Sashe 47
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk abinda Ghazalatu tayi na saurin zama a gaban Radhiya ta gani. To dama ita dinma yanzu bata ra'ayin gaban. Bata son zama kusa da Awwab din saboda yadda yake sawa tajita kamar ba ita ba.
Kusa da Zayyana ta zauna a tsakiya tana ta zuba surutu. Awwab ya kasa hakuri ya gyara madubin motar yadda zai rinka ganinta da kyau. Yana saita madubin suna hada ido da Emzee. Hade girar sama da kasa yayi da Emzee ya dago masa hannu yana murmushin tsokana. Kansa ya janye gefe Awwab ya hango Radhiya tana nunawa Zayyana makarantar da tayi primary.
"Ranar hutun da muka gama primary 5 muka yi dambe da Danmama a wurin bishiyar can, ko me yake yi yanzu oho"
"Damben fada kika yi dashi?" Zayyana tace da mamaki.
"Ke baki ji wulakancin da yayi min bane. Malamijo suke zagi ni kuwa na nuna musu matsayinsu."
"Zan so sake ganin Danmama, yanzu sai dai muyi gaisuwar mutumci idan an hadu"
Wani azababben kishi ne ya turnuke Awwab "duk yawan 'yan uwanki basu ishe ki ba sai kin hada da abokin fadanki? Wai shin ke namiji ce ne ma kike fada da maza?"
Ita me tace da zai rinka yi mata fada daga labari. Kallonta yayi ta madubin ta murtuke fuska "kuma idan na zama soja ....."
"Stop dreaming babu inda zaki. Idan bazaki yi karatu irin na kowa ba sai ki hakura"
A duniya ita tana da burin da ya wuce zama soja ne? Duk mai son hanata bai nemi zaman lafiya ba. Ko da kuwa Hamma Awwab din da take ji dashi ne. A take ta bata rai "ai dai Daddy yace zai nema min"
"To zamu gani" yace yana shiga kwanar da Emzee ya nuna masa.
Fauziyya tace "Hamma ka barta tayi kawai mu sami soja mace. Ni har hangota nake yi. Kasan Radhiya bata daukar raini kowa zai shiga hankalinsa"
"Idan kin haifi taki 'yar sai ki turata amma wannan dai na gama magana"
"Kai Hamma kada fa mu ganku a rana wannan kanwar taka bata iya fada ba. Sai ku kwana kuna yi"
Bai ce komai ba yayi parking a gefen gonar. Tun daga inda suke suna iya hango shanu da tumaki. Malamijo fa akwai kudi arziki ne kawai babu don bashi da zuciyar fitar da kudinsa a mora. Kowa ya fita saura Ghazalatu da Awwab a motar. Gani yayi bata da niyar fita ya koma ya zauna yana tambayarta me taki fita.
"Yayana kaki zama muyi hira, nayi maka wani abu ne?" Ta marairaice masa.
Tausayinta yaji domin daga baro Abuja zuwa Katsina, Kano da Sumaila duka tayi dominsa ne.
"Kiyi hakuri, kinga ban samu na zauna bane"
"Amma ka sami lokacin hira da kanwarka ko?" Tace cikin yanayin da ke nuna tsantsar kishi.
"Me yasa Alheran ta tsaya miki a rai ne?"
"Shakuwar taku tayi yawa Yayana, bana son abin ya koma wanda bazai mana dadi ba a gaba"
"Idan zakiyi min adalci Ghazalatu kin sani cewa duk wanda yasanni da su Mami to dole ya taba jin zancen Daddyn Alheran, Umminta da ita kanta ko da sau daya ne. Family dinsu suna da matukar daraja a idanun iyayena" tunawa yayi da zancen rasuwar Zayyan da Daddy yayi masa a daren da zai taho Kano da nanata masa ko bayan ransa ya taya shi rikon amanar iyalinsa. A daren sai da ya zubar da hawaye. Yayi zaton idan ya ga Radhiya kawai shakuwarsu ta baya zai tuna kila ya ga ma ta sauya daga sanin da yayi mata. Sai ya zamana abin ba haka yake ba. Ganin kwana daya Alheran nema take ta shige kowane bangare na jikinsa.
"Tunanin me kake yi ne?"
"Fito muje ba dadewa zamuyi ba" yace yana fita.
Dole tabi bayansa a ran ta tana jin dole ne ma suna komawa ya sanar da nasa iyayen idan ma kudin aure ko saka rana za'ayi duka ayi da wuri kafin abin yazo yafi karfinta.
