Sashe 129
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mami na jinsu hankalinta ya tashi ta soma kwalawa Awwab kira ta ma manta suna Katsina ne Radhiya na Abuja. Tare da Daddy su ka shigo daga waje ta fada musu me taji Radhiya na fada. Sosai hankalin Awwab yayi matukar tashi ya kasa zaune ya kasa tsaye. Ummi aka sake kira tace musu zazzabi ne da ciwon kai amma ta bata magani. Idan bata ji sauki ba zuwa wayewar gari sai suje asibiti.
Zayyan a dakin Radhiya ya zauna har wurin dayan dare bayan ya lallabata taci abinci da kyar. Maganar Ghazalatu keyi mata yawo a ka wai tasan Awwab kamar tafin hannunta kuma a gabansa amma bata ji yace komai ba. Ita bata taba sanin kishi ba sai akansa. Irin son da take masa ya saka mata wani irin kishi da take jin yafi karfinta. Idan yace zai auri kanwarsa ba hanawa zata yi ba amma ita ta yarda dari bisa dari da kazantar da baka gani ba tsaftace. Duk abinda zasuyi ayi a bayan idonta ba sai an nuna mata anayi ba. To itama Ghazalatun amsar da Radhiya ta bata tana nan tana ci mata rai.
A daddafe Awwab ya kai asuba kafin takwas yayi wanka ya shiga cikin gidan saboda kofar dakinsa ta waje take. Yayi sa'ar ganin Zahra ta fito da Femi ya fada mata Abuja zai tafi ta fadawa su Mami idan sun tashi.
Muryar Mami yaji tana tambayar shi jikin Radhiya ne yayi zafi ya juya yana sunne kai. Murmushi tayi "bazan hanaka zuwa duba matarka ba kuma hakan da kayi zai farantawa Umminku sosai"
Dakatar dashi tayi tace ya jira ta fadawa Daddy. Sai da yayi wanka ya fito shima dadi yaji da Awwab din yayi tunanin komawa saboda Radhiya.
"Akwai sauran kayan da Fauziyya za ta kawo ka fito min da akwatunan sai su jera anjima a kai gidan Alh Baba" Mami tace masa.
Kayan lefe ne kusan komai ya hado abinsa da zai dawo amma Mami sai da ta bada kudi aka karo mata atampa, leshi da shadda daga kantin kwari a Kano. Shine take so ya fito da akwatunan da ya siyo sai a jera da sauran kayan a kaiwa kakanni su gani. Sai ranar dauko amarya zasu tafi da kayan Sakkwato. Hana shi tafiya Mami tayi sai da Fauziyya tazo wurin tara da rabi wai idan bai gani yanzu ba babu lallai ya gani. Shi dai kamar yace ba gidansa za'a dawo da su ba yayi shiru dai.
Kaya sunyi kyau komai goma goma Mami ta kara sai da ta tashi ya janyo Zahra gefe saboda ta fi Fauziyya nutsuwa. Kitchen suka koma saboda Fauziyya da ta damu sai anyi da ita. Rasa yadda zaiyi da rigimar Radhiya yasa shi neman shawarar kanwarsa.
Baiyi mamaki ba da Fauziyya ta shigo kamar an korota kafin Zahra tayi magana ita ta soma "wallahi Hamma baka kyauta ba. Baiwar Allah kila ma abinda ya haddasa mata zazzabin kenan" tace cike da jimami.
"Yanzu waye ya sa dake?" Zahra ta harareta "kaga Hamma sai kayi a hankali don naga take taken Ghazalatu. Ita kuma Radhiya kaje ka bata hakuri kafin tayi maka balotelli"
Dariya yayi yana tuna kan Radhiya na da sai kuma ya tuno laushi da tsahon gashinta yanzu yayi murmushi.
Fita daga kitchen din Fauziyya take yi jin ance balotelli tace "ba wani balotelli fa indai za'a shanye janbaki tuni zasu daidaita"
Ba don rannan ya matsa Radhiya akan dalilin sake kwalliya ana kiran sallah ba da bazai san me Fauziyya take nufi ba. Baki ya rike ita kuwa hankali ya tashi da ta fuskanci ya gane me take nufi ta dora hannu a ka tana salati. Zahra ta rinka kyakyata dariya Awwab ya fice yana cewa irinsu ne masu zuwa gulma gidan amarya.
