Sashe 60
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Daddy yace in fada maka kaje wurin Alh Baba shima yana son ganinka. Ni duk za'a cinye min lokacina"
Murmushi yayi duk don ya nuna mata komai lafiya "My G baki da dama, yanzu su Alhajin ne masu cinye miki lokaci?"
Tana ta tura baki suka shiga wajen matan Alhajin daga nan ta bishi falonsa. Sun gaisa yayi masa barka da dawowa shi kuma Alhajin ya bashi karamar robar zamzam da dabino ya karba da godiya. Ganinsu da yayi da jikar tasa ya faranta masa rai sosai. A son ransa zuri'arsu suyi ta auren junansu yadda za'a sami hadin kai mai dorewa har jikoki.
"Dan bamu wuri zanyi magana da yayanki Ghazalatu"
Shikenan za'a sake ci mata lokaci ta ayyana a ranta. Zaman da tayi don ta sami damar fita dashi ne kada Alh Baba ya dauko doguwar hira a tsakaninsu. Iyakarta bakin kofa ta makale daga gefe da zummar idan taji hirar zata yi tsayi ta koma tace ana kiransa. Abinda taji Alh Baba yana cewa ne yasa ta sake matsowa sosai don taji da kyau.
"Munyi magana da iyayenku jiya. Naji dadi kwarai da kuka hada kai da kanwarka. Kuma na yanke cewa ayi auren nan da wata uku. Ina fata zaka iya shiryawa kafin nan."
Wani tsalle Ghazalatu ta daka daga inda take. Awwab godiya yayi masa sosai yana murmushi.
"Sai dai Mustapha ya kawo wani hanzari na cewa ya nema maka auren yarinyar abokinsa batare da sanin kana neman Ghazalatu ba"
Gabanta taji ya fadi don ta sani babu wadda ake nufi ko da ba'a ambaci suna ba sai Radhiya yarinyar nan mai kwalkwalin kai.
Kansa a kasa cike da ladabi Awwab yace "hakane Alhaji"
Tsohon ya gyara zamansa yana kallon jikan nasa "tun a jiyan na fada masa sai a basu hakuri tunda kana da wadda kake so bai kyautu ace sai ka aureta ba. Ni a tsarina ma Allah Ya gani nafi son ku rinka auren junanku. Ita idan aurenta ya tashi sai yayi mata duk abinda uba yake yiwa 'yarsa"
Wannan shine son kai. Babu yadda za'ayi Awwab yayi shiru da wannan magana ya karbi hukuncin Alh Baba batare da ya gabatar masa da nasa uzurin ba.
"Alhaji kayi min izini na auresu su biyu. Ina iya fara auren Ghazalatu sai na aureta daga baya"
Rai a bace ya soma fada "abinda uban naka ya turoka ka fada min kenan. Wato saboda jiya nace ban yarda ba shine kai ka shafawa idonka toka zaka yi min rashin kunya?"
"Alhaji kayi hakuri ba haka bane"
"To nace na soke bazaka aureta ba. Banda son dorawa kai wahala ina zaka kai mata biyu Muhammad? Idan kana son yiwa mahaifinka biyayya ne kaje abinka shima ai karkashina yake"
Ran Awwab sai kuna yake ya kasa daurewa "Alhaji wallahi ina sonta"
Kallon da Alh Baba ya watsa masa a lokacin kallo ne na tsananin bacin rai.
Ghazalatu da ta gama jin komai hankalinta bai tashi sosai ba sai da taji furucin Awwab. Kuka ta fashe dashi ga bakinciki ga kishi ta bar wurin a guje. Daga Alhajin har Awwab sun jiyo muryarta.
"Ka tashi kabi sawun kanwarka ku daidaita. Na gama magana Muhammad bana son sake jin wata magana"
"Alhaji...."
"Ka tashi ka tafi nace"
Yana fita daga falon waje ya nufa ya shiga mota ya kifa kai akan sitiyari.