Yawo su Radhiya ke yi sosai ga masu kiwon dabbobin suna ta bin bayansu ana musu karin bayani. Wurin wata saniya suka je ana tatsar nono. Mutumin da yake tare dasu yace ta haihu ne wani sa ya tunkuye dan makarakin bai shura ba.
"Ina son yin tatsar nima" Zayyana tace da Radhiya wadda lokaci lokaci sai ta waiga baya ta gani ko su Awwab sun fito. Haushi ne ma ya kamata saboda yace bazata yi soja ba a gaban mutane ta yi gaba cikin takaici tana jin zuciyarta tana nauyi.
"Muje na koya miki" Emzee yace da Zayyana bayan ya gama karantar yayarsa.
Irin hular kaba da suke sawa su kare rana mai fadin kasa Radhiya ta gani wani cikinsu ya cire ta dauka ta kwama a kanta ta sami kasan bishiya ta zauna akan wani dutse tana kallon su Fauziyya harda Ibrahim kowa tatsar nono yake yi. Idan wannan ya gwada sai ya matsa wani yayi.
Awwab da Ghazalatu ta gani suna tahowa taji wani abu na taso mata daga kirji har wuya. Rufe idanu tayi ta ja hular ta dora akan fuskarta. Duk abinda take yi Awwab na kallonta har ya karaso inda take. So take ta bude fuskar saboda wani sihirtaccen hamami da yake tashi a ciki amma bata san ta ina Awwab ko Gayanatunsa zasu bullo mata ba. Babu wanda take son gani cikinsu. Wari ne ya isheta ba arziki ta cire hular tayi jifa da ita sai a cinyar Awwab da zamansa kenan.
"Wai Allah, wannan shi ake kira gumama inji takari. Wannan uban wari....."
Kasa karasawa tayi tana kallonsa da hular a cinyarsa tsabar mugunta ta rinka dariya. Shi da budurwarsa suka janyo mata saka hular ai.
"Kina da matsala, kin gama bata rai kin zo kina dariya" yace yana kara rungume hular
"Na ga ka kama hula ka rungume ne kamar ta ka"
Miko mata yayi ta goce da sauri kada ta sake tabawa "nagode, ungo abinki tunda taki ce"
"Warin maza take wallahi" ta kwashe da dariya da ta ga ya tashi da sauri hular ta fadi kasa.
Yamutsa fuska yayi yana kallon yadda take jindadi hankali kwance "wannan wace irin kalma ce haka ko dadin ji babu?"
Idanunta da ya yarda suna dauke masa hankali ta watsa masa "wace kalmar? au wai warin maza. Kada kace min baka ji ba. Dauko ka sansana"
Dukawa tayi zata dauko yasa kafa yayi ball da hular yana kada kai yana kai hannuwansa wurin hancinsa ya kawar da kansa da sauri "dirty girl wannan kika dora a fuskarki"
"Rashin sani, nasan yanzu fuskata wari take yi ko"
"Ban sani ba" yace yana yin gaba. Daya daga cikin mutanen ya tambaya ina zai sami ruwa yace sai dai a rijiyar da suke debowa dabbobin. Ina wani bambanci da hular da ruwan da ya tabbatar shima bashi da tsafta. Emzee ya kira ya fada masa ruwa yake so da sabulu.
Kallon rashin fahimta yayi masa "wanka zaka yi a nan?"
Awwab ji yayi kamar ya hada shi da Radhiya ya musu duka. Ghazalatu da sauran duka kallonsa suke yi.
"Abu na taba zan wanke hannuna shikenan!"
Kamar yadda ya zata su uku suka tafi siyo ruwan da Ibrahim da Zayyana. Awwab ya koma wurin da Radhiya take zaune Ghazalatu za ta bishi Fauziyya ta sako mata zancen bikin da shirye shiryen da zasu yi. Tayi haka ne don tafi son yayansu da Radhiya su fara soyayya taji dadi fesawa Mami. Bata san su ma burinsu ba kenan ga kuma rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu.
Kin yi mata magana yayi ita kuwa ta ga lagonsa ta biyo shi ta zauna a kusa dashi a kan katuwar jijiyar bishiyar da ta fito.
"Ko ba komai na rama"
"A'a kin dai yi kazanta kinji dadi. Me nayi miki ma da zaki rama?"
Tura baki tayi cikin shagwabar da ta koyi yi masa "Cewa kayi fa bazanyi soja ba"
Sai da ya fuskanceta sosai yace "haka kawai kamar courses sun kare a universities ki rasa abin zaba sai soja."