"Idan na ga kafarki a kofar gidana nan da wata uku ma sai na karyata don nasan me ya kawoki"
Ta daure fuska "ai dai gaskiya na fada"
Bakin mota suka raka shi batare da ya sake neman wayar Radhiya ba ya dauki hanya. Karfe uku yana cikin garin Abuja saboda ko mai bai tsaya sha ba yayi full tank a Katsina. Gidansu ya fara zuwa amma wurin Mama ya shiga. Bata nan sai Baba Hadir shi kadai wai Ummi tazo sun koma can gidan tare. Abinci suka ci tare da sallah sannan ya je yayi wanka ya tafi ganin Radhiya. Kananan kaya ya saka bakin jeans da bakar shirt mai maballai da collar ya dora rigar sanyi mai v-neck cream ta saman wuyan ya lankwasa kwalar shirt din ciki. Ba karamin kyau yayi ba yana ta kamshi ya shige mota.
Yana shiga ya tarar da motar Ibrahim dama Baba Hadir ya fada masa can suka tafi duba Radhiya. Ummi da Mama sunyi mamakin ganinsa sosai ya sunkuyar da kai da Mama ta shiga tsokanarsa wai amarya tayi kira.
Murmushi kawai yake yi Ummi ta tura mai aikinsu kiran Radhiya tasa Rahima kawo masa abinci. Bata yarda ba da yace a koshe yake sai da ya tabbatar musu a gidan Mama yaci.
Mai aikin ce ta dawo tace wai bacci Radhiya take yi. Ba dai haka yaso ba kuma fuskarsa ta nuna. Mama ta nuna masa dakin da take ciki a kasa inda suke gyaran jiki. Yau ba'ayi ba amma saboda rashin kwarin jiki can ta shiga bayan an matsa mata ta sauko dazu.
"Shiga tana ciki ka samu ka tursasata cin abinci me yiwuwa kai taji maganarka"
Ummi ta kalla ganin ko motsi baiyi ba "muje sama mu karasa don naga alama dan naki ba tashi zaiyi ba"
Awwab kunya Ummi kunya. Sai da su ka shige sannan ya tashi da sauri ya tafi dakin da aka nuna masa. Kwankwasawa yayi tana kwance da waya a hannu r muryar Hammanta amma kishi ya hanata kunna waya ta kira.
Tura kofar yayi a hankali yaji tace "Rahima karo min bargo a sama dakin nan akwai sanyi sosai"
"Gani ki yafa"
Muryarsa ce tazo mata a bazata ta dago kai ta tabbatar shi din ne yana tsaye da ga bakin kofa sai kawai ta ja bargo ta rufe har kanta. Murmushi Awwab yayi ya zauna a gefen gado sannan a hankali ya zura hannunsa ciki ya kamo nata tana ta kokarin kwacewa ya rike.
"Idan baki nutsu ba zanyi miki rawar 'yar amana"
Dena motsin tayi yana jiyo sautin dariyarta a hankali yayin da take jin dumin hannunsa yana ratsa ta. Shiru su ka yi duka su biyun na dan lokaci sai daga baya ya soma magana. Hakuri ya bata tare da bayanin ya akayi ma taji shi tare da Ghazalatu a lokacin.
"Ko kinfi so ace mun dena zumunci da 'yan uwana?" Tana cikin bargon ta girgiza kai yace yana dariya "ashe ma zakiyi saurin hakura duk kika tayar min da hankali"
Gefen fuskarta kadan ta bude amma bata iya kallon idanunsa ba tace "ba hakura nayi ba ka tashi kayi min rawar"
"Sai dai muyi tare" yace yana kashe mata ido.
Sake rufa tayi ya kwanto a jikinta tuni ta fara rawar jiki kuwa "ko ki bude in ganki tunda dubiya nazo ko na shigo ta nan" yace yana dan matsa hannunta da ya rike ta kasan bargon. Ja taji yayi ta bude kanta da sauri.
A kunyace ta ture bargon tana sanye da dogon skirt baki sai rigar sanyi da ta kamata mai high neck.
"Give me a hug" yace yana ware hannuwansa. Bata motsa ba sai kai da ta sunkuyar yace "now please" da wata irin murya. Ji yake kamar ya janyo kwanakin nan su kare da wuri ace an gama biki kowa ya huta.
Ba yadda ta iya ta dan matso kadan shi kuwa ya janyota jikinsa ya rungume yana shafa kanta.
"I love you Schatzi ki dena kokwonto akan hakan. Bazan taba yin abu don na bata miki rai ina sane ba"
Dama can bata gama kukanta ba sai yanzu ta sami damar yi masa yana ta rarrashi.
"Ni dai ko za ka yi min kishiya bazan zauna gida daya da ita ba"
Kanta ya dago yana murmushi "saboda me?"
