Sashe 14
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin abu take ji yana mata yawo a jikinta. Idan a da tana tunanin tana son mijinta to a yau sonsa yana neman ranta ne. Gani take kamar bazata iya jurar rashinsa a tare da ita ko da na kwana daya bane. Ashe baka sanin mahimmancin abun da ka ke dashi sai yayi nisa da kai. Bata san lokacin da bacci ya dauketa ba sai ajiyar zuciya da take ta saukewa.
Sai da ya tabbatar tayi bacci ya tashi ya dauro alwala. Yasan yaudarar kansa zaiyi idan yace zaiyi bacci a wannan daren. Nan da kwana biyar zasu bar kasar, zai bar iyalinsa wanda basu dogara da kowa ba sai Allah sai kuma shi da nauyinsu yake wuyansa. Yayi nafila raka'a goma tare da witri sannan ya zauna yana jero addu'o'i. Motsin Radhiya yaji yayi saurin fita da ita daga dakin don kada ta tashi Mairam yaje ya hada mata tea a feeder ta shanye. Yana jiran ta koma bacci yarinya ido ya soye ta fara kiriniya. Bata tafiya sai rarrafe da mikewa. Biye mata yayi suna wasan. Sai gabanin asuba ta bingire a jikinsa tayi bacci. Kan ta ya rinka shafawa baiyi zato ba sai hawaye ya ziraro masa ya goge da sauri yana baiwa zuciyarsa hakurin cewa wata uku a wurin Allah kamar kiftawar ido zasu zo su wuce.
**********
Gidan Hadir ma basuyi bacci ba don Zainab kwana tayi kuka. Mami da sauki tunda ba zuwan Major na farko wurin rikici ko yaki kenan ba. Sai dai itanma kukan tayi don ba'a sabo da rabuwa.
Washegari harabar gidajen nasu kaf babu wata hayaniyar kirki. Sojoji ashirin ne zasu tafi a cikin magidantan da suke wurin. Kowa yana gida tare da iyalinsa.
Bayan la'asar Zayyan ya dauki Mairam su ka je gidansu da gidan kawunansa da Mal Aminu ya fada musu zaiyi tafiya. Kowa yayi masa addua da fatan alkhairi ban da Jume da bata dena jin zafin rashin basu kudi ba. Duk da haka ya yi musu kyauta ita da su Maikudi tunda sunyi aure. Matan ma a ranar sai da ya kai musu ziyara.
Sukuku su Mairam su ka koma babu walwala a tare dasu ita da Zainab. Mami ce tayi musu fada akan idan sun cigaba da haka a wane yanayi suke so mazajensu su tafi. Sun ji maganarta don kowacce sai da tayi kokarin gyarawa. Mairam dambun nama ta yiwa Zayyan gari guda sai da ya dibarwa Hadir da Major. Ta kuma saki jiki tana bashi kulawa fiye da yadda ta saba.
Sauran kwana biyu su tafi tana goge masa khakinsa Radhiya ta fito daga daki da kafafunta a hankali saboda rashin kwarin tafiyar. Murna ta kama Zayyan ya sunkuceta yana sumbatar kumatunta.
" 'Yar soja ta girma, yau yawo zamu je tunda anyi kafa"
Kamar taji me yace ta rinka bangala dariya. Ajiyeta yayi zai chanja kaya su fita tasa masa kuka "Daaadaa" yaji tace tana dago masa hannuwa.
A nutse ya juyo ya tabbatar shi take kira. Har yanzu hannuwanta take miko masa "Daaadaa". Ya kalli Mairam ita ma mamakin yarinyar ya kamata. Awwab bashi da aiki sai koya mata Ummi da Daddy wai dole sai tayi magana. Yau gashi ta kira mahaifinta dadi yasa yaji idonsa na alamun zafin kwalla. Daukanta yayi ya shiga dakin su ka bar Mairam tana guga tana diga masa hawaye a kayansa.
