Sashe 9
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To kiyi dariya in gani"
Dariya ya bata ya kafeta da ido wai tayi dariya. Motsin mutane suka fara ji daga waje ya tashi da sauri ya bude kofar. Zayyan ne da wani security soja sun kinkimo katon kwali ga wasu kwalayen biyu kuma a kasa daga gefe. Yana ganin Awwab yace ya je ya fadawa Mairama ta koma daki zasu shigo da kaya. Ta ji me yace kafin Awwab din ya dawo ta koma ciki ta kwanta.
Suna shigo da kayan ya fadawa Zayyan tana amai. Nan fa hankalinsa ya tashi ya bishi dakin bayan sun gama shigo da kayan.
A kwance take tana jin ya shigo ta tashi zaune.
"Mairam me ya same ki?"
Sai da ta harari Awwab ta bashi amsa "ulcer ta ce ta tashi tun dazu da na sha coke kirjina ke suya"
"Shine baki taba fada min kina da ulcer ba suk sati nake ajiye miki crate din minerals? To anyi an gama"
Bata da wata ulcer a iya saninta amma ta ki jinin asibiti. Kitchen din yaje ya zubo abinci.
"Nasan baki ci ba, tashi"
Wani aman taji ya taho mata daga ganin abincin ta daure "Awwab baici ba ka bashi zan ci anjima"
"Nima bazan ci ba sai kinci" Awwab din yace yana marairaicewa.
Zayyan ya janyo hannunsa ya zauna a kusa dashi da kyar ya samu ya karba yana ci yana mata hira.
"Kayi min kwacen mata kirikiri yaron nan"
Mairam ta soma dariya da Awwab ya dage sai ya fada masa me yake nufi. Sai can yamma ya tafi ya fadawa Maminsa bata da lafiya. Taso zuwa amma tunda Zayyan yana gida sai ta hakura sai gobe.
Sai dare Zayyan ya bude kwalayen da suka zo dasu. Daya firinji ne madaidaici mai kofa daya amma da freezer daga sama. Sai kuma TV da bidiyo duka sababbi. Mairama godiya harda kuka don murna.
Bayan kwana biyu kullum tana fama da amai da jiri ya kaita asibiti aka basu tabbacin ciki ne da ita. Tamkar ya hadiyeta don farinciki. Gani yake yanzu zai sami abinda zai kira nasa, jininsa sosai.
**********
Lokaci yana tafiya al'amura suna faruwa garesu. Captain Mustapha ya sami karin girma zuwa mukamin Major bayan ya dawo daga wani aiki da aka tura shi Warri. Zayyan da Hadir kuma sun zama Lieutenants.
Cikin Mairama yana da wata shida amma idan ka ganta sai ka rantse bazata kara kwana ba zata haihu. Su Mami sun gama sadakarwa ‘yan biyu ne a cikin. Bata wani laulayi sosai sai cin abinci akai akai tayi bulbul ta sake kyau da cikowa. Kwakkwaran motsi idan tayi Zayyan ya rinka cewa yaya akayi. Zainab ma cikin gareta wata uku amma ita laulayi yake saka ta don bata iya komai yanzu sai kwanciya duk ta rame abin tausayi. Mazajensu na fita suke tarewa a gidanta su taimaka mata da aikin gida. Mami tayi ta kokarin hana Mairama amma bata ji, tafi ganewa motsa jikin dama kuma haka ake so ga mai juna biyu.
Yau litinin suna tare a gidan Zainab su Awwab suka dawo daga makaranta. Tun da suka ga gidan a rufe sun san inda Maminsu ta tafi sai suka bita. A falo suke zaune suna hira yau Zainab din jikinta da kwari ba kamar kwanaki ba.
Kowa yana cin abinci an hadawa yaran a tray karami na silver iyayensu su ma sun hada tare. Zainab ce ta kula da Awwab gabadaya idanunsa suna kan Mairama. Idan ta yamutsa fuska sai yayi kamar zaiyi kuka.