Shagwabe masa tayi "Ni dai kawai bana so"
Goshinta ya yiwa kiss ta runtse idanu yace "saboda kina tunanin zanyi mata wannan?" Ya koma kumatunta hagu da dama "da wannan?" Sai kan hancinta "da wannan ma?"
"Ni dai ban ce ba"
"Ni nace baby...I miss you so much" yace yana kallon fuskarta idonta a rufe ya soma zana mata lips da karamin yatsansa "yau baki sa janbaki bane?"
Tamkar ta nutse a cikin gadon ta kawar da fuskarta "bani da lafiya fa"
Idanunsa a kanta yace "Ni kuma na taho all the way from Katsina shan janbaki ne fa"
Ciwo dama ya riga ya warke tunda ya iso da sauri ta tashi yana kiranta wai ko vaseline ne ta shafa ta bashi ya shanye ta gudu tana dariya. Bata sake bari sun kebe su kadai ba sai da zai tafi gida tayi masa sallama yana ta korafin bai sha janbaki ba tana dariya. Kafin dare ta ware tas sai karadi da dariyarta da ta cika mutane dashi. Zayyan yana ganin chanjin da ta samu kuma an fada masa Awwab yazo yayi dariya wai dama can ciwon soyayya ne.
"To saura ka fada a gabansu" Ummi tace fuska a daure don kada ya saka ta dariya.
Alamun zip ya yiwa bakinsa sannan ya tashi yana nade hannun rigar baccinsa "bari na gani ko ina da sauran karfi"
Mairama bata ankara ba ya dagata ya dire akan gado. Tana tashi ya danneta yana dariya "kwanta bitar karatunmu zamuyi muma"
**********
Yau litinin ya sati na gaba ya kamata a fara biki gidan gabadaya suka tafi Sumaila tare da Mama, Zayyan kuma ya tafi Sakkwato. Sun isa gidan na Malamijo ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Su Innawuro daga rugar Barkindo, Nene Marka da kishiyarta tare da 'ya'yab kishiyar da jikoki sai kuma 'yan uwan Malamijo da nasu iyalan. Ranar laraba zasu yi Kamu saboda da yawansu ba iya zuwa Abuja zasu yi ba. Emzee yana makaranta har lokacin sai wani satin zai taho. Sunyi waya da Rahima ta fada masa sun taho Sumaila sai dai har yau bai kawo komai ba. Sallah kawai Rahiman tayi ta fadawa Ummi zata je gida.
Zayyan a dakin Radhiya ya zauna har wurin dayan dare bayan ya lallabata taci abinci da kyar. Maganar Ghazalatu keyi mata yawo a ka wai tasan Awwab kamar tafin hannunta kuma a gabansa amma bata ji yace komai ba. Ita bata taba sanin kishi ba sai akansa. Irin son da take masa ya saka mata wani irin kishi da take jin yafi karfinta. Idan yace zai auri kanwarsa ba hanawa zata yi ba amma ita ta yarda dari bisa dari da kazantar da baka gani ba tsaftace. Duk abinda zasuyi ayi a bayan idonta ba sai an nuna mata anayi ba. To itama Ghazalatun amsar da Radhiya ta bata tana nan tana ci mata rai.
A daddafe Awwab ya kai asuba kafin takwas yayi wanka ya shiga cikin gidan saboda kofar dakinsa ta waje take. Yayi sa'ar ganin Zahra ta fito da Femi ya fada mata Abuja zai tafi ta fadawa su Mami idan sun tashi.
Muryar Mami yaji tana tambayar shi jikin Radhiya ne yayi zafi ya juya yana sunne kai. Murmushi tayi "bazan hanaka zuwa duba matarka ba kuma hakan da kayi zai farantawa Umminku sosai"
Dakatar dashi tayi tace ya jira ta fadawa Daddy. Sai da yayi wanka ya fito shima dadi yaji da Awwab din yayi tunanin komawa saboda Radhiya.
"Akwai sauran kayan da Fauziyya za ta kawo ka fito min da akwatunan sai su jera anjima a kai gidan Alh Baba" Mami tace masa.
Kayan lefe ne kusan komai ya hado abinsa da zai dawo amma Mami sai da ta bada kudi aka karo mata atampa, leshi da shadda daga kantin kwari a Kano. Shine take so ya fito da akwatunan da ya siyo sai a jera da sauran kayan a kaiwa kakanni su gani. Sai ranar dauko amarya zasu tafi da kayan Sakkwato. Hana shi tafiya Mami tayi sai da Fauziyya tazo wurin tara da rabi wai idan bai gani yanzu ba babu lallai ya gani. Shi dai kamar yace ba gidansa za'a dawo da su ba yayi shiru dai.