"To, to ni ba so nake na gaji su Daddy ba. Kuma Babana ma ai 'Yar soja yake ce min"
" 'Yar soja da Soja daya ne a garinku. Ki cire wannan tunanin a ranki da kaina zan zabar miki course. Kin ci SSCE din dai ko"
Kumbura baki tayi cikin fushi "naci"
"Bayan bikina gida na zaki koma sai kiyi karatun a Abuja. Gara ku fara shiri da Ghazalatu tun yanzu kada na fita watarana ku tayar min da gida"
"Ha'ann lallai ma Hamma ni bazan yi auren ba har sai kayi na dawo gidanka?" Ya ma za'ayi yace haka. To zaman me zata yi musu idan ba housegirl din da Ghazalatu ta kirata ba.
"Ashe aure kike so, gara da kika fada min"
Hannu tasa ta rufe fuska wai ita kunya "kai Hamma to ai kaine wai na koma gidanka nayi karatu...shi kuma abin sai yaushe?"
"You must be kidding"
"Me kenan ka ke nufi?"
Dariyar da baiyi niya ba ce ta biyo bayan tambayar ta ta. Yarinya 'yar shekara goma sha tara ke zancen aure. Karatu yake da burin tayi mai zurfi kafin maganar aure. Da kyar ya daidaita kansa bayan ya hango irin kallon da Ghazalatu take jefo masa.
"Okay, seriously kina da wanda yake sonki ne?"
Sama ta kalla kamar me tunani "akwai Kawu Zakari sai na koma gida zai gabatar da kansa sosai"
Ransa yaji ya soma baci to amma yanayin maganarta ke bashi dariya "zai gabatar da kansa wurin su Ummi?"
Innocently tace "a wurina dai, ai bai riga yace min I love you din ba"
"Ya Allah" Awwab yace dariya na sake kama shi sosai.
"Don na fada da turanci kake dariya?" Ita bata ga me tayi ba daidai ba. Wato shi yayi aure ita kuma ya hanata cikar burinta na zama soja sannan bazai barta tayi auren ba ita ma sai kace wata alhudahuda zai rinka kira mata karatu.
Sai da yayi dariya mai isarsa ya fadi abinda yaje mata a bazata "Allah Ka bani Alheran Radhiya" yana kallon kwayar idonta.
Kusa da Zayyana ta zauna a tsakiya tana ta zuba surutu. Awwab ya kasa hakuri ya gyara madubin motar yadda zai rinka ganinta da kyau. Yana saita madubin suna hada ido da Emzee. Hade girar sama da kasa yayi da Emzee ya dago masa hannu yana murmushin tsokana. Kansa ya janye gefe Awwab ya hango Radhiya tana nunawa Zayyana makarantar da tayi primary.
"Ranar hutun da muka gama primary 5 muka yi dambe da Danmama a wurin bishiyar can, ko me yake yi yanzu oho"
"Damben fada kika yi dashi?" Zayyana tace da mamaki.
"Ke baki ji wulakancin da yayi min bane. Malamijo suke zagi ni kuwa na nuna musu matsayinsu."
"Zan so sake ganin Danmama, yanzu sai dai muyi gaisuwar mutumci idan an hadu"
Wani azababben kishi ne ya turnuke Awwab "duk yawan 'yan uwanki basu ishe ki ba sai kin hada da abokin fadanki? Wai shin ke namiji ce ne ma kike fada da maza?"
Ita me tace da zai rinka yi mata fada daga labari. Kallonta yayi ta madubin ta murtuke fuska "kuma idan na zama soja ....."
"Stop dreaming babu inda zaki. Idan bazaki yi karatu irin na kowa ba sai ki hakura"
A duniya ita tana da burin da ya wuce zama soja ne? Duk mai son hanata bai nemi zaman lafiya ba. Ko da kuwa Hamma Awwab din da take ji dashi ne. A take ta bata rai "ai dai Daddy yace zai nema min"
"To zamu gani" yace yana shiga kwanar da Emzee ya nuna masa.
Fauziyya tace "Hamma ka barta tayi kawai mu sami soja mace. Ni har hangota nake yi. Kasan Radhiya bata daukar raini kowa zai shiga hankalinsa"
"Idan kin haifi taki 'yar sai ki turata amma wannan dai na gama magana"
"Kai Hamma kada fa mu ganku a rana wannan kanwar taka bata iya fada ba. Sai ku kwana kuna yi"
Bai ce komai ba yayi parking a gefen gonar. Tun daga inda suke suna iya hango shanu da tumaki. Malamijo fa akwai kudi arziki ne kawai babu don bashi da zuciyar fitar da kudinsa a mora. Kowa ya fita saura Ghazalatu da Awwab a motar. Gani yayi bata da niyar fita ya koma ya zauna yana tambayarta me taki fita.