“Awwabu ya aka yi ne kake ta kallon mamanka?”
“Anti baki ga cikinta ba kullum yana kato kamar na maman Ebere”
Mami ta tuntsire da dariya “kai kuma baka son cikinta yayi irin na maman Ebere din ne?”
Ya gyada kai “saboda fashewa zaiyi watarana, haka Ebere tace na mamansu ya fashe a asibiti.”
Zahra ta kai masa bugu a kafada “Kai Hamma haihuwa zatayi fa mu sami baby” Hamma shine sunan da Mairama tace su rinka kiransa dashi don da fari Awwab kawai suke cewa.
Maminsu ya kalla a tsorace “kinji tana rashin kunya Mami, ni dai ba ruwana”
Tsokanarsa Zainab ta shiga yi tana cewa Mairama danta yakware a wautar ‘yan fari. Da abun ya ishe shi sai ga hawaye Zahra da Fauziyya aka sami na yi. Mairama ta janyo shi kusa da ita.
“Kyalesu baby zan dauko maka a asibiti idan nawa cikin ya fashe kai kadai zaka rinka dauka.”
Wata dariya ya saki da ta kara masa kyau da nuna kuruciyarsa yana murna, har da yiwa su Fauziyya gwalo. A haka rayuwarsu take tafiya komai nasu cikin aminci tamkar ‘yan uwa na jini.
Ranar da nakuda ta kama Mairama Zayyan sun tafi gidan gwamnati shugaban kasa zai kawo ziyara. Nauyi da kunya ya sanya ta kasa fada masa tun gabanin asuba da ta fara ciwon har ya fita. Gashi abu yafi karfinta zamani ba na waya ba bare ta nemi taimako. Allah ne ya kawo mata Awwab tana cikin wannan matsanancin halin ta daure tace yaje gida ya kira Mami kuma ya tabbata ta taho yanzun nan. Ya kusa shekara tara a lokacin shiyasa duk da bata fada ba jikinsa ya bashi ba lafiya ba.
A guje ya koma gida sai gasu cikin mintuna kalilan. Tana ganinta tace ya fita ta shiga daki ta taimaka mata su fito kawai ta fara nishi. Mami ta san babu yadda zatayi tun da ta hango kai yana neman fitowa a take Allah Ya sako mata karfin zuciya ta karbi haihuwar santaleliyar yarinyar da Mairama ta haifa.
Tubarakallah yarinyar akwai girma da kiba taci ta koshi tun a ciki ga kyau. Kukan da ta chanyara ne ya sanar da gidan da yake jikin nasu an sauka. Matar gidan bayerabiya ce suna kiranta Maman Dolapo ta shigo da sallamarta domin su ma musulmai ne. Awwab aka tura ya kira Zainab itama tazo suna ta murna aka dora musu ruwan wanka. Yarinya tana ta wutsil wutsil kakkarfa da ita.
Mami girman yana gareta ita ta yiwa Mairama wanka. Jaririya kuwa Maman Dolapo ta roki alfarmar a barta tayi mata irin nasu na yarbawa. Babu wanda ya hana saboda zaman mutumci suke yi da ita. Sun kuwa ga wanka ba irin wanda suka saba ba. Ta wanke yarinyar nan sosai ga mamakinsu harda manja mai kyau ta dauko daga gidanta ta shefe jikin yarinyar ta mitstsiketa sosai sannan aka fara wankan da kyau ana fitar da datti da maikon manjan. Ko da ta gama yarinya kana tabata jikin nan subul ta kara wani haske kamar jini ya fito. Lallausan kayan sanyi aka sanya mata lokaci na damuna sannan akace Mairama ta bata nono. Nan fa ake yinta kunyar jama’a ko karbarta ta kasa. Zainab ta kamata ta maidata daki. Zata rufe mata kofa Awwab yayi kekam dole ta barshi ya bi bayan mamansa ana musu dariya.