Kaya sunyi kyau komai goma goma Mami ta kara sai da ta tashi ya janyo Zahra gefe saboda ta fi Fauziyya nutsuwa. Kitchen suka koma saboda Fauziyya da ta damu sai anyi da ita. Rasa yadda zaiyi da rigimar Radhiya yasa shi neman shawarar kanwarsa.
Baiyi mamaki ba da Fauziyya ta shigo kamar an korota kafin Zahra tayi magana ita ta soma "wallahi Hamma baka kyauta ba. Baiwar Allah kila ma abinda ya haddasa mata zazzabin kenan" tace cike da jimami.
"Yanzu waye ya sa dake?" Zahra ta harareta "kaga Hamma sai kayi a hankali don naga take taken Ghazalatu. Ita kuma Radhiya kaje ka bata hakuri kafin tayi maka balotelli"
Dariya yayi yana tuna kan Radhiya na da sai kuma ya tuno laushi da tsahon gashinta yanzu yayi murmushi.
Fita daga kitchen din Fauziyya take yi jin ance balotelli tace "ba wani balotelli fa indai za'a shanye janbaki tuni zasu daidaita"
Ba don rannan ya matsa Radhiya akan dalilin sake kwalliya ana kiran sallah ba da bazai san me Fauziyya take nufi ba. Baki ya rike ita kuwa hankali ya tashi da ta fuskanci ya gane me take nufi ta dora hannu a ka tana salati. Zahra ta rinka kyakyata dariya Awwab ya fice yana cewa irinsu ne masu zuwa gulma gidan amarya.
"Idan na ga kafarki a kofar gidana nan da wata uku ma sai na karyata don nasan me ya kawoki"
Ta daure fuska "ai dai gaskiya na fada"
Bakin mota suka raka shi batare da ya sake neman wayar Radhiya ba ya dauki hanya. Karfe uku yana cikin garin Abuja saboda ko mai bai tsaya sha ba yayi full tank a Katsina. Gidansu ya fara zuwa amma wurin Mama ya shiga. Bata nan sai Baba Hadir shi kadai wai Ummi tazo sun koma can gidan tare. Abinci suka ci tare da sallah sannan ya je yayi wanka ya tafi ganin Radhiya. Kananan kaya ya saka bakin jeans da bakar shirt mai maballai da collar ya dora rigar sanyi mai v-neck cream ta saman wuyan ya lankwasa kwalar shirt din ciki. Ba karamin kyau yayi ba yana ta kamshi ya shige mota.
Yana shiga ya tarar da motar Ibrahim dama Baba Hadir ya fada masa can suka tafi duba Radhiya. Ummi da Mama sunyi mamakin ganinsa sosai ya sunkuyar da kai da Mama ta shiga tsokanarsa wai amarya tayi kira.
Murmushi kawai yake yi Ummi ta tura mai aikinsu kiran Radhiya tasa Rahima kawo masa abinci. Bata yarda ba da yace a koshe yake sai da ya tabbatar musu a gidan Mama yaci.
Mai aikin ce ta dawo tace wai bacci Radhiya take yi. Ba dai haka yaso ba kuma fuskarsa ta nuna. Mama ta nuna masa dakin da take ciki a kasa inda suke gyaran jiki. Yau ba'ayi ba amma saboda rashin kwarin jiki can ta shiga bayan an matsa mata ta sauko dazu.
"Shiga tana ciki ka samu ka tursasata cin abinci me yiwuwa kai taji maganarka"
Ummi ta kalla ganin ko motsi baiyi ba "muje sama mu karasa don naga alama dan naki ba tashi zaiyi ba"
Awwab kunya Ummi kunya. Sai da su ka shige sannan ya tashi da sauri ya tafi dakin da aka nuna masa. Kwankwasawa yayi tana kwance da waya a hannu r muryar Hammanta amma kishi ya hanata kunna waya ta kira.
Tura kofar yayi a hankali yaji tace "Rahima karo min bargo a sama dakin nan akwai sanyi sosai"
"Gani ki yafa"
Muryarsa ce tazo mata a bazata ta dago kai ta tabbatar shi din ne yana tsaye da ga bakin kofa sai kawai ta ja bargo ta rufe har kanta. Murmushi Awwab yayi ya zauna a gefen gado sannan a hankali ya zura hannunsa ciki ya kamo nata tana ta kokarin kwacewa ya rike.