Ranar ashirin da daya ga watan Mayu na 1993 ne Giginya Barrack dake cikin garin Sakkwato ta kwashi sojojinta za'a kaisu Lagos washegari su tashi zuwa Liberia ta ruwa.
Daren ranar ya kasance dare na soyayya, jaddada alkawura da kuma sabunta matsayi a zukatan su Zayyan da iyalansu. Daga shi har Mairam babu wanda ya runtsa kuma hakan take a wurin Hadir da Zainab da Major kansa da Mami.
Komai Mairam ce ta yiwa Zayyan hatta abinci a baki take bashi. Tayi ta daurewa kada tayi kuka zuciyarta ta kasa daukan wannan lamari. Ko kadan baya son nuna mata damuwar da yake ciki shiyasa ya fake da yiwa Radhiya wasa.
Jiniya mai sanar da su fito ce tayi kara sai da cikin Mairama ya murda kawai ta fashe da kuka iya karfinta.
"Zayyan"
Tashi yayi ya rungumeta tsam a jikinsa "ashe kin iya fadin suna na"
"Ka ajiye aikin nan mu koma Nijar ko kiwo ka rinka yi"
Fuskarta ya zagaye a tsakiyar tafukan hannunsa.
"I love you Maryam Ali Gidado. Ki rike wannan a zuciyarki har na dawo. Nayi miki ajiya a kan mudubi idan na tafi ki duba"
Hade bakinsu yayi tamkar ranar su ka fara haduwa yana jin karar jiniyar a karo na biyu ya saketa ya dauki Radhiya.
"Ki tayani kula da Umminki da baby kinji mamana."
"Daaadaa" tace tana washe hakoranta biyu dimple dinta ya lotsa ciki sosai.
Ita ma ya sumbaci kuncinta hagu da dama kafin Mairam ta farga ya fice daga gidan.[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Daga tashar jirgin ruwa ta Apapa da ke dake Lagos su Zayyan zasu tashi a jirgin ruwa zuwa babban birnin Liberia wato Monrovia. Akan tekun Atlantika jirgin nasu ya dau hanya sai da suka wuce Benin republic wadda mu ka fi sani da Cotounou, sai Togo, Ghana, Cote d'voire sannan Allah Ya saukesu a kasar da rikici na cikin gida ya kaurewa tun shekarar 1989.
Motocin yaki aka turo domin daukarsu. Zayyan da Hadir zuwansu sansanin yaki irin wannan na farko kenan. Major Mustapha yazo ne a matsayin babban soja don ba wuri daya zasu zauna ba. Shi Computer Engineer ne saboda haka aikinsa yafi karfi ne daga bayan fage musamman da a wannan lokacin babu masu karatu irin nasa da yawa saboda karancin kayan aiki.
Cikin garuruwa ko kauyuka da rikicin yafi shafa ake watsa sojojin. Sune suke kwantar da tarzoma da fitina idan ta taso a tsakanin mazauna garin da kuma 'yan tawaye.
Ranar farko su Zayyan da sauran da su ka zo tare da yawansu basu iya rintsawa ba. Daki ne kato kowa da yalolowar katifarsa akan gadon karfe mai hawa biyu. Wasu kuma a kasa katifunsu suke saboda rashin wadatar gadajen. Zayyan da Hadir a kusa da juna suka shimfida katifun da aka basu. Shi dai tunanin Mairama da Radhiya yake yi. Ko me sukeyi a wannan lokaci? Tafiyar Radhiya ta kara kwari a kwanakin da suka shafe a kan ruwa? Idan ya koma zata yi masa kyuya? Gajeren tsaki yayi da wannan tunanin. Burinsa ace kowane mataki na rayuwar 'yarsa ya faru a kan idanunsa.
Hadir yace "kaima ka kasa bacci ko?"
