Sashe 24
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk gidajen 'yan uwan Zayyan na jini da makusanta irin su Mal Aminu sai taje. Kuma bata fasa zuwa barikinsu ba ko zata sami labarin Zainab da Mami. Gidan iyayen Zainab yanzu wasu ne a ciki. Ta matsu tasan halin da suke ciki amma babu dama. Haka kuma har yau babu wanda ya kirasu akan wani kudi na ihsani ga jaruman da suka rasu.
Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne.
Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam.
Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu.
Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu.
**********
Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama.
Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba.
Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama.
"Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba"
Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa."
Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta.
Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai.
Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta.
Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta.
***********
Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka.
Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide"
"Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa.
"Habubakari"
"Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa.
Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro.
"Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya"
Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo.
Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba"
Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan"
"Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro"
Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota.
Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo.
"Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne"
Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan"
Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?"
"Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata."
Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi.
Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: WAIWAYE....
Zainab tayi kuka har ta gode Allah. Hadir dinta ne kwance baya iya motsa kowace gaba a jikinsa sannan baya iya magana. Idanunsa kadai ke aiki idan anyi magana kuma yana ji amma babu damar amsawa. Tun iyaye na rarrashinta har suka kyaleta ta koka ko zata ji sa'ida.
Zuwansu Kano kenan aka kaisu tsohon dakinsa inda yake zaman jinya. A hankali ya bude idanunsa ya saukesu a kanta. Murmushi yayi wanda ya hado da zubar hawayensa. Sunanta yake kira amma babu mai jin sautin saboda baya iya motsa harshensa. A guje ta fita da ta ga ya tashi ta dauko Ibrahim yana wasansa a dakin kakarsa. Dakin ta koma dashi ta kama hannun Hadir ta hada da nasa.
"Idan ni bazaka tabani ba ka tashi ka dauki danka. Don Allah...don Allah Hadir ko Ibrahim ne ka rike da kanka"
Runtse idanunsa kawai yayi. Yaya zaiyi da iyalinsa? Allah ne gatan gidansu sai shi da guntun albashinsa. Shikenan rayuwarsa da tasu ta tsaya saboda lalurar da ta same shi? Ina Major Mustapha? Yayi rai ko shima ya rasu? Ina Mairama da Radhiya? Akwai amanar takardun kwafin gidansa a wurinsa. Ta yaya zai isa ga wannan mutane da yake tausayawa duk da halin da yake ciki.
Kanwar Hadir ce ta jiyo Zainab tana surutai ita kadai tazo ta fitar da Ibrahim sannan ta fadawa mamansu halin da take ciki. Tun zuwansu ko ruwa bata sha ba sai kuka. Umman tasu taje har dakin tace mata ta taso ta ci abinci shima ta barshi ya huta. Kamar ba da ita take ba tana ta magana taki tashi sai cewa take ta koshi. Babansu Hadir aka kira shima yazo yace indai kuka zata rinka yi to ta fita daga dakin.
Hannu ta dora a baki da sauri "na dena, wallahi na dena" tana magana hawayenta da na Hadir yana karuwa.
Baban ya fita yana cewa Umma ta kyaleta dama sun sani dole tayi kuka.
Bayan fitarsu hannunsa ta kama tana shafa kumatunta "Hadir kana ji na?"
Jikakkun idanunsa ya kifta mata yana son yin murmushi "kin fiye rigima" yace a ransa.
Shagwabar da ta saba yi masa take kokarin yi kuka yana cin karfinta "ka taimakeni ka tashi, kaga Ibrahim ya kara nauyi yanzu. Ni kadai kake so na rinka daukarsa? So kake ya buda min kirji irin naka?"
Suna hira da matar Maikudi da Jume Maikudin ya shigo yana hade rai. Shi yafi kowa sanin babban dalilinsa na kin zuwansu garin amma bazai iya fadawa kowa ba. Yaran dama baya sakar musu fuska. Sai dai suna da kyakkyawar mu'amala da 'yan uwansu wato jikokin gidan. Satinsu daya suka juya Jume kamar a bar mata su. Babbar damuwarta shine rashin kowa daga bangaren Innar Zayyan wanda Jume tace har yau itama tana zuba idanu ne.
Maikudi bai sami sukuni ba sai da suka bar garin. Sirrika biyu yake boyewa Mairama saboda mugunta da kuma son kai irin na dan Adam.
Na farko dai wata shida da rasuwar Zayyan kawunsa Sidi yazo bisa shawarar 'yan uwa. Ashe ya tura musu wasika da zai tafi ta tasha. Sidi yazo gari Jume da matan gidan sun tafi Tureta biki. Maikudi kawai ya samu su Badaru basa gida. Lokacin yana tsaka da jin haushin rashin mutumcin Malamijo kuma yasan idan mutanen nan suka san da zamansu ba karamin alheri zasu rinka musu ba. Wanda zai koma jikin Malamijo a karshe. Saboda haka ya matso hawaye ya sanar dashi mutuwar Zayyan da kuma hatsarin da su Mairama suka yi ita da 'yarta suka rasu gabadaya. Wannan shine dalilin da yasa aka dena ji daga garesu.