"Idan baki nutsu ba zanyi miki rawar 'yar amana"
Dena motsin tayi yana jiyo sautin dariyarta a hankali yayin da take jin dumin hannunsa yana ratsa ta. Shiru su ka yi duka su biyun na dan lokaci sai daga baya ya soma magana. Hakuri ya bata tare da bayanin ya akayi ma taji shi tare da Ghazalatu a lokacin.
"Ko kinfi so ace mun dena zumunci da 'yan uwana?" Tana cikin bargon ta girgiza kai yace yana dariya "ashe ma zakiyi saurin hakura duk kika tayar min da hankali"
Gefen fuskarta kadan ta bude amma bata iya kallon idanunsa ba tace "ba hakura nayi ba ka tashi kayi min rawar"
"Sai dai muyi tare" yace yana kashe mata ido.
Sake rufa tayi ya kwanto a jikinta tuni ta fara rawar jiki kuwa "ko ki bude in ganki tunda dubiya nazo ko na shigo ta nan" yace yana dan matsa hannunta da ya rike ta kasan bargon. Ja taji yayi ta bude kanta da sauri.
A kunyace ta ture bargon tana sanye da dogon skirt baki sai rigar sanyi da ta kamata mai high neck.
"Give me a hug" yace yana ware hannuwansa. Bata motsa ba sai kai da ta sunkuyar yace "now please" da wata irin murya. Ji yake kamar ya janyo kwanakin nan su kare da wuri ace an gama biki kowa ya huta.
Ba yadda ta iya ta dan matso kadan shi kuwa ya janyota jikinsa ya rungume yana shafa kanta.
"I love you Schatzi ki dena kokwonto akan hakan. Bazan taba yin abu don na bata miki rai ina sane ba"
Dama can bata gama kukanta ba sai yanzu ta sami damar yi masa yana ta rarrashi.
"Ni dai ko za ka yi min kishiya bazan zauna gida daya da ita ba"
Kanta ya dago yana murmushi "saboda me?"
Shagwabe masa tayi "Ni dai kawai bana so"
Goshinta ya yiwa kiss ta runtse idanu yace "saboda kina tunanin zanyi mata wannan?" Ya koma kumatunta hagu da dama "da wannan?" Sai kan hancinta "da wannan ma?"
"Ni dai ban ce ba"
"Ni nace baby...I miss you so much" yace yana kallon fuskarta idonta a rufe ya soma zana mata lips da karamin yatsansa "yau baki sa janbaki bane?"
Tamkar ta nutse a cikin gadon ta kawar da fuskarta "bani da lafiya fa"
Idanunsa a kanta yace "Ni kuma na taho all the way from Katsina shan janbaki ne fa"
Ciwo dama ya riga ya warke tunda ya iso da sauri ta tashi yana kiranta wai ko vaseline ne ta shafa ta bashi ya shanye ta gudu tana dariya. Bata sake bari sun kebe su kadai ba sai da zai tafi gida tayi masa sallama yana ta korafin bai sha janbaki ba tana dariya. Kafin dare ta ware tas sai karadi da dariyarta da ta cika mutane dashi. Zayyan yana ganin chanjin da ta samu kuma an fada masa Awwab yazo yayi dariya wai dama can ciwon soyayya ne.
"To saura ka fada a gabansu" Ummi tace fuska a daure don kada ya saka ta dariya.
Alamun zip ya yiwa bakinsa sannan ya tashi yana nade hannun rigar baccinsa "bari na gani ko ina da sauran karfi"
Mairama bata ankara ba ya dagata ya dire akan gado. Tana tashi ya danneta yana dariya "kwanta bitar karatunmu zamuyi muma"
**********
Yau litinin ya sati na gaba ya kamata a fara biki gidan gabadaya suka tafi Sumaila tare da Mama, Zayyan kuma ya tafi Sakkwato. Sun isa gidan na Malamijo ya cika da 'yan uwa da abokan arziki. Su Innawuro daga rugar Barkindo, Nene Marka da kishiyarta tare da 'ya'yab kishiyar da jikoki sai kuma 'yan uwan Malamijo da nasu iyalan. Ranar laraba zasu yi Kamu saboda da yawansu ba iya zuwa Abuja zasu yi ba. Emzee yana makaranta har lokacin sai wani satin zai taho. Sunyi waya da Rahima ta fada masa sun taho Sumaila sai dai har yau bai kawo komai ba. Sallah kawai Rahiman tayi ta fadawa Ummi zata je gida.