Babu abinda makota basu yiwa Mairama ba. Daki ta shiga tayi kukan rashin dangin uwa da basu damu da ita ba. Da kanta ta nemi Zayyan akan bata son zuwa gida wanka saboda ta sani ba wata kulawa da zata samu. Bayan auren nasu sunje sau daya bata ji dadin gidan ba ko kadan. Wani kallo na kyashi ake watsa mata, Yadikko ce kadai mai janta a jiki. Malamijo kuwa zubar da girma yayi gaban Zayyan yana fada masa yadda yake cikin mawuyacin halin kula da iyali. Allah Yasa sunyo musu tsaraba irin ta Sakkwato amma duk da haka sai da ya bashi kudi. Kurewar lokaci yasa basu tsaya a gidan Salame ba. Abin da bata sani ba da gangan Zayyan yayi haka don ko kadan baya kaunar yadda Salamen take yiwa matarsa ita kuma bata gani.
Ba su suka dawo gida ba sai daya saura na dare. Lokacin kowa ya watse hatta Mami ta tafi saboda yara sun fara bacci. Mairama da jaririyarta ma baccin suke jiki ya gaji ga wankan da suka sha. Ko ina a gyare tsaf gidan ya bude kofar dakin a hankali don kada ya tasheta ko fitila bai kunna ba. Kayansa ya cire yaje yayi wanka ya fito yana komai a nutse don baya son damunta. Duhun dakin yasa garin neman robar mai ya tunkudu wani abu daga kan madubin ya fado da karfi. Karar ce ta tashi baby din yaji ana inya inyaa.
Hanyar kofa ya nufa da fari ya ajiye sojancin na wucin gadi, sai yaji muryar Mairama tana cewa shhhh. Da mugun sauri ya kunna fitila idanunsa a kan gadon. Kyakkyawan gamo yayi. Masoyiyarsa abar kaunarsa ya gani tare da baby kunshe cikin shawul fari tas.
Zuciyarsa ce tayi wani irin nauyi ya tako gaban gadon a hankali ya zauna a gefenta. Murmushi ta sakar masa kafin ta dora masa jaririyar a kan hannuwan da ya miko mata. Rungumesu yayi tare yana fidda numfashi da sauri. Mairama sai ta soma hawayen farinciki ta kara shiga jikinsa yana yiwa baby addu’a. Sun dauki lokaci a haka kafin ya bude fuskarta tana tandar baki.
“Yunwa take ji ko?” ya kalli Mairama
Karbarta tayi ta juya masa baya zata shayar da ita ya hawo gadon ya zagaya gabanta “kada ki cuceni da kunya”
Ba yadda ta iya yana ta kallonsu cike da sha’awa kamar wani zai ce ba nasa bane. Bai iya tashi ba har ta gama ya ga babyn tayi bacci ita ma idanu sun fara rufewa.
Kwanciya ya gyara musu ya dauko darduma ya shimfida yana nafilar godiyarsa ga Allah. Duk gajiyar da ya kwaso ranar babu wani bacci da ya iya yi sai gadinsu har asuba tayi. A masallaci Major Mustapha da Hadir su ka yi masa barka tare da sauran abokan aikinsu ana taya shi murna. Papa Dolapo ya tsokane shi wai Allah Yasa dai ba mai kiriniya bane kamarsa akayi dariya.
Aikinsu bai kare ba zasu koma gidan gwamna. Kafin su tafi Major Mustapha da Hadir su ka je gidan ganin baby da kuma yi mata addu’a. Zayyan ya dan taba Hadir yana yi masa magana da ido. Ya san zancen shiyasa ya dubi Major din.
“Sir kaine zaka rada mata suna fa, kayi mata huduba”
Wani iri yaji yadda yaran nan suke matukar girmama shi tamkar yayansu na jini “wane sunan zan saka mata?”
