Sashe 38
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ya gyada mata yana murmushi. Hannunsa taje ta rike tana durkushe a gabansa ita dai tana son sa sosai, sai da Daddy yace ta bi bayan 'yan uwanta zaiyi magana da iyayenta ta fita. Da taje dakin daga bakin kofa ta wulla jakarta ciki sai gasu suna darewa da sauri don ba karamin tsoro ta basu ba. Wata shu'umar dariya tayi wani abu ma sai an dawo daga makarantar sojoji. Babu wadda ta tanka mata ta shigo ta haye gado ta kwanta. Wayar Zahra aka kira ashe Awwab ne ya ya tambayeta size din takalmin Radhiya saboda yasan suna gidan. Kintata kawai tayi ta fada masa saboda ita dai bazata tambayeta ba a yau dai sannan a gabanta bazata taba mata takalmi ba don tsoron me zai faru take ji.
A falon Daddy kuwa bayan fitarsu Mairama ta shiga basu hakurin halayyar Radhiya. Gani take kamar laifinta ne ko sakacin tarbiya ne ya kawo hakan.
"Kowane da da irin halayensa da dabi'u da ake haihuwarsa dashi. Kuma yadda take dinnan Allah kadai Yasan wace irin tarin baiwa Yayi mata. Ki dena damun kaki watarana zaki ga kamar ba'ayi ba"
Mami ce da wannan dogon jawabi sauran suna gyada kai. Daddy ya bijoro musu da zancen da sukayi da su Ardo.
"Hada Awwab da kanwarsa abu ne da na kudurta tun ranar da na dora ido a kanta. Hadir ya amince ina fata Allah Yasa ku ma ku bani goyon baya"
Gabadaya matan nan uku bakunansu murmushin jindadi suke nunawa. Mami tana maraba da wannan hadin domin bazata taba kyamar tsatson Mairama da Zayyan ba. Tafi kowa sanin mahimmancin yin hakan a wurin mijinta. Zai kara sakawa yaji a ransa cewa bai ya da iyalan Zayyan din ba. Ya so Zayyan tun basu saba ba duk ranar da suka je training zata kwana yana bata labarin fitinannen basakkwacen nan. Lokaci kalilan ne Radhiya zata waye tayi zarra cikin sa'anni. Zainab ma taji dadi don burinta su hadu su baiwa Mairama da 'ya'yanta dukkan farincikin da suka rasa. Allah Ya sani ba don sa'anni suke da Ibrahim har ta bashi watanni ba itama da zata so hadasu ne.
Farincikin Mairama yafi na kowa. Wadannan mutane masu dimbin karamci a gareta ace babu kyamar yadda su suka kara wayewa ita da 'ya'yanta suka sake ci baya ta fannin wayewa da sanin ababen rayuwa amma su nemi hada Radhiya da Awwab, Awwab dinta dai wanda ya mayar da ita da mijinta iyaye tun farkon haduwarsu. Hawaye ta shiga yi tana mika godiya garesu.
"Bani da bakin godiya, Zainab kunji wani karamcin kuma?"
"Idan kina haka sai mu ga kamar a wurinka Radhiya da Zayyan ba namu bane Ummin Awwab"
"Haba Mami kada kice haka mana, farinciki ne kawai yayi min yawa"
Mami ta tambayi Major "yaushe kake tunanin auren?"
"Kuna ganin zamu iya hadawa da na su Zahra? Idan hakan yayi in sha Allahu karshen sati Alh Baba zai dawo daga Umara sai na fada masa"
To waye ma zaice baiyi na'am da wannan hadi ba. Bakinsu duk yazo daya, abu guda ya rage a sanar da Alh Baba sai ayi shiri aje a nemi aurenta wurin wadanda ya dace wato dangin mahaifinta na Sakkwato da kuma marikanta ta bangaren uwa su Ardo Barkindo.
**********
"Banza jaka bace min da gani ko inyi kwallo dake. Har yau ina tsananin mamakin yadda akayi na kwaso ki Salame"
Janye tsumman jikinta tayi da ya gama karewa ya tsotse babu wani tudu a jikinta bayan cikin jikinta na wata shida. Gabadaya ta mokade baka ce Salame bace da tauraruwarta ta taba haskawa a gidan Salisu. Aure dududu bai wuce shekara takwas ba amma haihuwarta biyar ga cikin na shida. Da kyar take tafiya yunwa ta yiwa hanjinta mugun lahani ga yara tun asuba suke kira mata yunwa suna kuka.