Abu na biyu kuma shine aike duk karshen wata daga kasar Germany wanda Retired Major Mustapha bai taba dena yi ba tun bayan samun lafiyarsa da aiki a can din kusan shekaru hudu. Kudi ne yake turowa ta hanyar wani soja da yake karkashinsa a da kuma ya yarda dashi. Wannan mutumi duk wata Maikudi yasan ranar da yake zuwa har barikinsu ya karbi kudin da suke mazaunin kudin makarantar Radhiya da kuma tallafi ga Mairama. Soke abinsa yake ga gidan Kano ya saka 'yan haya. A takaice dai yana ta gina kansa don ya sayi fili a cikin Sakkwato yana ta makara gini da kudin marayu.
**********
Mairama ta koma ta tarar da babbar kura. Malamijo ya karbi sadakinta daga hannun Alh Indararo an saka biki wata uku kafin ya gama yi mata gyaran gida. Ta shiga matsanancin tashin hankali har Nene Marka tazo amma kowa cewa yake tayi auren ko zata sami hutu itama.
Tayi kukan, tayi haukan duk a banza bata da mai tsaya mata. A bangare daya kuma duniyar Salame ta juye. Mutum kamar Alh Indararo ace yana son mace kakarta ta yanke saka. Shine wannan karon ma irin abinda take muradi ya tafi ga Mairama. Rantsuwa tayi cewa hakan bazata sake sabuwa ba.
Gidan Malaminta da suka saba kashewa kudi domin a dawo mata da Salisu taje. Bayan dogon bugun kasa yace ta saka ranta a inuwa akwai rabo yana iya gani tsakaninta da Alh Indararo amma sai an kawar da Mairama.
"Malam rufa min asiri kanwata ce fa. Ni dai bazan iya kasheta ba"
Gemunsa na munafurci da suke cutar jama'a dashi ya ja yana murmushi "waye yace sai kin kasheta. Idan kina so nakasa kawai zamu dora mata wadda zata saka ya fasa."
Kwana biyu tana tunani kafin ta hasko me take son ayiwa Mairama. Magani ya bata ta wuce gida ta saka a inda ya umarceta.
Kwana uku a tsakani kuwa wata safiyar lahadi Mairama ta tashi bata gani sai dususu komai yayi hazo. Cikin maganin digawarta na ido Salame ta zuba mata maganin. Cikin wata guda idanun Mairama sai suna. Duk abinda ya rage mata ya kare a neman maganin ciwon idon amma asibiti basa ganin komai.
Kuka ashe bai kare mata ba. Bata gane kowa sai duhun inuwa. Tashi guda Radhiya ta koma idanunta madogararta. Alh Indararo ya canja sheka bazai iya auran musaka ba Salame har ta tare abinta.
Karatun yaran ya tsaya yau da gobe Malamijo ya gaji da dan mikawar da yake yi. A bisa dole ta hakura da karatun Radhiya da Emzee. Tana kuka kan kuka amma mahaifinta bazai iya kulawa da ita ba bare 'ya'ya, iyakarsa dasu shine za'a dafa abincin gidan dasu. Radhiya ta fara hankali tasan cewa mahaifiyarta tana bukatarta shiyasa bata fita idan ba aike ba. Emzee kuwa dama daddawar daka ne shiyasa bata hadu da matsalar ace suna yawace-yawace ba. Rayuwar Mairama matar soja ta cika da wahalhalun da suka sa take bukatar a dube ta.
***********
Maza ne uku a karkashin bishiyar darbejiya wadda ta yiwa wurin yalwatacciyar inuwa. Daya yana zaune akan kujera sauran biyun kuma suna gabansa ne kana gani kasan mai mulki ne da wadanda yake mulka.
Gyaran murya na kan kujerar yayi suka dawo da hankula gareshi "Mal Gide"
"Ranka ya dade" wanda yafi manyanta cikinsu ya amsa.
"Habubakari"
"Allah Yaja zamaninka" na biyun ya amsa.
Dan murmushi yayi domin kuwa su biyun yayun matarsa ne Innawuro.
"Mal Gide kaine babba saboda haka ta kanka zan fara. Ba tare da jan zance ba magana ce akan sakacinku da zumunci saboda wani abu can da ya faru shekarun baya"
Mal Gide ya hadiyi yawu yana kallon Habubakari shima kuma yayan nasa yake kallo.
Ardo Barkindo ya dan duku da kansa kadan daga kan kujerar "wannan zumuncin da kuka banzatar ina mai tabbatar muku sai Allah Ya tambayeku akansa. Kune kuka ci bashi kamar yadda naji a bisa dole. Dole tasa kuka biya bashin da kanwarku sai gashi daga karshe ya sakota ya bukaci kudinsa ko. 'Yar uwarku ta sadaukar da farincikinta saboda ku amma shekaru sun tasanmu talatin marainiyar da ta bari baku san cinta ba baku san shanta ba"
Habubakar wanda abin shima ya dame shi amma tsoron Gide ya hana shi furtawa ya sharce kwalla "Ardo zamu gyara, wallahi nima abin ya dameni. Ali bashi da kirki ko kadan. Allah ma yasa tana da rai yarinyar nan"
"Yarinya da ranta amma tana cikin mawuyacin hali. Yanzu da na kiraku dama sanar daku zanyi cewa zan daukota ko dan kwanciyar hankalin Innawuro"
Nan ya sanar dasu komai game da Mairama kamar yadda yaji daga bakin mijin Nene Marka bayan ya soma binciken nemota.