Dariya ya bata ya kafeta da ido wai tayi dariya. Motsin mutane suka fara ji daga waje ya tashi da sauri ya bude kofar. Zayyan ne da wani security soja sun kinkimo katon kwali ga wasu kwalayen biyu kuma a kasa daga gefe. Yana ganin Awwab yace ya je ya fadawa Mairama ta koma daki zasu shigo da kaya. Ta ji me yace kafin Awwab din ya dawo ta koma ciki ta kwanta.
Suna shigo da kayan ya fadawa Zayyan tana amai. Nan fa hankalinsa ya tashi ya bishi dakin bayan sun gama shigo da kayan.
A kwance take tana jin ya shigo ta tashi zaune.
"Mairam me ya same ki?"
Sai da ta harari Awwab ta bashi amsa "ulcer ta ce ta tashi tun dazu da na sha coke kirjina ke suya"
"Shine baki taba fada min kina da ulcer ba suk sati nake ajiye miki crate din minerals? To anyi an gama"
Bata da wata ulcer a iya saninta amma ta ki jinin asibiti. Kitchen din yaje ya zubo abinci.
"Nasan baki ci ba, tashi"
Wani aman taji ya taho mata daga ganin abincin ta daure "Awwab baici ba ka bashi zan ci anjima"
"Nima bazan ci ba sai kinci" Awwab din yace yana marairaicewa.
Zayyan ya janyo hannunsa ya zauna a kusa dashi da kyar ya samu ya karba yana ci yana mata hira.
"Kayi min kwacen mata kirikiri yaron nan"
Mairam ta soma dariya da Awwab ya dage sai ya fada masa me yake nufi. Sai can yamma ya tafi ya fadawa Maminsa bata da lafiya. Taso zuwa amma tunda Zayyan yana gida sai ta hakura sai gobe.
Sai dare Zayyan ya bude kwalayen da suka zo dasu. Daya firinji ne madaidaici mai kofa daya amma da freezer daga sama. Sai kuma TV da bidiyo duka sababbi. Mairama godiya harda kuka don murna.
Bayan kwana biyu kullum tana fama da amai da jiri ya kaita asibiti aka basu tabbacin ciki ne da ita. Tamkar ya hadiyeta don farinciki. Gani yake yanzu zai sami abinda zai kira nasa, jininsa sosai.
**********
Lokaci yana tafiya al'amura suna faruwa garesu. Captain Mustapha ya sami karin girma zuwa mukamin Major bayan ya dawo daga wani aiki da aka tura shi Warri. Zayyan da Hadir kuma sun zama Lieutenants.
Cikin Mairama yana da wata shida amma idan ka ganta sai ka rantse bazata kara kwana ba zata haihu. Su Mami sun gama sadakarwa ‘yan biyu ne a cikin. Bata wani laulayi sosai sai cin abinci akai akai tayi bulbul ta sake kyau da cikowa. Kwakkwaran motsi idan tayi Zayyan ya rinka cewa yaya akayi. Zainab ma cikin gareta wata uku amma ita laulayi yake saka ta don bata iya komai yanzu sai kwanciya duk ta rame abin tausayi. Mazajensu na fita suke tarewa a gidanta su taimaka mata da aikin gida. Mami tayi ta kokarin hana Mairama amma bata ji, tafi ganewa motsa jikin dama kuma haka ake so ga mai juna biyu.
Yau litinin suna tare a gidan Zainab su Awwab suka dawo daga makaranta. Tun da suka ga gidan a rufe sun san inda Maminsu ta tafi sai suka bita. A falo suke zaune suna hira yau Zainab din jikinta da kwari ba kamar kwanaki ba.
Kowa yana cin abinci an hadawa yaran a tray karami na silver iyayensu su ma sun hada tare. Zainab ce ta kula da Awwab gabadaya idanunsa suna kan Mairama. Idan ta yamutsa fuska sai yayi kamar zaiyi kuka.
