Sashe 140
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saurin fita tayi daga motar don tasan me zai ce. Ita kuwa babu lokacin da ko tuna shi idan tayi sai taji matsananciyar kunya kamar farkon haduwarsu a falon Mama. Fuskarta da alamun bacci ga kai a aske. Bayanta ya biyo yana cewa ta saurare shi ita kuwa ta ki suna dariya wata mai aiki ta kaisu falon da Yousuf da Arifah suke baje kolin soyayya suna jiransu.
Arifah rungume Radhiya tayi suna murna sannan ta ja hannunta zuwa dakinta inda wata mai kwalliya take jiransu. Jaka ce guda biyu iri daya sai dai kala da ta bambanta Arifah ta mika mata farar ita kuma ta dauki cream.
"Ga kayan da zamu saka kuma an nanata min yadda suke a jere har kasa haka zamu rinka dauka" tace tana murmushin yadda suka yi da Yousuf kafin zuwan su Awwab.
"Ina mamakin yaushe suka sayi kayan da dinki" cewar Radhiya.
"Nima tambayar da nayi kenan. Amma wurin telan nan da muka kaiwa dinkin biki suka kai. Yanzu dai tashi mu shirya"
"Muje na fara gashe da Mom tukunna"
"Tun safe ta fita maybe ta dawo kafin mu gama"
Kayan saman suka fara daukowa tare da fadawa mai kwalliyar kada tayi musu heavy make up. Atampa ce ja da zanen fulawa manya navy blue anyi musu riga da skirt fitted a cikin kayan akwai dan karamin kwalin fashion sarka da dankunne ja sai mayafansu kashka mai stones navy blue. Kowacce cikinsu ta kasa boye farincikinta suna murna kai kace yara ne. Duka kayan da mahadinsu na mayafi da sarka. Babu bata lokaci aka tsara musu kwalliya kowacce tayi kyau. Daurinsu ma iri daya ne mai hawa hawa su ka dora mayafan a kafadunsu.
Ga mamakinsu Awwab da Yousuf suna sanye da blue jeans da red shirt mai dogon hannu. Radhiya dai hawaye take neman yi saboda yadda Awwab yayi surprising dinta yayi matukar burgeta da shiga rai.
Mai hoto yace idan sun shirya shima fa ya shirya. Hotuna suka yi sosai kowanne couple sunyi su kadai sannan anyi musu tare. Kayansu na biyu shadda ce ta matan orange ta mazan kuma combination din orange da fari sun sha hula. Nan ma kamar wancan kowa yayi da matarsa sannan sunyi tare. Sai kaya na uku matan lace doguwar riga anyi aiki a gaban na mazan ma irinsa ne dinkin yarbawa harda hularsu. Wannan gudunmawar Raji ce mijin Zahra kayan sun amshi kowa aka yi hotuna ana zolayar juna. Kayan karshe abaya ce hadaddiyya kowa ya nemi kalar da matarsa tafi so amma design iri daya. Na Radhiya light green na Arifah light purple (lilac). Ango Awwab yasa yadi irin mai shara sharan nan light green amma babu hula shi kuma Yousuf lilac. Idan ka kansu kamar kada ka dauke ido. Sunyi matukar kyau aka karasa musu hotunan Yousuf ya nanatawa mai hoton zasu zo da daddare su nuna masa hotunan da su ka zaba da kuma jerin yadda suke son ayi musu slide show din.
Ko a nan kawai amaren sun san mazansu sun karramasu sun nuna musu soyayya. A daki Arifah take fadawa Radhiya abinda Dad dinta yake yawan fada mata tun bayan da aka daura auren.
"Akwai ranar da zaki ji wai me ya sameki ne kika rasa mijin aure sai wane saboda kawai ya bata miki rai. Shima watarana zaiji kamar ya rufeki da duka don takaicin wani abu da kika yi ba daidai ba. A irin wannan lokacin babu abinda ke rike igiyar aure kamar idan kuka tuna memorable moments din da kuka gina lokacin ganiyar soyayya. Saboda haka kowa ya sami dama yayi kokarin nunawa dayan cewa they are special"
Radhiya ta jinjina kai tace "Sis to mu me zamuyi musu?"
"Ki bari a gama biki yanzu dai sunyi mana one-zero."