"Ya Allah" ya furta a hankali ko ina na jikinsa yana cikin tashin hankali. Bazai taba iya hakura ko rabuwa da Alheran ba. Ya barta a kira shi da me? Butulu ko mayaudari? A cikin abinda bai gaza sati biyu ba ya fada matsananciyar soyayyarta kuma itama ya koya mata sonsa. Akwai kunya da nauyi sosai tsakanin iyayensu wanda bai cancanci a sanadiyarsa ya kawo wata baraka a tsakani ba kamar yadda baya fatan kawo baraka ga danginsa. Shi da Ghazalatu sunyi dumu dumu a cikin dangi. Idan baka dubesu ta nan ba zaka dubesu ta can. Hadi ne tun daga kakanni an cakude da juna.
Dakin mahaifiyarta Mummy Gambo ta wuce kai tsaye tana kuka kamar ranta zai fita. Babu abinda yake mata yawo a ka sai jin da tayi Awwab da bakinsa yace yana son wannan yarinyar.
Mummy ta taso ta tarbeta da sauri "me ya sameki?"
"Mummy Yaya ne...Yaya Awwab baya sona"
"Ban gane ba, idan wani shirmen fadanku ne dama kada ki soma gaya min. Kije can ku sasanta"
"Mummy wata yake so. Yaci amanata wallahi 'yar wannan makauniyar da ta zauna gidansu yake so"
Nata hankalin sai yafi na Ghazalatu tashi "dena kuka bari na kira Hassana naji daga bakinta."
Mami tana daki da Zahra wadda take ta kuka tana bata hakuri Mummy ta kira. Shawara ta yanke gara ta sanar da ita ko Hussaina su tayata bawa Zahra baki.
Sai da ta saita muryarta don ita din ma zuciyarta a karye take "Mummyn yara yanzu kuwa nake shirin nemanki."
"Kina shirin nemana ki fada min kun yiwa Awwab mata ko" tace cikin gatse.
Mami da bata san wainar da ake toyawa ba tayi dariya "hala yazo ya fada miki. 'Yar wajen Mairama ce. Kin ganeta ai wadda tazo ta kwana mana biyu matar ....."
Kit taji shiru Mummy ta kashe wayar. Kallon wayar hannunta tayi da mamaki sai kuma ta soma kiranta missed calls biyar bata dauka. Abin ya dameta ta lallaba Zahra ta fita ta tafi dakin Daddy.
Mummy Gambo ta cika tayi fam. Ita Mami zata wulakantawa 'ya har tana fada mata wadda suka zabawa Awwab. Kenan basu aminta da ya auri Ghazalatu ba. A tunaninta tafi karfin haka a wurin 'yar uwarta ta. Kallon Ghazakatu tayi da take ta kuka tana rarrashinta ta kira Daddy Haroun a waya don ya fita unguwa. Cewa tayi kawai ya dawo gida babu lafiya yace to.
Mami tana zuwa dakin Daddy shi kuma ta same shi yana waya da Alh Baba yana ta ban hakuri. Alh Baba yace ya fadawa Awwab lallai aurensa da Ghazalatu babu fashi. Wurgi ta ga yayi da wayarsa ta karaso kusa dashi da sauri.
"Daddy lafiya?"
"Ki bari muyi maganar nan bayan bikin su Fauziyya kamar yadda Alh Baba yace"
"Wallahi hankalina ya tashi. Tun jiya ka chanja min gabaki daya. Yanzu Gambo ta kirani tana cewa munyiwa Awwab mata nace mata eh kawai ta kashe wayar kamar wadda na yiwa wani abu"
Ran Major tuni ya soma baci kuwa. Yasan Gambo da masifa amma baya son duk abinda zai sosa ran Mami. Ga dadin haushin akan 'yarta ne ake son kirikiri a gwada son kai. Meye matsalar ya auri mata biyu da za'a ce dole sai an janye maganar Radhiya. Radhiya diyar Zayyanunsa.