“Awwabu ya aka yi ne kake ta kallon mamanka?”
“Anti baki ga cikinta ba kullum yana kato kamar na maman Ebere”
Mami ta tuntsire da dariya “kai kuma baka son cikinta yayi irin na maman Ebere din ne?”
Ya gyada kai “saboda fashewa zaiyi watarana, haka Ebere tace na mamansu ya fashe a asibiti.”
Zahra ta kai masa bugu a kafada “Kai Hamma haihuwa zatayi fa mu sami baby” Hamma shine sunan da Mairama tace su rinka kiransa dashi don da fari Awwab kawai suke cewa.
Maminsu ya kalla a tsorace “kinji tana rashin kunya Mami, ni dai ba ruwana”
Tsokanarsa Zainab ta shiga yi tana cewa Mairama danta yakware a wautar ‘yan fari. Da abun ya ishe shi sai ga hawaye Zahra da Fauziyya aka sami na yi. Mairama ta janyo shi kusa da ita.
“Kyalesu baby zan dauko maka a asibiti idan nawa cikin ya fashe kai kadai zaka rinka dauka.”
Wata dariya ya saki da ta kara masa kyau da nuna kuruciyarsa yana murna, har da yiwa su Fauziyya gwalo. A haka rayuwarsu take tafiya komai nasu cikin aminci tamkar ‘yan uwa na jini.
Ranar da nakuda ta kama Mairama Zayyan sun tafi gidan gwamnati shugaban kasa zai kawo ziyara. Nauyi da kunya ya sanya ta kasa fada masa tun gabanin asuba da ta fara ciwon har ya fita. Gashi abu yafi karfinta zamani ba na waya ba bare ta nemi taimako. Allah ne ya kawo mata Awwab tana cikin wannan matsanancin halin ta daure tace yaje gida ya kira Mami kuma ya tabbata ta taho yanzun nan. Ya kusa shekara tara a lokacin shiyasa duk da bata fada ba jikinsa ya bashi ba lafiya ba.
A guje ya koma gida sai gasu cikin mintuna kalilan. Tana ganinta tace ya fita ta shiga daki ta taimaka mata su fito kawai ta fara nishi. Mami ta san babu yadda zatayi tun da ta hango kai yana neman fitowa a take Allah Ya sako mata karfin zuciya ta karbi haihuwar santaleliyar yarinyar da Mairama ta haifa.
Tubarakallah yarinyar akwai girma da kiba taci ta koshi tun a ciki ga kyau. Kukan da ta chanyara ne ya sanar da gidan da yake jikin nasu an sauka. Matar gidan bayerabiya ce suna kiranta Maman Dolapo ta shigo da sallamarta domin su ma musulmai ne. Awwab aka tura ya kira Zainab itama tazo suna ta murna aka dora musu ruwan wanka. Yarinya tana ta wutsil wutsil kakkarfa da ita.
Mami girman yana gareta ita ta yiwa Mairama wanka. Jaririya kuwa Maman Dolapo ta roki alfarmar a barta tayi mata irin nasu na yarbawa. Babu wanda ya hana saboda zaman mutumci suke yi da ita. Sun kuwa ga wanka ba irin wanda suka saba ba. Ta wanke yarinyar nan sosai ga mamakinsu harda manja mai kyau ta dauko daga gidanta ta shefe jikin yarinyar ta mitstsiketa sosai sannan aka fara wankan da kyau ana fitar da datti da maikon manjan. Ko da ta gama yarinya kana tabata jikin nan subul ta kara wani haske kamar jini ya fito. Lallausan kayan sanyi aka sanya mata lokaci na damuna sannan akace Mairama ta bata nono. Nan fa ake yinta kunyar jama’a ko karbarta ta kasa. Zainab ta kamata ta maidata daki. Zata rufe mata kofa Awwab yayi kekam dole ta barshi ya bi bayan mamansa ana musu dariya.
