Sashe 108
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lekowa tayi ta amsa sallamarsu sannan tace tana zuwa. Kwashe abincin ta yi ta fito tana sanar dasu yanzu Mami da Fauziyya suka tafi asibiti. Jikin Fauziyya babu dadi tayi ta amai tun safe ko tashi bata iyawa.
Da dukkan gaskiyarsa Ibrahim yace "Wane irin ciwo ne yake damunta haka kullum sai ace bata da lafiya" don duk laulayin da ake cewa tana yi yayi zaton ana nufin ita mutum ce mai yawan rashin lafiya.
Zayyana sai ta sake biris dashi ta tambayi Emzee ko zai ci abinci yace ya koshi labari yazo ji. Shagwabe fuska tayi Ibrahim yaji wani azababben bacin rai da bai san dalilinsa ko daga ina yake ba ya dirar masa a zuciya. A gaban Emzee take wannan kwabe fuskar...to me take so yayi mata? Maganarta ya tsinkayo tana cewa
"Hibbah ta takura min Ya Emzee wai zata fadawa Alhajinsu ya hadamu a kaimu Dubai karatu. Ita bata ma gama ba amma take nacin kada na karbi admission din Baze. Yanzu idan taje ta fada akayiwa Daddy magana fada zaiyi min nasan" ta kare maganar muryarta na rauni.
"Ki fada mata ba kya so kawai na kula tana da rawar kai." Emzee yace bayan gajeren tunani.
"Na fada fa har kusan fada muka yi taki yarda. Jiya da mukayi magana da Ya Halifa..."
A fusace Ibrahim ya harareta bai ma san yana daga murya ba yace "Halifa kuma? Me ya hadaki waya da Halifa?"
Idanunta ne suka yi kwal-kwal za tayi kuka ta kara narkewa za ta kai kararsa wurin Emzee.
"Ya Emzee ka ...."
"Emzee pls bamu wuri yarinyar nan is trying my patience" Ibrahim yace yana hade girar sama da kasa.
"Anzo wurin" Emzee yace da shakiyanci ya dauki Jawad yayi waje abinsa.
Tsilli Zayyana tayi da idanu a tsorace saboda babu alamun wasa ko kadan a fuskar Ibrahim.
"Zayyana" ya kira sunanta rai a bace. Wai har waya take da Halifa shi yana zaune hoto.
A hankali ta dago idanunta suka sauka acikin nasa. Nasa sun kankance da kishi ita kuma nata sai girma da suka kara cike da hawaye. Fuskarta so cute bakin nan ta gama shirin kyabe masa shi da yayi mata magana mara dadi ta saki kuka. Kamar wanda aka sokawa kibiya haka idanun Zayyana da fuskarta suka shiga zuciyar Ibrahim. Abin da bai yarda shi yake ji ba game da ita ya yunkuro masa gabaki daya. Fadan da ya so yi mata ya makale a makoshi sai samun kansa yayi da narke fuska irin nata.
"You look beautiful" yace da taushin murya idanunsa a kanta.
Tsigar jikinta ce taji ta tashi ba shiri ta tashi a guje za ta bar falon ya sake cewa.
"Zayyana me yasa kika dena yi min magana?"
"Ba kaine ba" tace fuskar nan a shagwabe.
Da sauri yace "Na dena"
"Me din?"
"Ko ma meye please kada ki sake yi min irin haka"
Murmushi tayi da ya sake tafiya da sauran kuzarin Ibrahim ta shige daki ta barshi yana ta sakin murmushi shi kadai. Da dan gudu ya koma gida ya sami Mama da Emzee suna hira. Wani tsalle ya daka ya mikawa Emzee hannu suka tafa.
"An kashe boss kenan" Emzee yace yana dariya.
Kafadarsa Ibrahim ya daka yana nuna masa Mama. Girgiza kai tayi abinta tana murmushi tasan ko ma meye da kansa zai dawo ya fada mata don baya iya boye mata komai. Ba don kada tayi azarbabi ba ma sai tace yayi mata kama da sabon shigar soyayya.
Da kyar Ibrahim ya nutsu suka yi maganar daraktan da ya dace su nema. An sha buge bugen waya da abokan Ibrahim na Kano kafin Allah Yasa suka sami nambar wani Nafi'u Bigman. Shi Bigman ba'a ma gama sanin sunansa cikin daraktocin ba amma akwai kokari da himma duk da bako ne a harkar. Rashin suna da yayi yasa bashi da ayyuka a gabansa har ya amsa gayyatar gaggawa da aka tura masa. Bai yarda aikin gaske bane sai da Zayyan yayi magana dashi yaji muryar babba. Emzee yayi masa sauran bayani aka bukaci ya tafi Kwara jibi sannan aka bashi nambar wayar Radhiya. Karamin aiki ne ya koma babba domin tana gama yi masa bayani yaji gabadaya ta kwadaita masa son aikin. Email dinsa ya tura musu a take Arifah ta tura masa sauran bayani da kuma tsarin kalmomin tambaya na hira da Radhiya zata rinka yi musu. Kusan kwana yayi yana bincike mai zurfi akan harkar rayuwar sojoji da irin matsalolin da suke fuskanta na yau da gobe.