"Yayana kaki zama muyi hira, nayi maka wani abu ne?" Ta marairaice masa.
Tausayinta yaji domin daga baro Abuja zuwa Katsina, Kano da Sumaila duka tayi dominsa ne.
"Kiyi hakuri, kinga ban samu na zauna bane"
"Amma ka sami lokacin hira da kanwarka ko?" Tace cikin yanayin da ke nuna tsantsar kishi.
"Me yasa Alheran ta tsaya miki a rai ne?"
"Shakuwar taku tayi yawa Yayana, bana son abin ya koma wanda bazai mana dadi ba a gaba"
"Idan zakiyi min adalci Ghazalatu kin sani cewa duk wanda yasanni da su Mami to dole ya taba jin zancen Daddyn Alheran, Umminta da ita kanta ko da sau daya ne. Family dinsu suna da matukar daraja a idanun iyayena" tunawa yayi da zancen rasuwar Zayyan da Daddy yayi masa a daren da zai taho Kano da nanata masa ko bayan ransa ya taya shi rikon amanar iyalinsa. A daren sai da ya zubar da hawaye. Yayi zaton idan ya ga Radhiya kawai shakuwarsu ta baya zai tuna kila ya ga ma ta sauya daga sanin da yayi mata. Sai ya zamana abin ba haka yake ba. Ganin kwana daya Alheran nema take ta shige kowane bangare na jikinsa.
"Tunanin me kake yi ne?"
"Fito muje ba dadewa zamuyi ba" yace yana fita.
Dole tabi bayansa a ran ta tana jin dole ne ma suna komawa ya sanar da nasa iyayen idan ma kudin aure ko saka rana za'ayi duka ayi da wuri kafin abin yazo yafi karfinta.
Yawo su Radhiya ke yi sosai ga masu kiwon dabbobin suna ta bin bayansu ana musu karin bayani. Wurin wata saniya suka je ana tatsar nono. Mutumin da yake tare dasu yace ta haihu ne wani sa ya tunkuye dan makarakin bai shura ba.
"Ina son yin tatsar nima" Zayyana tace da Radhiya wadda lokaci lokaci sai ta waiga baya ta gani ko su Awwab sun fito. Haushi ne ma ya kamata saboda yace bazata yi soja ba a gaban mutane ta yi gaba cikin takaici tana jin zuciyarta tana nauyi.
"Muje na koya miki" Emzee yace da Zayyana bayan ya gama karantar yayarsa.
Irin hular kaba da suke sawa su kare rana mai fadin kasa Radhiya ta gani wani cikinsu ya cire ta dauka ta kwama a kanta ta sami kasan bishiya ta zauna akan wani dutse tana kallon su Fauziyya harda Ibrahim kowa tatsar nono yake yi. Idan wannan ya gwada sai ya matsa wani yayi.
Awwab da Ghazalatu ta gani suna tahowa taji wani abu na taso mata daga kirji har wuya. Rufe idanu tayi ta ja hular ta dora akan fuskarta. Duk abinda take yi Awwab na kallonta har ya karaso inda take. So take ta bude fuskar saboda wani sihirtaccen hamami da yake tashi a ciki amma bata san ta ina Awwab ko Gayanatunsa zasu bullo mata ba. Babu wanda take son gani cikinsu. Wari ne ya isheta ba arziki ta cire hular tayi jifa da ita sai a cinyar Awwab da zamansa kenan.
"Wai Allah, wannan shi ake kira gumama inji takari. Wannan uban wari....."
Kasa karasawa tayi tana kallonsa da hular a cinyarsa tsabar mugunta ta rinka dariya. Shi da budurwarsa suka janyo mata saka hular ai.
"Kina da matsala, kin gama bata rai kin zo kina dariya" yace yana kara rungume hular
"Na ga ka kama hula ka rungume ne kamar ta ka"
Miko mata yayi ta goce da sauri kada ta sake tabawa "nagode, ungo abinki tunda taki ce"
"Warin maza take wallahi" ta kwashe da dariya da ta ga ya tashi da sauri hular ta fadi kasa.