Sallamar Awwab din suka rinka ji kana jinsa kasan baya cikin nutsuwa. Izinin shigowa Daddy yayi masa yana zuwa ya zube masa.
"Daddy Alh Baba yace bazan auri Alheran ba. To wallahi idan bai amince ba itama Ghazalatun na rantse da Allah ko an daura sai na saketa"
"Kai Awwab, kana cikin hankalinka kuwa? Daddy me yake faruwa ne kun kara sakani cikin duhu"
"Fita ka tafi dakinka" Daddy yace ransa shima a baci. Dakin gabadaya ya juye walwalar ma'abotansa ta fi kamar an kadata da iska.
Tattaro nutsuwarsa ya daure yayi ya fadawa Mami halin da ake ciki. Boyewar bata da amfani tunda Gambo ta sani.
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Yanzu sai Gambo ta ga kamar da gangan nayi"
"Gambo kike ji ko kuwa halin da Awwab zai shiga da yaran nan"
"Daddy ni fa ban ga wata gagarumar matsala a cikin wannan abu ba. Awwab namiji ne saboda haka zai iya aurensu duka. Ciki mu mun isa muce ga wadda zai zaba ya bar dayar? Babu wadda mahaifinta baiyi mana halacci ba saboda haka ka kwantar da hankalinka in sha Allahu komai zai zo da sauki"
A sanyaye yace "Alh Baba yace bazai auri mata biyu ba kuma su Baba sun amince"
Kanta ta dora akan kafadarsa ta kwantar da murya domin kwantar masa da hankali "mu bi komai a sannu saboda kuskure daya zai iya janyo mana rikici a dangi ko tare da iyayen Mairama wanda bana fata. Gobe muje mu roki arzikin suyi hakuri su amince ya auresu su biyun"
Kalamai masu kwantar da hankali ta rinka amfani dasu wurin sanyayawa mijinta rai suka dauki dogon lokaci suna shawara akan wannan matsala.
Tunda Awwab ya shiga daki bai fito ba sai asuba. Kallo daya Major yayi masa ya san cewa da wahala idan ya runtsa. Soyayyar Awwab da Alheran daga Allah ce. Ya tabbatar duk wannan tashin hankalin saboda an hanashi aurenta ne.
**********
Da wuri aka gama komai na sallamar Ummi daga asibiti. Abin da mamaki matuka ta shafe shekaru kusan goma da makanta yau ita ce take da idanun kallon Radhiya da Karami. Bayan an bata gilashinta tana kallonsu ta fashe da kuka. Karami bai baro mahaifinsa da komai ba sai fari da ya dan dara shi wanda ta alakanta shi da kuruciyarsa sai kuma tsaho da shi Zayyan din yafi dan nasa. Radhiya kuwa tafi dauko kamanni da ita sai dai ta rasa inda ta samo wannan kirar jiki. Mairama doguwa ce siririya mai kyaun sura da daukar ido yayin da Radhiya take a murje babu rama amma baza'a a kirata mai kiba ba. Jikinta a cike yake ko ta ina. Yanayin hancinta sam baiyi kama da na Umminta ko mahaifinta ba. Idan tayi murmushi sai kaji kamar ka dauketa saboda yadda fuskar take nuna zallan yarinta idan kumatunta ya lotsa ciki.
Lokacin da suka hada ido da Zainab sai sabon kuka.
"Haka kika koma wata 'yar gayu Zainab dina"
Yaran suna dariya iyayensu suka rungume juna.
"Muje gida kafin ki bar garin nan sai kin zama 'yar gayu kema. Ba biki zakuyi ba....hmmm Allah Mairama sai nasa idanu sun koma kanki a wurin bikin nan" suka yi dariya.
A gaban mota Ummi ta zauna Radhiya da Nene Marka suna baya. 'Yan samari kuwa adaidaita sahu tace su shiga su biyo bayansu.
Sunje gida Ummi ido ya bude ta ga halin da Baba Hadir yake ciki. Tana kuka Zainab tace mata kada ta jangwalo idanun tayi hakuri haka.