"Yadda ka san nayi tsuntsuwa naje na gansu na dawo" yayi maganar cike da kewa.
Muskutawa Hadir yayi ya gyara kwanciyarsa. Shi kuma Zayyan yayi rub da ciki ya rike fuskarsa a tafukan hannunsa da ya tokare kansa dasu.
"Bansan yaya Zainab take yi da Ibrahim ba yanzu. Kusan wata guda yaron nan ba ya iya bacci sai akan kirjina"
Dariya Zayyan yayi "kace akwai daru, don ma bai kai Alheran rigima ba abin zai zo da sauki."
Wani cikin wadanda suka tarar a sansanin yana daga gefe yana jin hirarsu ya soma dariya "kusan kowa ranar farko sai yayi hirar gida"
Gwangwani ya dauka a kusa da shi ya bubbuga da hancin katuwar bindigarsa. Sai ga sojoji suna tashi zaune wasu akan gado wasu a katifa. Kalilan ne masu bacci. Mutumin yace "kunga yau anyi baki ku tashi mu san juna." Ya kalli bangaren da yawancin bakin nasu suke "babu wani abin debe kewa a wurin nan sai hira da muke samun yi da juna cikin dare"
Na kan gado na dirowa na kasa na matsawa sai gasu sunyi da'ira sun zagaye katifar wanda yayi maganar. Da gani zai girmi da yawansu. Kallonsa ya ga suna yi ya kada kafada.
"Ok, ok ni zan fara"
Ihu wasu suka fara su Zayyan dai abin duka sabo ya zame musu. Duk wata hayaniya sun saba da ita a irin training da suke zuwa. Amma wannan karon fa a filin yaki suke tare da sojojin wasu barracks din da basu taba haduwa ba. Muryar mutumin yaji ya soma magana.
"Nine shugabanku a harkar abinci" sai sowa da tafi yayi murmushi "Chief cook kuke gani. Suna na Captain Ogbonna Odili. Ina da mata Mabel da yara hudu a Enugu. Ogechi, Uloma, Nneka da Kachiku muna kiransa Kachi. Kamar kowa a nan ina matukar son family dina. Musamman ma Uloma saboda tana da kokari sosai a school. Yanzu zaka rubuta mata abu indai ta karance shi daga farko zuwa karshe to ya gama zama. Da kuke ganina kudi nake nema domin na kaita wata babbar makaranta a garinmu ta gifted children. Uloma is born to be a great doctor"
"So shall it beeeee" wasu suka amsa da ihunsu na sojoji. Capt. Ogbonna yana ta dariya ya cigaba da hirar iyalinsa ana tayashi murna.
Bayan shi sai aka ce mutum daya cikin newcomers ya gabatar da kansa. Papa Dolapo ne ya fara shima yana bayani ana dariya da kuma nuna tausayi musamman da yace ya baro matarsa da tsohon ciki suna jinjina masa.
Zayyan sai ya tuna cikin jikin tasa matar ya daga hannu "I am next please, please"
Dariya suka sa ana tsokanarsa ya dake yana basu labarin Mairama da Radhiya "babban farincikina kafin na taho Alheran ta iya kiran suna na"
"Fada mana ya take cewa" wani yace sauran na goya masa baya.
"Daaadaa"
Ihunsu ya karade dakin masu baccin ma sun tashi anayi dasu.
"Kuma nima matata tana da ciki amma sai mun koma zata haihu In sha Allah. Sorry Papa Dolapo kaine za'ayi ba kai"
Hadir yayi dariya yana cewa Zayyan yayi masa wayo "muna komawa da wata tara zaka ji Zainab ta haihu"
Tafawa suka yi wani mutumin Adamawa Austin Bakari dan kabilar Chamba ya fara bada labarin iyayensa tsofaffi wanda sun dora duk wani buri nasu akan cigabansa. Labarin iyayen nasa akwai ban tausayi domin dukkansu guragu ne da basu da mataimaki sai shi kadai. Dan albashin nasa shine cinsu shine shansu. Ya sanya sauran cikin yanayi na jimami kowa na fadin albarkacin bakinsa sai su ka ji wata muguwar kara mai razanarwa.