Yamutsa fuska yayi yana kallon yadda take jindadi hankali kwance "wannan wace irin kalma ce haka ko dadin ji babu?"
Idanunta da ya yarda suna dauke masa hankali ta watsa masa "wace kalmar? au wai warin maza. Kada kace min baka ji ba. Dauko ka sansana"
Dukawa tayi zata dauko yasa kafa yayi ball da hular yana kada kai yana kai hannuwansa wurin hancinsa ya kawar da kansa da sauri "dirty girl wannan kika dora a fuskarki"
"Rashin sani, nasan yanzu fuskata wari take yi ko"
"Ban sani ba" yace yana yin gaba. Daya daga cikin mutanen ya tambaya ina zai sami ruwa yace sai dai a rijiyar da suke debowa dabbobin. Ina wani bambanci da hular da ruwan da ya tabbatar shima bashi da tsafta. Emzee ya kira ya fada masa ruwa yake so da sabulu.
Kallon rashin fahimta yayi masa "wanka zaka yi a nan?"
Awwab ji yayi kamar ya hada shi da Radhiya ya musu duka. Ghazalatu da sauran duka kallonsa suke yi.
"Abu na taba zan wanke hannuna shikenan!"
Kamar yadda ya zata su uku suka tafi siyo ruwan da Ibrahim da Zayyana. Awwab ya koma wurin da Radhiya take zaune Ghazalatu za ta bishi Fauziyya ta sako mata zancen bikin da shirye shiryen da zasu yi. Tayi haka ne don tafi son yayansu da Radhiya su fara soyayya taji dadi fesawa Mami. Bata san su ma burinsu ba kenan ga kuma rashin sanin tsakaninsa da Ghazalatu.
Kin yi mata magana yayi ita kuwa ta ga lagonsa ta biyo shi ta zauna a kusa dashi a kan katuwar jijiyar bishiyar da ta fito.
"Ko ba komai na rama"
"A'a kin dai yi kazanta kinji dadi. Me nayi miki ma da zaki rama?"
Tura baki tayi cikin shagwabar da ta koyi yi masa "Cewa kayi fa bazanyi soja ba"
Sai da ya fuskanceta sosai yace "haka kawai kamar courses sun kare a universities ki rasa abin zaba sai soja."
"To, to ni ba so nake na gaji su Daddy ba. Kuma Babana ma ai 'Yar soja yake ce min"
" 'Yar soja da Soja daya ne a garinku. Ki cire wannan tunanin a ranki da kaina zan zabar miki course. Kin ci SSCE din dai ko"
Kumbura baki tayi cikin fushi "naci"
"Bayan bikina gida na zaki koma sai kiyi karatun a Abuja. Gara ku fara shiri da Ghazalatu tun yanzu kada na fita watarana ku tayar min da gida"
"Ha'ann lallai ma Hamma ni bazan yi auren ba har sai kayi na dawo gidanka?" Ya ma za'ayi yace haka. To zaman me zata yi musu idan ba housegirl din da Ghazalatu ta kirata ba.
"Ashe aure kike so, gara da kika fada min"
Hannu tasa ta rufe fuska wai ita kunya "kai Hamma to ai kaine wai na koma gidanka nayi karatu...shi kuma abin sai yaushe?"
"You must be kidding"
"Me kenan ka ke nufi?"
Dariyar da baiyi niya ba ce ta biyo bayan tambayar ta ta. Yarinya 'yar shekara goma sha tara ke zancen aure. Karatu yake da burin tayi mai zurfi kafin maganar aure. Da kyar ya daidaita kansa bayan ya hango irin kallon da Ghazalatu take jefo masa.
"Okay, seriously kina da wanda yake sonki ne?"
Sama ta kalla kamar me tunani "akwai Kawu Zakari sai na koma gida zai gabatar da kansa sosai"
Ransa yaji ya soma baci to amma yanayin maganarta ke bashi dariya "zai gabatar da kansa wurin su Ummi?"
Innocently tace "a wurina dai, ai bai riga yace min I love you din ba"
"Ya Allah" Awwab yace dariya na sake kama shi sosai.
"Don na fada da turanci kake dariya?" Ita bata ga me tayi ba daidai ba. Wato shi yayi aure ita kuma ya hanata cikar burinta na zama soja sannan bazai barta tayi auren ba ita ma sai kace wata alhudahuda zai rinka kira mata karatu.
Sai da yayi dariya mai isarsa ya fadi abinda yaje mata a bazata "Allah Ka bani Alheran Radhiya" yana kallon kwayar idonta.