Wayar Awwab ta katsesu Radhiya tayi hanzarin mayar da kayan da tazo dasu ta dauki jakar kayanta ta sauka. Abinci aka gabatar musu wanda Arifah tasa aka shirya amma kunya ta hanasu ci. Plate Awwab ya samu ya zuba musu shi da Radhiya ya rike hannunta su ka koma wurin wasu kujera daga can gefe guda. Yousuf yace masa ya kyauta dama bashi da niyar barin Arifah ta tashi bata ci komai ba.
Yadda suka saba kama-kama da spoon daya Awwab da Radhiya suka yi a haka aka ci abincin sannan suka tafi tare da Yousuf ya sauketa a gida.
***********
Ana saura kwana biyu fara events din Jos wanda kowa zaije banda Radhiya ance itama amarya ce. Tayi magiyar har Awwab ta roka yace tayi hakuri ba yinsa bane amma idan ta shirya ya kama musu masauki shi da ita sai su tafi tare. Da jin haka tasan hakuri ya zame mata dole ta gama rigimarta da shagwaba ta sallama. Sai gashi Zayyana da Rahima suka ce mata zasu zauna da ita su ma sun fasa zuwa. Ummi kuwa tace basu isa ba ya zama dole a karrama iyalin Excellency. To karshe dai Fauziyya ce ta fake da laulayi ta zauna tunda kwana biyu ne zasu yi kuma dai ba son tafiyar take ba. An gama wannan shawarar washegari ya kama ranar da za'a mayar da Rahima asibiti. Ido ya sace kamar bashi ba amma kuma yana ta ruwa.
Ummi ta shirya zasu tafi da Emzee da Ibrahim shiru bata sauko ba Emzee ya hau sama kiranta. A falon saman ya ganta zaune akan kujera ta dafe kai tare da runtse idanu.
"Ummi..." yace a tsorace ganin tana ta runtse ido "baki da lafiya ne?"
Hannunta ta dago masa tana son ya taimaka mata ta tashi "tun dazu nake jiran wani ya hawo, taimaka ka mayar dani daki jiri ke dibata sosai"
Da taimakonsa ta karasa dakin da kyar kanta yana ta juyawa kuma ta kafe bazata bisu asibitin ba wai stress ne kawai da rashin zama.
"Kaje ka kai min yarinyata a duba mata idon nan idan kun dawo sai ku karbo sakon nan da na fada maka wanda zamu tafi dashi Jos gobe"
Ba haka yaso ba don har Daada ya kira a waya ya fada masa. Sanin halinta na kin asibiti yace su tafi da Rahiman ya kusa tasowa zai kaita da kansa.
Yana saukowa ya nemi Ibrahim ya rasa. Can ya hango shi da Zayyana suna hira an nutse a cikin soyayya. Tsaki yaja tuni ya dawo daga rakiyar 'yan mata. Zayyana ya tura ta kira Rahima su tafi Ibrahim ya kyabe baki
"Ni dai gaskiya babu inda zata je ka kira wayarta mana ko kaje ka kirata da kanka. Dawo ki zauna kinji"
Emzee ya rike haba "ashe da gaske akwai ranar da zan ga kana tale baki? Kanwata kiyi a hankali kada ya fiki iyawa a kasa gane wace Zayyana waye Ibrahim"
"Banda abinka ga Zayyanan ai" Ibrahim ya nuna kansa sannan ya nuna Zayyana yace "ga Ibrahim".
Murmushi tayi tana jin kunya ta je kiran Rahima. Dama a shirye take gudun bacin rai daga Emzee yasa tayi zamanta sai Ummi ta sauko. Lokacin da ya fadawa Radhiya Ummin bata jindadi tana daki bata sani ba. Zayyana tace bazata bisu ba saboda anyi printing takardunta na admission da ta samu a Nile University akwai wuraren da zata cike Mami zata turo dreba a karba. Ibrahim kememe yaki bin Emzee da yaji haka.
"Kuje ku dawo Zee-zee ina jiranka a nan" ya nuna inda yake zaune.
Haushi ya kama shi kuwa saboda ganin yanzu su biyu ne kadai zasu shiga motar. Gaba tayi nufin shiga tunda su kadai ne yace "koma baya".
Bayan ta zaga ta zauna abinta batare da tayi masa magana ba. Yana zama ya kula kamar mudubinsa a saitin fuskarta yake don duk motsinta yana gani maimakon ya hango titi.