Mal Gide sai hawaye. Bakar zuciya tasa ya umarci 'yan uwansa da babu su babu zuri'ar Malamijo, ciki kuwa harda 'ya daya tilo ga kanwarsa Mairo wadda ya yiwa auren dole da Malamijo.
"Da kaina zanje in daukota da yaran su zauna a gidana Zan gyara wannan abu duka laifina ne"
Ardo Barkindo ya kada kai yana murmushi "haba dai Gide ai bazamu yi haka da kai ba. Yarinya a wurin babarta zata zauna. Duk na gama wahalar neman sannan kace zaka daukota ka kwashe ladan"
Murmushi ya maida masa "duk yadda kace ranka ya dade, kamar yaushe zamu tafi?"
"Jibi in sha Allahu. Ina so ku tattaro kan 'ya'yanku har na gidan aure da suke rugar nan da kewaye maza da mata. So nake muje mu cika musu ido mu wanke gorin dangin uwa da na tabbatar ansha yi mata."
Sun tashi da fara'a kowa yana jin kamar an sauke masa nauyi daga zuciya. Ardo Barkindo ya nisa yana tunanin ya boye musu makantar Mairama saboda yasan duka hankulansu zasu tashi. Idan sun je zasu ganewa idanunsu. Ko matarsa ya kasa fadawa ita da ta uzzura masa akan neman 'yar yayarta da take bi.
Mal Gide kuwa har ya isa gida yana tunanin da yardar Allah zasu kula da ita bakin iyawarsu su daidaita tsohuwar baraka. Tunawa yayi da umarnin Ardo ya tura guda cikin 'ya'yansa da yaje ya fara sanar da yayyensa cewa suna da zuwa Kano jibi daga rugarsu wadda take cikin karamar hukumar Giade a jihar Bauchin Yakubu.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: WAIWAYE....
Zainab tayi kuka har ta gode Allah. Hadir dinta ne kwance baya iya motsa kowace gaba a jikinsa sannan baya iya magana. Idanunsa kadai ke aiki idan anyi magana kuma yana ji amma babu damar amsawa. Tun iyaye na rarrashinta har suka kyaleta ta koka ko zata ji sa'ida.
Zuwansu Kano kenan aka kaisu tsohon dakinsa inda yake zaman jinya. A hankali ya bude idanunsa ya saukesu a kanta. Murmushi yayi wanda ya hado da zubar hawayensa. Sunanta yake kira amma babu mai jin sautin saboda baya iya motsa harshensa. A guje ta fita da ta ga ya tashi ta dauko Ibrahim yana wasansa a dakin kakarsa. Dakin ta koma dashi ta kama hannun Hadir ta hada da nasa.
"Idan ni bazaka tabani ba ka tashi ka dauki danka. Don Allah...don Allah Hadir ko Ibrahim ne ka rike da kanka"
Runtse idanunsa kawai yayi. Yaya zaiyi da iyalinsa? Allah ne gatan gidansu sai shi da guntun albashinsa. Shikenan rayuwarsa da tasu ta tsaya saboda lalurar da ta same shi? Ina Major Mustapha? Yayi rai ko shima ya rasu? Ina Mairama da Radhiya? Akwai amanar takardun kwafin gidansa a wurinsa. Ta yaya zai isa ga wannan mutane da yake tausayawa duk da halin da yake ciki.
Kanwar Hadir ce ta jiyo Zainab tana surutai ita kadai tazo ta fitar da Ibrahim sannan ta fadawa mamansu halin da take ciki. Tun zuwansu ko ruwa bata sha ba sai kuka. Umman tasu taje har dakin tace mata ta taso ta ci abinci shima ta barshi ya huta. Kamar ba da ita take ba tana ta magana taki tashi sai cewa take ta koshi. Babansu Hadir aka kira shima yazo yace indai kuka zata rinka yi to ta fita daga dakin.
Hannu ta dora a baki da sauri "na dena, wallahi na dena" tana magana hawayenta da na Hadir yana karuwa.
Baban ya fita yana cewa Umma ta kyaleta dama sun sani dole tayi kuka.
Bayan fitarsu hannunsa ta kama tana shafa kumatunta "Hadir kana ji na?"
Jikakkun idanunsa ya kifta mata yana son yin murmushi "kin fiye rigima" yace a ransa.
Shagwabar da ta saba yi masa take kokarin yi kuka yana cin karfinta "ka taimakeni ka tashi, kaga Ibrahim ya kara nauyi yanzu. Ni kadai kake so na rinka daukarsa? So kake ya buda min kirji irin naka?"