Ba ta daddara ba ta sake hada hannuwa a gaban Alh Indararo "Alhaji ko naira hamsin ce ka bani don Allah, bani da karfin karbo wankau da bazan tambayeka ba"
Kallon kin ma rainani ya jefa mata "sai ki tafi inda kika saba zuwa gidan tsoho aje a ci abinda ya sauwaka"
Duk magiya da rokonta ta bayan kunnensa tabi sai da ranta ya baci sosai ta tsaya masa kerere a gaba. Tulun cikinsa kadai ya isa ya tureta dashi ta fadi.
"Ka sakeni in koma gidan ubana ai ba a titi aka daura mana aure ba. Wannan wace irin rayuwa ce ace matanka tsakaninka dasu bai wuce ka dirka mana ciki ba. Ci da sha da sutura sai dai mu yiwa kanmu. Ko kunya baka ji duk kudinka. Mune wankau, surfe da duk wani aikin kaskanci don mu ciyar da kanmu da 'ya 'yanmu"
Marin da ya zabga mata ne yana faman nade hannun malum malum ya gigita ta ta kasa cigaba da maida martani.
"Ki fita idona Salame, wannan jarababben auren naki kuma yanzu muka fara babu inda zaki je"
Fuuuu ya fice daga gidan sai dariyar Maman Danmama da ta cika mata kunne. Bata saurara ba sai da ta fito daga dakinta tazo gaban Salame tana mata dariyar mugunta.
"Mu dai sai dai muce Allah Ya kara karawa. Ki koma wurin bokanki kice masa kwabarki tayi ruwa. Irin wadannan ranakun tsakaninki da Alhaji su kan sani nishadi da wanke min zuciya. Anyi walkiya Salame mun ganki tsamo tsamo"
Dan sauran kuzarin nata na fada marin da ta sha ya tafi dashi, shiyasa ta kasa maidawa Maman Danmama. Ita kuwa batayi shiru ba.
"Ohhh ni 'yasu. Kamar ba'ayi zamanin da kike sa Alhaji ya zage ya zanemu a cikin gidan nan ba. Kika dawo kika saka shi sakin kowa banda ni wai na zauna nayi raino kema a gidanku uwargidan babanku aikinta kenan. Ai ance tsafi gaskiyar mai shi. Kinyi kin gama surkullen tazo ta kare miki"
Wani dukunkunannen hijabi Salame ta saka taki kula Mama ta fita tare da yaranta ta nufi gida.
A soro suka yi kicibus da Malamijo zai fita. Girma ya kara kama shi sai dai akwai kyan jiki tunda babu kiba kuma yanzu ya yarda da ci da sha wa kansa mai kyau a waje. 'Yar fara'ar da ya taho da ita sakamakon faranta masa da amarya tayi kafin ya fito ce ta bace yana ganinta.
"Allah Yayi dare gari ya waye an kwaso jiki an taho cin banza. To baki isa ba Salame. Tunda na aurar dake ko dan ihsanin nan na tsakanin da da mahaifi bai taba giftawa tsakaninmu ba sai ma dai ki karkace ki fada min magana idan kinso. Amma 'yan kwanakin nan kullum ana fada min sai kinzo, kuma ba kya tashi zuwa sai kin daidaici an gama abinci. Ki kwaso yara rabe-rabe azo aci bati. To na gaji, ki juya sawunki a likkafa ki koma inda kika fito"
Jikinta har bari yake saboda yunwar dake sasakarta fushi da maidawa mahaifinta martani ba nata bane yau dinnan idan ba so take daga ita har yaran yunwa ta kar su ba.
"Ku shige gani nan zuwa" tace tana kadasu ciki.
"Ya ina cewa ku koma kina turasu? Salame, Salame ki kiyayeni." Yace yana nunata da yatsa.
"Gaisawa kawai zanyi dasu mu tafi"
Tausayinta ya dan ji saboda ya tabbatar yadda ta fige dinnan tabbas kila mijin da har shi take iya yiwa rashin kunya a kansa ya juya mata baya ne.
"Jeki amma daga yau na sake ganinki zanje na sami Alh Indararon inji ko har ya cinye sadakinsa ne shiyasa zamu fara raba nauyin. Mairama ma da take ruga ta fiki abin arziki. Makanta, rashin miji da nisa basu hanata yi min alheri ba."