"Koma gefe" ya umarceta.
Gefen ta koma ta rakube zuciyarta tana zafi. Ba komai yake damunta ba sai rashin sanin aihinin abinda tayi masa wanda ya bata masa rai har yake mata haka. A gaban mutane bama ya shiga shirginta sai ya zama dole. Idan su kadai ne kuma dalili ya janyo sai yayi mata magana to ba mai dadi yake yi ba. Ba karamin azabtuwa yake da yin hakan ba domin kuwa har yanzu ya kasa rabata da matsayin da ya bata na Rahiman Muhammad. Ga tausayinta da yake dawainiya dashi saboda ciwon idonta.
Ko tari taki yi a motar ya kunna karatun Qur'ani kira'ar Mishary Rashid Al-Afasy cikin suratul Kahf. Da kadan da kadan yake jin tashin muryarta tana bin karatun a hankali sai ya sami kansa da rage volume batare da tayi la'akari ba. Idanunta a rufe sai dai lokaci lokaci tana sanya tissue ta goge ruwan da yake fitowa kamar hawaye daga dayan idon nata. Bakinta yake bi da kallo ta mudubi can cikin zuciyarsa yace "Rahima".
Wani mugun horn yaji yayi saurin kallon gabansa tare da taka burki da karfi kadan ya rage ya dokawa motar gabansa. Rahima ta bude ido da sauri ya juyo suka hada ido sai harara yake maka mata.
"Wato ta nan kika bullo kuma? Bari mu koma gida addu'a zan ce Ummi ta rinka yi min saboda na fuskanci abin naki da gaske ne."
Bata fahimci me yake nufi ba shi kuwa bai fasa cewa zai tsananta addu'a ba wai tunda an biyo ta can asirinsu ya tono shine ake neman sake tafiyar da tunaninsa gashi daga kallonta ta mirror ya kusa yin accident. Idan ka ga yadda yake fadan abin dariya kuma ya kasa hakura da kallonta ta mirror din. Sun kusa isa asibitin yayi parking a gefen hanya saboda abin ya ishe shi yace ta dawo gaba. Ita dai bata da ta cewa sai fatan idan ma wata lalurar ya gamu da ita da ta janyo masa chanja halaye Allah Ya yaye masa. Yanzu ta dena jin haushinsa sam sai tausayi.
Arifah rungume Radhiya tayi suna murna sannan ta ja hannunta zuwa dakinta inda wata mai kwalliya take jiransu. Jaka ce guda biyu iri daya sai dai kala da ta bambanta Arifah ta mika mata farar ita kuma ta dauki cream.
"Ga kayan da zamu saka kuma an nanata min yadda suke a jere har kasa haka zamu rinka dauka" tace tana murmushin yadda suka yi da Yousuf kafin zuwan su Awwab.
"Ina mamakin yaushe suka sayi kayan da dinki" cewar Radhiya.
"Nima tambayar da nayi kenan. Amma wurin telan nan da muka kaiwa dinkin biki suka kai. Yanzu dai tashi mu shirya"
"Muje na fara gashe da Mom tukunna"
"Tun safe ta fita maybe ta dawo kafin mu gama"
Kayan saman suka fara daukowa tare da fadawa mai kwalliyar kada tayi musu heavy make up. Atampa ce ja da zanen fulawa manya navy blue anyi musu riga da skirt fitted a cikin kayan akwai dan karamin kwalin fashion sarka da dankunne ja sai mayafansu kashka mai stones navy blue. Kowacce cikinsu ta kasa boye farincikinta suna murna kai kace yara ne. Duka kayan da mahadinsu na mayafi da sarka. Babu bata lokaci aka tsara musu kwalliya kowacce tayi kyau. Daurinsu ma iri daya ne mai hawa hawa su ka dora mayafan a kafadunsu.
Ga mamakinsu Awwab da Yousuf suna sanye da blue jeans da red shirt mai dogon hannu. Radhiya dai hawaye take neman yi saboda yadda Awwab yayi surprising dinta yayi matukar burgeta da shiga rai.