Sai da ya tabbatar tayi bacci ya tashi ya dauro alwala. Yasan yaudarar kansa zaiyi idan yace zaiyi bacci a wannan daren. Nan da kwana biyar zasu bar kasar, zai bar iyalinsa wanda basu dogara da kowa ba sai Allah sai kuma shi da nauyinsu yake wuyansa. Yayi nafila raka'a goma tare da witri sannan ya zauna yana jero addu'o'i. Motsin Radhiya yaji yayi saurin fita da ita daga dakin don kada ta tashi Mairam yaje ya hada mata tea a feeder ta shanye. Yana jiran ta koma bacci yarinya ido ya soye ta fara kiriniya. Bata tafiya sai rarrafe da mikewa. Biye mata yayi suna wasan. Sai gabanin asuba ta bingire a jikinsa tayi bacci. Kan ta ya rinka shafawa baiyi zato ba sai hawaye ya ziraro masa ya goge da sauri yana baiwa zuciyarsa hakurin cewa wata uku a wurin Allah kamar kiftawar ido zasu zo su wuce.
**********
Gidan Hadir ma basuyi bacci ba don Zainab kwana tayi kuka. Mami da sauki tunda ba zuwan Major na farko wurin rikici ko yaki kenan ba. Sai dai itanma kukan tayi don ba'a sabo da rabuwa.
Washegari harabar gidajen nasu kaf babu wata hayaniyar kirki. Sojoji ashirin ne zasu tafi a cikin magidantan da suke wurin. Kowa yana gida tare da iyalinsa.
Bayan la'asar Zayyan ya dauki Mairam su ka je gidansu da gidan kawunansa da Mal Aminu ya fada musu zaiyi tafiya. Kowa yayi masa addua da fatan alkhairi ban da Jume da bata dena jin zafin rashin basu kudi ba. Duk da haka ya yi musu kyauta ita da su Maikudi tunda sunyi aure. Matan ma a ranar sai da ya kai musu ziyara.
Sukuku su Mairam su ka koma babu walwala a tare dasu ita da Zainab. Mami ce tayi musu fada akan idan sun cigaba da haka a wane yanayi suke so mazajensu su tafi. Sun ji maganarta don kowacce sai da tayi kokarin gyarawa. Mairam dambun nama ta yiwa Zayyan gari guda sai da ya dibarwa Hadir da Major. Ta kuma saki jiki tana bashi kulawa fiye da yadda ta saba.
Sauran kwana biyu su tafi tana goge masa khakinsa Radhiya ta fito daga daki da kafafunta a hankali saboda rashin kwarin tafiyar. Murna ta kama Zayyan ya sunkuceta yana sumbatar kumatunta.
" 'Yar soja ta girma, yau yawo zamu je tunda anyi kafa"
Kamar taji me yace ta rinka bangala dariya. Ajiyeta yayi zai chanja kaya su fita tasa masa kuka "Daaadaa" yaji tace tana dago masa hannuwa.
A nutse ya juyo ya tabbatar shi take kira. Har yanzu hannuwanta take miko masa "Daaadaa". Ya kalli Mairam ita ma mamakin yarinyar ya kamata. Awwab bashi da aiki sai koya mata Ummi da Daddy wai dole sai tayi magana. Yau gashi ta kira mahaifinta dadi yasa yaji idonsa na alamun zafin kwalla. Daukanta yayi ya shiga dakin su ka bar Mairam tana guga tana diga masa hawaye a kayansa.
Ranar ashirin da daya ga watan Mayu na 1993 ne Giginya Barrack dake cikin garin Sakkwato ta kwashi sojojinta za'a kaisu Lagos washegari su tashi zuwa Liberia ta ruwa.