Murmushi yayi duk don ya nuna mata komai lafiya "My G baki da dama, yanzu su Alhajin ne masu cinye miki lokaci?"
Tana ta tura baki suka shiga wajen matan Alhajin daga nan ta bishi falonsa. Sun gaisa yayi masa barka da dawowa shi kuma Alhajin ya bashi karamar robar zamzam da dabino ya karba da godiya. Ganinsu da yayi da jikar tasa ya faranta masa rai sosai. A son ransa zuri'arsu suyi ta auren junansu yadda za'a sami hadin kai mai dorewa har jikoki.
"Dan bamu wuri zanyi magana da yayanki Ghazalatu"
Shikenan za'a sake ci mata lokaci ta ayyana a ranta. Zaman da tayi don ta sami damar fita dashi ne kada Alh Baba ya dauko doguwar hira a tsakaninsu. Iyakarta bakin kofa ta makale daga gefe da zummar idan taji hirar zata yi tsayi ta koma tace ana kiransa. Abinda taji Alh Baba yana cewa ne yasa ta sake matsowa sosai don taji da kyau.
"Munyi magana da iyayenku jiya. Naji dadi kwarai da kuka hada kai da kanwarka. Kuma na yanke cewa ayi auren nan da wata uku. Ina fata zaka iya shiryawa kafin nan."
Wani tsalle Ghazalatu ta daka daga inda take. Awwab godiya yayi masa sosai yana murmushi.
"Sai dai Mustapha ya kawo wani hanzari na cewa ya nema maka auren yarinyar abokinsa batare da sanin kana neman Ghazalatu ba"
Gabanta taji ya fadi don ta sani babu wadda ake nufi ko da ba'a ambaci suna ba sai Radhiya yarinyar nan mai kwalkwalin kai.
Kansa a kasa cike da ladabi Awwab yace "hakane Alhaji"
Tsohon ya gyara zamansa yana kallon jikan nasa "tun a jiyan na fada masa sai a basu hakuri tunda kana da wadda kake so bai kyautu ace sai ka aureta ba. Ni a tsarina ma Allah Ya gani nafi son ku rinka auren junanku. Ita idan aurenta ya tashi sai yayi mata duk abinda uba yake yiwa 'yarsa"
Wannan shine son kai. Babu yadda za'ayi Awwab yayi shiru da wannan magana ya karbi hukuncin Alh Baba batare da ya gabatar masa da nasa uzurin ba.
"Alhaji kayi min izini na auresu su biyu. Ina iya fara auren Ghazalatu sai na aureta daga baya"
Rai a bace ya soma fada "abinda uban naka ya turoka ka fada min kenan. Wato saboda jiya nace ban yarda ba shine kai ka shafawa idonka toka zaka yi min rashin kunya?"
"Alhaji kayi hakuri ba haka bane"
"To nace na soke bazaka aureta ba. Banda son dorawa kai wahala ina zaka kai mata biyu Muhammad? Idan kana son yiwa mahaifinka biyayya ne kaje abinka shima ai karkashina yake"
Ran Awwab sai kuna yake ya kasa daurewa "Alhaji wallahi ina sonta"
Kallon da Alh Baba ya watsa masa a lokacin kallo ne na tsananin bacin rai.
Ghazalatu da ta gama jin komai hankalinta bai tashi sosai ba sai da taji furucin Awwab. Kuka ta fashe dashi ga bakinciki ga kishi ta bar wurin a guje. Daga Alhajin har Awwab sun jiyo muryarta.
"Ka tashi kabi sawun kanwarka ku daidaita. Na gama magana Muhammad bana son sake jin wata magana"
"Alhaji...."
"Ka tashi ka tafi nace"
Yana fita daga falon waje ya nufa ya shiga mota ya kifa kai akan sitiyari.