Mai hoto yace idan sun shirya shima fa ya shirya. Hotuna suka yi sosai kowanne couple sunyi su kadai sannan anyi musu tare. Kayansu na biyu shadda ce ta matan orange ta mazan kuma combination din orange da fari sun sha hula. Nan ma kamar wancan kowa yayi da matarsa sannan sunyi tare. Sai kaya na uku matan lace doguwar riga anyi aiki a gaban na mazan ma irinsa ne dinkin yarbawa harda hularsu. Wannan gudunmawar Raji ce mijin Zahra kayan sun amshi kowa aka yi hotuna ana zolayar juna. Kayan karshe abaya ce hadaddiyya kowa ya nemi kalar da matarsa tafi so amma design iri daya. Na Radhiya light green na Arifah light purple (lilac). Ango Awwab yasa yadi irin mai shara sharan nan light green amma babu hula shi kuma Yousuf lilac. Idan ka kansu kamar kada ka dauke ido. Sunyi matukar kyau aka karasa musu hotunan Yousuf ya nanatawa mai hoton zasu zo da daddare su nuna masa hotunan da su ka zaba da kuma jerin yadda suke son ayi musu slide show din.
Ko a nan kawai amaren sun san mazansu sun karramasu sun nuna musu soyayya. A daki Arifah take fadawa Radhiya abinda Dad dinta yake yawan fada mata tun bayan da aka daura auren.
"Akwai ranar da zaki ji wai me ya sameki ne kika rasa mijin aure sai wane saboda kawai ya bata miki rai. Shima watarana zaiji kamar ya rufeki da duka don takaicin wani abu da kika yi ba daidai ba. A irin wannan lokacin babu abinda ke rike igiyar aure kamar idan kuka tuna memorable moments din da kuka gina lokacin ganiyar soyayya. Saboda haka kowa ya sami dama yayi kokarin nunawa dayan cewa they are special"
Radhiya ta jinjina kai tace "Sis to mu me zamuyi musu?"
"Ki bari a gama biki yanzu dai sunyi mana one-zero."
Wayar Awwab ta katsesu Radhiya tayi hanzarin mayar da kayan da tazo dasu ta dauki jakar kayanta ta sauka. Abinci aka gabatar musu wanda Arifah tasa aka shirya amma kunya ta hanasu ci. Plate Awwab ya samu ya zuba musu shi da Radhiya ya rike hannunta su ka koma wurin wasu kujera daga can gefe guda. Yousuf yace masa ya kyauta dama bashi da niyar barin Arifah ta tashi bata ci komai ba.
Yadda suka saba kama-kama da spoon daya Awwab da Radhiya suka yi a haka aka ci abincin sannan suka tafi tare da Yousuf ya sauketa a gida.
***********
Ana saura kwana biyu fara events din Jos wanda kowa zaije banda Radhiya ance itama amarya ce. Tayi magiyar har Awwab ta roka yace tayi hakuri ba yinsa bane amma idan ta shirya ya kama musu masauki shi da ita sai su tafi tare. Da jin haka tasan hakuri ya zame mata dole ta gama rigimarta da shagwaba ta sallama. Sai gashi Zayyana da Rahima suka ce mata zasu zauna da ita su ma sun fasa zuwa. Ummi kuwa tace basu isa ba ya zama dole a karrama iyalin Excellency. To karshe dai Fauziyya ce ta fake da laulayi ta zauna tunda kwana biyu ne zasu yi kuma dai ba son tafiyar take ba. An gama wannan shawarar washegari ya kama ranar da za'a mayar da Rahima asibiti. Ido ya sace kamar bashi ba amma kuma yana ta ruwa.
Ummi ta shirya zasu tafi da Emzee da Ibrahim shiru bata sauko ba Emzee ya hau sama kiranta. A falon saman ya ganta zaune akan kujera ta dafe kai tare da runtse idanu.
"Ummi..." yace a tsorace ganin tana ta runtse ido "baki da lafiya ne?"
Hannunta ta dago masa tana son ya taimaka mata ta tashi "tun dazu nake jiran wani ya hawo, taimaka ka mayar dani daki jiri ke dibata sosai"
Da taimakonsa ta karasa dakin da kyar kanta yana ta juyawa kuma ta kafe bazata bisu asibitin ba wai stress ne kawai da rashin zama.