Kunci taji ya ziyarci zuciyarta saboda ya ambaci kamwarta da ta mayar kishiyarta ta karfin tsiya. Duk ita ce silar komai tunda dalilinta taje wurin boka aka rabata da Alh Indararo saboda kawai bata son ta ga tayi gaba ta barta ba wai don ita din sonsa take yi ba. Da asiri ta rinka cin galaba akansa da matansa komai na tafiya daidai ta kuma saki jiki tana ta haihuwa don ta tara magada sosai. Cikin jikinta na da wata biyu bokan nata yace ga garinku. Shikenan duniya tayi mata atishawar 'yan tsaki. Komai ya lalace wai ita da take mulkin gidan a tsakar gida Alh Indararo ya kalleta yace yaushe ya aurota. Da bakinsa yake cewa ina Mairama kanwarta. Rai a bace ta shige ta ce da yaranta su taso su tafi.
"Ki barsu yanzu zan zuba musu abinci Salame" Yadikko tace mata tana kallonta da tausayawa. Ko bata ce komai ba kana kallonta kasan akwai yunwa daga ita har yaran.
"Tafiya zamuyi, kai ku tashi mana"
"Umma ki bari muci abinci" babbar 'yarta tace idonta cike da kwalla.
"Ko ku tashi ko jikinku ya gaya muku ku duka. Aikin banza kai."
Duk yadda Yadikko taso kin zama tayi saboda kawai an yabi Mairama ta gwammace su sake kwana da yunwa.
**********
Karfe biyar da rabi Awwab ya sauka a Nnamdi Azikiwe International Airport da yake birnin tarayya. Ya saba tafiye tafiyensa babu wasu kaya sai 'yar jaka karama da yake saka kayan sakawa biyu ko uku ya danganta da kwana nawa zaiyi a garin. Wannan karon kuwa sai da ya hado da akwati mai kyau na turawa dan madaidaici. Jin kansa yake wasai babu tarin gajiyar nan saboda a fasinja ya taho ba pilot ba, tun daga tasowarsu sai minti goma kafin saukar jirgin ya farka.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Zainab baki yaki rufuwa "Awwab, Masha Allah sannu da zuwa...zauna, zauna kasha hanya"
Shi dai murmushi yake yi amma hankalinsa gabadaya yana wurin wannan kan dake kwance akan kujera. Allah ne Ya taimaka Zainab ta kula da me yake kallo tayi saurin dora yatsanta a baki wai yayi shiru. Dankwalin da Radhiya ta rufe kafa dashi shi ta dauka a hankali ta mayar mata dashi kanta. Sai lokacin ya iya dauke ido daga kanta ya mayar garesu. Gaban Hadir yaje ya durkusa ya rike masa hannu yana jin kwalla ta taho masa.
"Nasan ka gama jin duk wani labari a wurinsu Mami kuma ka gama kukanka. Kayi hakuri ka saki zuciyarka muyi murnar sake haduwa" Zainab tace tana kallon yadda Awwab din ya koma ingarman matashi.
A falon Daddy kuwa bayan fitarsu Mairama ta shiga basu hakurin halayyar Radhiya. Gani take kamar laifinta ne ko sakacin tarbiya ne ya kawo hakan.
"Kowane da da irin halayensa da dabi'u da ake haihuwarsa dashi. Kuma yadda take dinnan Allah kadai Yasan wace irin tarin baiwa Yayi mata. Ki dena damun kaki watarana zaki ga kamar ba'ayi ba"
Mami ce da wannan dogon jawabi sauran suna gyada kai. Daddy ya bijoro musu da zancen da sukayi da su Ardo.
"Hada Awwab da kanwarsa abu ne da na kudurta tun ranar da na dora ido a kanta. Hadir ya amince ina fata Allah Yasa ku ma ku bani goyon baya"
Gabadaya matan nan uku bakunansu murmushin jindadi suke nunawa. Mami tana maraba da wannan hadin domin bazata taba kyamar tsatson Mairama da Zayyan ba. Tafi kowa sanin mahimmancin yin hakan a wurin mijinta. Zai kara sakawa yaji a ransa cewa bai ya da iyalan Zayyan din ba. Ya so Zayyan tun basu saba ba duk ranar da suka je training zata kwana yana bata labarin fitinannen basakkwacen nan. Lokaci kalilan ne Radhiya zata waye tayi zarra cikin sa'anni. Zainab ma taji dadi don burinta su hadu su baiwa Mairama da 'ya'yanta dukkan farincikin da suka rasa. Allah Ya sani ba don sa'anni suke da Ibrahim har ta bashi watanni ba itama da zata so hadasu ne.