"Ya Allah" ya furta a hankali ko ina na jikinsa yana cikin tashin hankali. Bazai taba iya hakura ko rabuwa da Alheran ba. Ya barta a kira shi da me? Butulu ko mayaudari? A cikin abinda bai gaza sati biyu ba ya fada matsananciyar soyayyarta kuma itama ya koya mata sonsa. Akwai kunya da nauyi sosai tsakanin iyayensu wanda bai cancanci a sanadiyarsa ya kawo wata baraka a tsakani ba kamar yadda baya fatan kawo baraka ga danginsa. Shi da Ghazalatu sunyi dumu dumu a cikin dangi. Idan baka dubesu ta nan ba zaka dubesu ta can. Hadi ne tun daga kakanni an cakude da juna.
Dakin mahaifiyarta Mummy Gambo ta wuce kai tsaye tana kuka kamar ranta zai fita. Babu abinda yake mata yawo a ka sai jin da tayi Awwab da bakinsa yace yana son wannan yarinyar.
Mummy ta taso ta tarbeta da sauri "me ya sameki?"
"Mummy Yaya ne...Yaya Awwab baya sona"
"Ban gane ba, idan wani shirmen fadanku ne dama kada ki soma gaya min. Kije can ku sasanta"
"Mummy wata yake so. Yaci amanata wallahi 'yar wannan makauniyar da ta zauna gidansu yake so"
Nata hankalin sai yafi na Ghazalatu tashi "dena kuka bari na kira Hassana naji daga bakinta."
Mami tana daki da Zahra wadda take ta kuka tana bata hakuri Mummy ta kira. Shawara ta yanke gara ta sanar da ita ko Hussaina su tayata bawa Zahra baki.
Sai da ta saita muryarta don ita din ma zuciyarta a karye take "Mummyn yara yanzu kuwa nake shirin nemanki."
"Kina shirin nemana ki fada min kun yiwa Awwab mata ko" tace cikin gatse.
Mami da bata san wainar da ake toyawa ba tayi dariya "hala yazo ya fada miki. 'Yar wajen Mairama ce. Kin ganeta ai wadda tazo ta kwana mana biyu matar ....."
Kit taji shiru Mummy ta kashe wayar. Kallon wayar hannunta tayi da mamaki sai kuma ta soma kiranta missed calls biyar bata dauka. Abin ya dameta ta lallaba Zahra ta fita ta tafi dakin Daddy.
Mummy Gambo ta cika tayi fam. Ita Mami zata wulakantawa 'ya har tana fada mata wadda suka zabawa Awwab. Kenan basu aminta da ya auri Ghazalatu ba. A tunaninta tafi karfin haka a wurin 'yar uwarta ta. Kallon Ghazakatu tayi da take ta kuka tana rarrashinta ta kira Daddy Haroun a waya don ya fita unguwa. Cewa tayi kawai ya dawo gida babu lafiya yace to.
Mami tana zuwa dakin Daddy shi kuma ta same shi yana waya da Alh Baba yana ta ban hakuri. Alh Baba yace ya fadawa Awwab lallai aurensa da Ghazalatu babu fashi. Wurgi ta ga yayi da wayarsa ta karaso kusa dashi da sauri.
"Daddy lafiya?"
"Ki bari muyi maganar nan bayan bikin su Fauziyya kamar yadda Alh Baba yace"
"Wallahi hankalina ya tashi. Tun jiya ka chanja min gabaki daya. Yanzu Gambo ta kirani tana cewa munyiwa Awwab mata nace mata eh kawai ta kashe wayar kamar wadda na yiwa wani abu"
Ran Major tuni ya soma baci kuwa. Yasan Gambo da masifa amma baya son duk abinda zai sosa ran Mami. Ga dadin haushin akan 'yarta ne ake son kirikiri a gwada son kai. Meye matsalar ya auri mata biyu da za'a ce dole sai an janye maganar Radhiya. Radhiya diyar Zayyanunsa.
Sallamar Awwab din suka rinka ji kana jinsa kasan baya cikin nutsuwa. Izinin shigowa Daddy yayi masa yana zuwa ya zube masa.