Babu abinda makota basu yiwa Mairama ba. Daki ta shiga tayi kukan rashin dangin uwa da basu damu da ita ba. Da kanta ta nemi Zayyan akan bata son zuwa gida wanka saboda ta sani ba wata kulawa da zata samu. Bayan auren nasu sunje sau daya bata ji dadin gidan ba ko kadan. Wani kallo na kyashi ake watsa mata, Yadikko ce kadai mai janta a jiki. Malamijo kuwa zubar da girma yayi gaban Zayyan yana fada masa yadda yake cikin mawuyacin halin kula da iyali. Allah Yasa sunyo musu tsaraba irin ta Sakkwato amma duk da haka sai da ya bashi kudi. Kurewar lokaci yasa basu tsaya a gidan Salame ba. Abin da bata sani ba da gangan Zayyan yayi haka don ko kadan baya kaunar yadda Salamen take yiwa matarsa ita kuma bata gani.
Ba su suka dawo gida ba sai daya saura na dare. Lokacin kowa ya watse hatta Mami ta tafi saboda yara sun fara bacci. Mairama da jaririyarta ma baccin suke jiki ya gaji ga wankan da suka sha. Ko ina a gyare tsaf gidan ya bude kofar dakin a hankali don kada ya tasheta ko fitila bai kunna ba. Kayansa ya cire yaje yayi wanka ya fito yana komai a nutse don baya son damunta. Duhun dakin yasa garin neman robar mai ya tunkudu wani abu daga kan madubin ya fado da karfi. Karar ce ta tashi baby din yaji ana inya inyaa.
Hanyar kofa ya nufa da fari ya ajiye sojancin na wucin gadi, sai yaji muryar Mairama tana cewa shhhh. Da mugun sauri ya kunna fitila idanunsa a kan gadon. Kyakkyawan gamo yayi. Masoyiyarsa abar kaunarsa ya gani tare da baby kunshe cikin shawul fari tas.
Zuciyarsa ce tayi wani irin nauyi ya tako gaban gadon a hankali ya zauna a gefenta. Murmushi ta sakar masa kafin ta dora masa jaririyar a kan hannuwan da ya miko mata. Rungumesu yayi tare yana fidda numfashi da sauri. Mairama sai ta soma hawayen farinciki ta kara shiga jikinsa yana yiwa baby addu’a. Sun dauki lokaci a haka kafin ya bude fuskarta tana tandar baki.
“Yunwa take ji ko?” ya kalli Mairama
Karbarta tayi ta juya masa baya zata shayar da ita ya hawo gadon ya zagaya gabanta “kada ki cuceni da kunya”
Ba yadda ta iya yana ta kallonsu cike da sha’awa kamar wani zai ce ba nasa bane. Bai iya tashi ba har ta gama ya ga babyn tayi bacci ita ma idanu sun fara rufewa.
Kwanciya ya gyara musu ya dauko darduma ya shimfida yana nafilar godiyarsa ga Allah. Duk gajiyar da ya kwaso ranar babu wani bacci da ya iya yi sai gadinsu har asuba tayi. A masallaci Major Mustapha da Hadir su ka yi masa barka tare da sauran abokan aikinsu ana taya shi murna. Papa Dolapo ya tsokane shi wai Allah Yasa dai ba mai kiriniya bane kamarsa akayi dariya.
Aikinsu bai kare ba zasu koma gidan gwamna. Kafin su tafi Major Mustapha da Hadir su ka je gidan ganin baby da kuma yi mata addu’a. Zayyan ya dan taba Hadir yana yi masa magana da ido. Ya san zancen shiyasa ya dubi Major din.
“Sir kaine zaka rada mata suna fa, kayi mata huduba”
Wani iri yaji yadda yaran nan suke matukar girmama shi tamkar yayansu na jini “wane sunan zan saka mata?”