Daren ranar ya kasance dare na soyayya, jaddada alkawura da kuma sabunta matsayi a zukatan su Zayyan da iyalansu. Daga shi har Mairam babu wanda ya runtsa kuma hakan take a wurin Hadir da Zainab da Major kansa da Mami.
Komai Mairam ce ta yiwa Zayyan hatta abinci a baki take bashi. Tayi ta daurewa kada tayi kuka zuciyarta ta kasa daukan wannan lamari. Ko kadan baya son nuna mata damuwar da yake ciki shiyasa ya fake da yiwa Radhiya wasa.
Jiniya mai sanar da su fito ce tayi kara sai da cikin Mairama ya murda kawai ta fashe da kuka iya karfinta.
"Zayyan"
Tashi yayi ya rungumeta tsam a jikinsa "ashe kin iya fadin suna na"
"Ka ajiye aikin nan mu koma Nijar ko kiwo ka rinka yi"
Fuskarta ya zagaye a tsakiyar tafukan hannunsa.
"I love you Maryam Ali Gidado. Ki rike wannan a zuciyarki har na dawo. Nayi miki ajiya a kan mudubi idan na tafi ki duba"
Hade bakinsu yayi tamkar ranar su ka fara haduwa yana jin karar jiniyar a karo na biyu ya saketa ya dauki Radhiya.
"Ki tayani kula da Umminki da baby kinji mamana."
"Daaadaa" tace tana washe hakoranta biyu dimple dinta ya lotsa ciki sosai.
Ita ma ya sumbaci kuncinta hagu da dama kafin Mairam ta farga ya fice daga gidan.[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Daga tashar jirgin ruwa ta Apapa da ke dake Lagos su Zayyan zasu tashi a jirgin ruwa zuwa babban birnin Liberia wato Monrovia. Akan tekun Atlantika jirgin nasu ya dau hanya sai da suka wuce Benin republic wadda mu ka fi sani da Cotounou, sai Togo, Ghana, Cote d'voire sannan Allah Ya saukesu a kasar da rikici na cikin gida ya kaurewa tun shekarar 1989.
Motocin yaki aka turo domin daukarsu. Zayyan da Hadir zuwansu sansanin yaki irin wannan na farko kenan. Major Mustapha yazo ne a matsayin babban soja don ba wuri daya zasu zauna ba. Shi Computer Engineer ne saboda haka aikinsa yafi karfi ne daga bayan fage musamman da a wannan lokacin babu masu karatu irin nasa da yawa saboda karancin kayan aiki.
Cikin garuruwa ko kauyuka da rikicin yafi shafa ake watsa sojojin. Sune suke kwantar da tarzoma da fitina idan ta taso a tsakanin mazauna garin da kuma 'yan tawaye.
Ranar farko su Zayyan da sauran da su ka zo tare da yawansu basu iya rintsawa ba. Daki ne kato kowa da yalolowar katifarsa akan gadon karfe mai hawa biyu. Wasu kuma a kasa katifunsu suke saboda rashin wadatar gadajen. Zayyan da Hadir a kusa da juna suka shimfida katifun da aka basu. Shi dai tunanin Mairama da Radhiya yake yi. Ko me sukeyi a wannan lokaci? Tafiyar Radhiya ta kara kwari a kwanakin da suka shafe a kan ruwa? Idan ya koma zata yi masa kyuya? Gajeren tsaki yayi da wannan tunanin. Burinsa ace kowane mataki na rayuwar 'yarsa ya faru a kan idanunsa.
Hadir yace "kaima ka kasa bacci ko?"
"Yadda ka san nayi tsuntsuwa naje na gansu na dawo" yayi maganar cike da kewa.
Muskutawa Hadir yayi ya gyara kwanciyarsa. Shi kuma Zayyan yayi rub da ciki ya rike fuskarsa a tafukan hannunsa da ya tokare kansa dasu.