"Daddy Alh Baba yace bazan auri Alheran ba. To wallahi idan bai amince ba itama Ghazalatun na rantse da Allah ko an daura sai na saketa"
"Kai Awwab, kana cikin hankalinka kuwa? Daddy me yake faruwa ne kun kara sakani cikin duhu"
"Fita ka tafi dakinka" Daddy yace ransa shima a baci. Dakin gabadaya ya juye walwalar ma'abotansa ta fi kamar an kadata da iska.
Tattaro nutsuwarsa ya daure yayi ya fadawa Mami halin da ake ciki. Boyewar bata da amfani tunda Gambo ta sani.
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Yanzu sai Gambo ta ga kamar da gangan nayi"
"Gambo kike ji ko kuwa halin da Awwab zai shiga da yaran nan"
"Daddy ni fa ban ga wata gagarumar matsala a cikin wannan abu ba. Awwab namiji ne saboda haka zai iya aurensu duka. Ciki mu mun isa muce ga wadda zai zaba ya bar dayar? Babu wadda mahaifinta baiyi mana halacci ba saboda haka ka kwantar da hankalinka in sha Allahu komai zai zo da sauki"
A sanyaye yace "Alh Baba yace bazai auri mata biyu ba kuma su Baba sun amince"
Kanta ta dora akan kafadarsa ta kwantar da murya domin kwantar masa da hankali "mu bi komai a sannu saboda kuskure daya zai iya janyo mana rikici a dangi ko tare da iyayen Mairama wanda bana fata. Gobe muje mu roki arzikin suyi hakuri su amince ya auresu su biyun"
Kalamai masu kwantar da hankali ta rinka amfani dasu wurin sanyayawa mijinta rai suka dauki dogon lokaci suna shawara akan wannan matsala.
Tunda Awwab ya shiga daki bai fito ba sai asuba. Kallo daya Major yayi masa ya san cewa da wahala idan ya runtsa. Soyayyar Awwab da Alheran daga Allah ce. Ya tabbatar duk wannan tashin hankalin saboda an hanashi aurenta ne.
**********
Da wuri aka gama komai na sallamar Ummi daga asibiti. Abin da mamaki matuka ta shafe shekaru kusan goma da makanta yau ita ce take da idanun kallon Radhiya da Karami. Bayan an bata gilashinta tana kallonsu ta fashe da kuka. Karami bai baro mahaifinsa da komai ba sai fari da ya dan dara shi wanda ta alakanta shi da kuruciyarsa sai kuma tsaho da shi Zayyan din yafi dan nasa. Radhiya kuwa tafi dauko kamanni da ita sai dai ta rasa inda ta samo wannan kirar jiki. Mairama doguwa ce siririya mai kyaun sura da daukar ido yayin da Radhiya take a murje babu rama amma baza'a a kirata mai kiba ba. Jikinta a cike yake ko ta ina. Yanayin hancinta sam baiyi kama da na Umminta ko mahaifinta ba. Idan tayi murmushi sai kaji kamar ka dauketa saboda yadda fuskar take nuna zallan yarinta idan kumatunta ya lotsa ciki.
Lokacin da suka hada ido da Zainab sai sabon kuka.
"Haka kika koma wata 'yar gayu Zainab dina"
Yaran suna dariya iyayensu suka rungume juna.
"Muje gida kafin ki bar garin nan sai kin zama 'yar gayu kema. Ba biki zakuyi ba....hmmm Allah Mairama sai nasa idanu sun koma kanki a wurin bikin nan" suka yi dariya.
A gaban mota Ummi ta zauna Radhiya da Nene Marka suna baya. 'Yan samari kuwa adaidaita sahu tace su shiga su biyo bayansu.
Sunje gida Ummi ido ya bude ta ga halin da Baba Hadir yake ciki. Tana kuka Zainab tace mata kada ta jangwalo idanun tayi hakuri haka.