Farincikin Mairama yafi na kowa. Wadannan mutane masu dimbin karamci a gareta ace babu kyamar yadda su suka kara wayewa ita da 'ya'yanta suka sake ci baya ta fannin wayewa da sanin ababen rayuwa amma su nemi hada Radhiya da Awwab, Awwab dinta dai wanda ya mayar da ita da mijinta iyaye tun farkon haduwarsu. Hawaye ta shiga yi tana mika godiya garesu.
"Bani da bakin godiya, Zainab kunji wani karamcin kuma?"
"Idan kina haka sai mu ga kamar a wurinka Radhiya da Zayyan ba namu bane Ummin Awwab"
"Haba Mami kada kice haka mana, farinciki ne kawai yayi min yawa"
Mami ta tambayi Major "yaushe kake tunanin auren?"
"Kuna ganin zamu iya hadawa da na su Zahra? Idan hakan yayi in sha Allahu karshen sati Alh Baba zai dawo daga Umara sai na fada masa"
To waye ma zaice baiyi na'am da wannan hadi ba. Bakinsu duk yazo daya, abu guda ya rage a sanar da Alh Baba sai ayi shiri aje a nemi aurenta wurin wadanda ya dace wato dangin mahaifinta na Sakkwato da kuma marikanta ta bangaren uwa su Ardo Barkindo.
**********
"Banza jaka bace min da gani ko inyi kwallo dake. Har yau ina tsananin mamakin yadda akayi na kwaso ki Salame"
Janye tsumman jikinta tayi da ya gama karewa ya tsotse babu wani tudu a jikinta bayan cikin jikinta na wata shida. Gabadaya ta mokade baka ce Salame bace da tauraruwarta ta taba haskawa a gidan Salisu. Aure dududu bai wuce shekara takwas ba amma haihuwarta biyar ga cikin na shida. Da kyar take tafiya yunwa ta yiwa hanjinta mugun lahani ga yara tun asuba suke kira mata yunwa suna kuka.
Ba ta daddara ba ta sake hada hannuwa a gaban Alh Indararo "Alhaji ko naira hamsin ce ka bani don Allah, bani da karfin karbo wankau da bazan tambayeka ba"
Kallon kin ma rainani ya jefa mata "sai ki tafi inda kika saba zuwa gidan tsoho aje a ci abinda ya sauwaka"
Duk magiya da rokonta ta bayan kunnensa tabi sai da ranta ya baci sosai ta tsaya masa kerere a gaba. Tulun cikinsa kadai ya isa ya tureta dashi ta fadi.
"Ka sakeni in koma gidan ubana ai ba a titi aka daura mana aure ba. Wannan wace irin rayuwa ce ace matanka tsakaninka dasu bai wuce ka dirka mana ciki ba. Ci da sha da sutura sai dai mu yiwa kanmu. Ko kunya baka ji duk kudinka. Mune wankau, surfe da duk wani aikin kaskanci don mu ciyar da kanmu da 'ya 'yanmu"
Marin da ya zabga mata ne yana faman nade hannun malum malum ya gigita ta ta kasa cigaba da maida martani.
"Ki fita idona Salame, wannan jarababben auren naki kuma yanzu muka fara babu inda zaki je"
Fuuuu ya fice daga gidan sai dariyar Maman Danmama da ta cika mata kunne. Bata saurara ba sai da ta fito daga dakinta tazo gaban Salame tana mata dariyar mugunta.
"Mu dai sai dai muce Allah Ya kara karawa. Ki koma wurin bokanki kice masa kwabarki tayi ruwa. Irin wadannan ranakun tsakaninki da Alhaji su kan sani nishadi da wanke min zuciya. Anyi walkiya Salame mun ganki tsamo tsamo"
Dan sauran kuzarin nata na fada marin da ta sha ya tafi dashi, shiyasa ta kasa maidawa Maman Danmama. Ita kuwa batayi shiru ba.
"Ohhh ni 'yasu. Kamar ba'ayi zamanin da kike sa Alhaji ya zage ya zanemu a cikin gidan nan ba. Kika dawo kika saka shi sakin kowa banda ni wai na zauna nayi raino kema a gidanku uwargidan babanku aikinta kenan. Ai ance tsafi gaskiyar mai shi. Kinyi kin gama surkullen tazo ta kare miki"
Wani dukunkunannen hijabi Salame ta saka taki kula Mama ta fita tare da yaranta ta nufi gida.
A soro suka yi kicibus da Malamijo zai fita. Girma ya kara kama shi sai dai akwai kyan jiki tunda babu kiba kuma yanzu ya yarda da ci da sha wa kansa mai kyau a waje. 'Yar fara'ar da ya taho da ita sakamakon faranta masa da amarya tayi kafin ya fito ce ta bace yana ganinta.