"Kaje ka kai min yarinyata a duba mata idon nan idan kun dawo sai ku karbo sakon nan da na fada maka wanda zamu tafi dashi Jos gobe"
Ba haka yaso ba don har Daada ya kira a waya ya fada masa. Sanin halinta na kin asibiti yace su tafi da Rahiman ya kusa tasowa zai kaita da kansa.
Yana saukowa ya nemi Ibrahim ya rasa. Can ya hango shi da Zayyana suna hira an nutse a cikin soyayya. Tsaki yaja tuni ya dawo daga rakiyar 'yan mata. Zayyana ya tura ta kira Rahima su tafi Ibrahim ya kyabe baki
"Ni dai gaskiya babu inda zata je ka kira wayarta mana ko kaje ka kirata da kanka. Dawo ki zauna kinji"
Emzee ya rike haba "ashe da gaske akwai ranar da zan ga kana tale baki? Kanwata kiyi a hankali kada ya fiki iyawa a kasa gane wace Zayyana waye Ibrahim"
"Banda abinka ga Zayyanan ai" Ibrahim ya nuna kansa sannan ya nuna Zayyana yace "ga Ibrahim".
Murmushi tayi tana jin kunya ta je kiran Rahima. Dama a shirye take gudun bacin rai daga Emzee yasa tayi zamanta sai Ummi ta sauko. Lokacin da ya fadawa Radhiya Ummin bata jindadi tana daki bata sani ba. Zayyana tace bazata bisu ba saboda anyi printing takardunta na admission da ta samu a Nile University akwai wuraren da zata cike Mami zata turo dreba a karba. Ibrahim kememe yaki bin Emzee da yaji haka.
"Kuje ku dawo Zee-zee ina jiranka a nan" ya nuna inda yake zaune.
Haushi ya kama shi kuwa saboda ganin yanzu su biyu ne kadai zasu shiga motar. Gaba tayi nufin shiga tunda su kadai ne yace "koma baya".
Bayan ta zaga ta zauna abinta batare da tayi masa magana ba. Yana zama ya kula kamar mudubinsa a saitin fuskarta yake don duk motsinta yana gani maimakon ya hango titi.
"Koma gefe" ya umarceta.
Gefen ta koma ta rakube zuciyarta tana zafi. Ba komai yake damunta ba sai rashin sanin aihinin abinda tayi masa wanda ya bata masa rai har yake mata haka. A gaban mutane bama ya shiga shirginta sai ya zama dole. Idan su kadai ne kuma dalili ya janyo sai yayi mata magana to ba mai dadi yake yi ba. Ba karamin azabtuwa yake da yin hakan ba domin kuwa har yanzu ya kasa rabata da matsayin da ya bata na Rahiman Muhammad. Ga tausayinta da yake dawainiya dashi saboda ciwon idonta.
Ko tari taki yi a motar ya kunna karatun Qur'ani kira'ar Mishary Rashid Al-Afasy cikin suratul Kahf. Da kadan da kadan yake jin tashin muryarta tana bin karatun a hankali sai ya sami kansa da rage volume batare da tayi la'akari ba. Idanunta a rufe sai dai lokaci lokaci tana sanya tissue ta goge ruwan da yake fitowa kamar hawaye daga dayan idon nata. Bakinta yake bi da kallo ta mudubi can cikin zuciyarsa yace "Rahima".
Wani mugun horn yaji yayi saurin kallon gabansa tare da taka burki da karfi kadan ya rage ya dokawa motar gabansa. Rahima ta bude ido da sauri ya juyo suka hada ido sai harara yake maka mata.
"Wato ta nan kika bullo kuma? Bari mu koma gida addu'a zan ce Ummi ta rinka yi min saboda na fuskanci abin naki da gaske ne."
Bata fahimci me yake nufi ba shi kuwa bai fasa cewa zai tsananta addu'a ba wai tunda an biyo ta can asirinsu ya tono shine ake neman sake tafiyar da tunaninsa gashi daga kallonta ta mirror ya kusa yin accident. Idan ka ga yadda yake fadan abin dariya kuma ya kasa hakura da kallonta ta mirror din. Sun kusa isa asibitin yayi parking a gefen hanya saboda abin ya ishe shi yace ta dawo gaba. Ita dai bata da ta cewa sai fatan idan ma wata lalurar ya gamu da ita da ta janyo masa chanja halaye Allah Ya yaye masa. Yanzu ta dena jin haushinsa sam sai tausayi.