"Bansan yaya Zainab take yi da Ibrahim ba yanzu. Kusan wata guda yaron nan ba ya iya bacci sai akan kirjina"
Dariya Zayyan yayi "kace akwai daru, don ma bai kai Alheran rigima ba abin zai zo da sauki."
Wani cikin wadanda suka tarar a sansanin yana daga gefe yana jin hirarsu ya soma dariya "kusan kowa ranar farko sai yayi hirar gida"
Gwangwani ya dauka a kusa da shi ya bubbuga da hancin katuwar bindigarsa. Sai ga sojoji suna tashi zaune wasu akan gado wasu a katifa. Kalilan ne masu bacci. Mutumin yace "kunga yau anyi baki ku tashi mu san juna." Ya kalli bangaren da yawancin bakin nasu suke "babu wani abin debe kewa a wurin nan sai hira da muke samun yi da juna cikin dare"
Na kan gado na dirowa na kasa na matsawa sai gasu sunyi da'ira sun zagaye katifar wanda yayi maganar. Da gani zai girmi da yawansu. Kallonsa ya ga suna yi ya kada kafada.
"Ok, ok ni zan fara"
Ihu wasu suka fara su Zayyan dai abin duka sabo ya zame musu. Duk wata hayaniya sun saba da ita a irin training da suke zuwa. Amma wannan karon fa a filin yaki suke tare da sojojin wasu barracks din da basu taba haduwa ba. Muryar mutumin yaji ya soma magana.
"Nine shugabanku a harkar abinci" sai sowa da tafi yayi murmushi "Chief cook kuke gani. Suna na Captain Ogbonna Odili. Ina da mata Mabel da yara hudu a Enugu. Ogechi, Uloma, Nneka da Kachiku muna kiransa Kachi. Kamar kowa a nan ina matukar son family dina. Musamman ma Uloma saboda tana da kokari sosai a school. Yanzu zaka rubuta mata abu indai ta karance shi daga farko zuwa karshe to ya gama zama. Da kuke ganina kudi nake nema domin na kaita wata babbar makaranta a garinmu ta gifted children. Uloma is born to be a great doctor"
"So shall it beeeee" wasu suka amsa da ihunsu na sojoji. Capt. Ogbonna yana ta dariya ya cigaba da hirar iyalinsa ana tayashi murna.
Bayan shi sai aka ce mutum daya cikin newcomers ya gabatar da kansa. Papa Dolapo ne ya fara shima yana bayani ana dariya da kuma nuna tausayi musamman da yace ya baro matarsa da tsohon ciki suna jinjina masa.
Zayyan sai ya tuna cikin jikin tasa matar ya daga hannu "I am next please, please"
Dariya suka sa ana tsokanarsa ya dake yana basu labarin Mairama da Radhiya "babban farincikina kafin na taho Alheran ta iya kiran suna na"
"Fada mana ya take cewa" wani yace sauran na goya masa baya.
"Daaadaa"
Ihunsu ya karade dakin masu baccin ma sun tashi anayi dasu.
"Kuma nima matata tana da ciki amma sai mun koma zata haihu In sha Allah. Sorry Papa Dolapo kaine za'ayi ba kai"
Hadir yayi dariya yana cewa Zayyan yayi masa wayo "muna komawa da wata tara zaka ji Zainab ta haihu"
Tafawa suka yi wani mutumin Adamawa Austin Bakari dan kabilar Chamba ya fara bada labarin iyayensa tsofaffi wanda sun dora duk wani buri nasu akan cigabansa. Labarin iyayen nasa akwai ban tausayi domin dukkansu guragu ne da basu da mataimaki sai shi kadai. Dan albashin nasa shine cinsu shine shansu. Ya sanya sauran cikin yanayi na jimami kowa na fadin albarkacin bakinsa sai su ka ji wata muguwar kara mai razanarwa.