"Allah Yayi dare gari ya waye an kwaso jiki an taho cin banza. To baki isa ba Salame. Tunda na aurar dake ko dan ihsanin nan na tsakanin da da mahaifi bai taba giftawa tsakaninmu ba sai ma dai ki karkace ki fada min magana idan kinso. Amma 'yan kwanakin nan kullum ana fada min sai kinzo, kuma ba kya tashi zuwa sai kin daidaici an gama abinci. Ki kwaso yara rabe-rabe azo aci bati. To na gaji, ki juya sawunki a likkafa ki koma inda kika fito"
Jikinta har bari yake saboda yunwar dake sasakarta fushi da maidawa mahaifinta martani ba nata bane yau dinnan idan ba so take daga ita har yaran yunwa ta kar su ba.
"Ku shige gani nan zuwa" tace tana kadasu ciki.
"Ya ina cewa ku koma kina turasu? Salame, Salame ki kiyayeni." Yace yana nunata da yatsa.
"Gaisawa kawai zanyi dasu mu tafi"
Tausayinta ya dan ji saboda ya tabbatar yadda ta fige dinnan tabbas kila mijin da har shi take iya yiwa rashin kunya a kansa ya juya mata baya ne.
"Jeki amma daga yau na sake ganinki zanje na sami Alh Indararon inji ko har ya cinye sadakinsa ne shiyasa zamu fara raba nauyin. Mairama ma da take ruga ta fiki abin arziki. Makanta, rashin miji da nisa basu hanata yi min alheri ba."
Kunci taji ya ziyarci zuciyarta saboda ya ambaci kamwarta da ta mayar kishiyarta ta karfin tsiya. Duk ita ce silar komai tunda dalilinta taje wurin boka aka rabata da Alh Indararo saboda kawai bata son ta ga tayi gaba ta barta ba wai don ita din sonsa take yi ba. Da asiri ta rinka cin galaba akansa da matansa komai na tafiya daidai ta kuma saki jiki tana ta haihuwa don ta tara magada sosai. Cikin jikinta na da wata biyu bokan nata yace ga garinku. Shikenan duniya tayi mata atishawar 'yan tsaki. Komai ya lalace wai ita da take mulkin gidan a tsakar gida Alh Indararo ya kalleta yace yaushe ya aurota. Da bakinsa yake cewa ina Mairama kanwarta. Rai a bace ta shige ta ce da yaranta su taso su tafi.
"Ki barsu yanzu zan zuba musu abinci Salame" Yadikko tace mata tana kallonta da tausayawa. Ko bata ce komai ba kana kallonta kasan akwai yunwa daga ita har yaran.
"Tafiya zamuyi, kai ku tashi mana"
"Umma ki bari muci abinci" babbar 'yarta tace idonta cike da kwalla.
"Ko ku tashi ko jikinku ya gaya muku ku duka. Aikin banza kai."
Duk yadda Yadikko taso kin zama tayi saboda kawai an yabi Mairama ta gwammace su sake kwana da yunwa.
**********
Karfe biyar da rabi Awwab ya sauka a Nnamdi Azikiwe International Airport da yake birnin tarayya. Ya saba tafiye tafiyensa babu wasu kaya sai 'yar jaka karama da yake saka kayan sakawa biyu ko uku ya danganta da kwana nawa zaiyi a garin. Wannan karon kuwa sai da ya hado da akwati mai kyau na turawa dan madaidaici. Jin kansa yake wasai babu tarin gajiyar nan saboda a fasinja ya taho ba pilot ba, tun daga tasowarsu sai minti goma kafin saukar jirgin ya farka.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Zainab baki yaki rufuwa "Awwab, Masha Allah sannu da zuwa...zauna, zauna kasha hanya"
Shi dai murmushi yake yi amma hankalinsa gabadaya yana wurin wannan kan dake kwance akan kujera. Allah ne Ya taimaka Zainab ta kula da me yake kallo tayi saurin dora yatsanta a baki wai yayi shiru. Dankwalin da Radhiya ta rufe kafa dashi shi ta dauka a hankali ta mayar mata dashi kanta. Sai lokacin ya iya dauke ido daga kanta ya mayar garesu. Gaban Hadir yaje ya durkusa ya rike masa hannu yana jin kwalla ta taho masa.
"Nasan ka gama jin duk wani labari a wurinsu Mami kuma ka gama kukanka. Kayi hakuri ka saki zuciyarka muyi murnar sake haduwa" Zainab tace tana kallon yadda Awwab din ya koma ingarman matashi.