa da kowa ya shiga layi. Tsit hall din yayi kamar ruwa ya cinyesu lokacin da aka saka wani kida irin na band din sojoji sai gasu nan sun fito mutum arba'in cikon na arba'in da dayan shine commander din wannan parade din wato Cadet Muhammad Zayyan Tureta. 

Sun sha training ba na wasa ba daga shi har sauran shiyasa babu kuskure ko na motsi daga garesu. Bindiga ce a hannunsu duk da ba harbi zasu yi ba suka yi wani wasa da ita da ya burge kowa a wurin. Komai nasu tare kidan yana chanjawa da umarnin Emzee. Karshe mutane suka ga wadanda suka gama parade din sun matsa Emzee ya sake bada umarni sai ga wasu suna fitowa cikin tsari suka shiga sahu suka yi wani layi layi sai da suka durkusa kowa ya gane sun rubuta Nigeria ne ai kuwa mutane a tare suka karanta 

"NIGERIA"

Wasu suka fito a bayansu suma suka dunkule a kasa aka sake karantawa.

"WELCOMES"

Sai na karshen suma cikin gwaninta suka yi nasu layin tare da durkusawa.

"ZAYYAN"

Habawa sai wuri ya kaure da tafi da murna KDM yace

"Da wannan nake gabatar muku da tauraron wannan rana Major General Zayyan Muhammad Tureta"

Chanja kida akayi yazo ya haye stage din bayan ya yiwa dansa abim sonsa Emzee kallo daya tak yana tsaye ya kame sauran suna nan inda suke.

KDM yace ko yana da abin fada ga dimbin 'yan Nigeria da suke wurin da masu kallo live a gida.
Chapter 117 · 0% Book details