Gari na wayewa ya nemi Assistant dinsa suka tafi Kwara. Shi da ba kowan kowa ba sai gashi a gidan gwamnati ana karrama shi. Takarkar contarct wadda Ibrahim ya tsara aka tura musu suka yi printing a take Bigman yasa hannu Radhiya ma ta saka sai Arifah da Assistant dinsa a matsayin shaidu. Gyare gyare suka kawowa aikin ta fannin yanayin presentation da dialogue (maganar da zasu rinka yi idan camera na kansu). Karin bayani yayi musu cewa ba shirin film bane amma ko documentaries ana tsari sosai kafin ayisu idan ba haka ba zai zama kara zube karshe a kasa isar da sako sai asarar lokaci da kudi.
Wannan abu ya yiwa Radhiya da Arifah dadi. Sun dauki lokaci a wani falo da aka basu suka gama gyara komai washegari sai wurin Maman Dolapo.
Motar da aka basu bus ce wadda camera man ya sako kayan aikinsa suka taho tare da dan gari wanda yake musu rakiya da kwatancen da aka basu. Layin da suka shiga a cabalbake yake da ruwa kamar tsakiyar kasuwa. Tambaya ya rinka yi har aka kaisu gaban wani gida mai karamar kofa da shago a jikinsa. Babbar mace ce zaune a kan benci a kofar shagon da aka zubawa provision irisu kayan shayi da lemo. Ganin mutane cikin shigar alfarma ta fito da sauri tana dariya ciniki yazo. Da pidgin English tace musu.
"Una welcome, wetin u wan buy?" (Sannunku da zuwa. Me zaku saya?)
Zuciyar Radhiya ta bata wannan ce Maman Dolapo din haka kawai sai taji kwalla ta taho mata. Shagon fa babu wani abin arziki a ciki duk kankantarsa ko rabi bai cika ba.
"Mama Dolapo?"
"Yes, yes" tace a dan tsorace don bata ganesu ba kada ace 'ya'yanta sunyi laifi ne.
Hoton da Ummi ta bata ta ciro daga jaka ta mika mata "kin gane wannan da kuka zauna a Sokoto Mairama."
Hoton ranar sunanta ne da akayi da su Ummi da yawancin matan da suke makotaka dasu. Namiji daya ne a cikinsu Awwab yana manne da Mama saboda a hannunta Radhiya take ya dora nasa hannun ya tallefota ta kasa.
A take Maman Dolapo ta saki kuka tana tuno shekaru masu yawa da suka gabata. Idanu ta zubawa Radhiya kafin cike da rashin yarda tace "kene yarinya wannan ko?" Ta nuna Mairama.
Kai Radhiya ta gyada da mamakin yadda matar tayi saurin ganeta. Ji tayi ta tattarota gabadaya ta rungume tana ihun murna. Makota kuwa da masu shaguna aka taro a kofar gidan tana kuka tana dariya tace 'yarta ce tazo daga Sokoto. Cikin gidan ta ja su ta rasa inda zata saka kanta don murna. Nan ta tura aka kira Dolapo daga garejin da yake aikin makanike da sauran yaranta.
Duka bayanin Radhiya ta gane ga kukan da taci na jin dawowar Zayyan daga prison. Canja kaya taje tayi aka hada yaran duka sannan aka fara shirin daukar kashi na farko na shirin Military Voice. Ana dora camera akan Radhiya a kofar gidan inda zata gabatar da gidan waye suka zo jikinta ya fara bari. Anyi ya kai sau biyar sai tayi kamar zata daure sai murya ta fara rawa. Arifah ta gaji ta kira Awwab.
"Matarka fa zabuwa ce ta kasa yin abinda ya kawota sai rawar jiki take yiwa mutane"
"Bani ita" Yaso ace tare suka zo Allah bai nufa ba.
"Schatzi" ya kira sunanta a hankali.
Hawaye ne ya digo mata ba shiri "Hammana"
"Mw kike tsoro hmm? Ashe baki damu da rayuwar da families din sojoji suke yi ba."
"Na damu mana"
"Then do your best my baby..go on and make soldiers proud"
Wani irin dadi da karfin gwiwa taji gami da kunya tace masa "kayi ta min addu'a har mu gama na sake kiranka"
"Alwala ma zanyi yanzu kinji. Jeki kada ki bata musu lokaci"
Rigar da ta dora akan kayanta mai karamin hannu da tambarin makarantarsu ta gefen dama a gaba kuma an rubuta AZM Tureta. Gyara tsayuwarta tayi ta gabatar da kanta da kyakkyawan murmushi.
"Alheran welcomes you to the Military Voice"
Daga nan tsarin Darakta Bigman da kalaman da Arifah ta rubuta ta rinka bi har suka shiga cikin gidan inda Mama Dolapo take zaune a tsakiyar 'ya'yanta guda shida. Ta amsa tambayoyi game da sunayensu, aikin mijinta da shekarar da ya rasu. Sai kuma irin yadda suka rayu da wahalhalun da ta jurewa domin 'ya'yanta.
"A iya zaman da kuka yi da mijinki ko zaki iya fada mana wane abu ne yafi tsaya miki a rai game da aikinsa na soja"
Kwalla Mama Dolapo ta share tana murmushi mai ciwo tana magana da pidgin dai wanda a wurin tacewa zasu rubuta abinda take fada da turanci mai kyau a kasa saboda mutane su fahimta "kinsan kowane maaikaci yana fita yaje wurin harkokinsa ya dawo gida ga iyalansa. Idan tafiya ce zai ce kwana kaza zanyi na dawo. Amma mu indai miji yace zashi aiki fieldwork to fa dake matar dashi sai kun ga juna kawai musamman wurin rikici ne. Mafiya yawan lokuta duk inda sojoji suka je kai taimako na tsaro indai wata mushkila ta taso da za'aji rauni ko rasa rai da wuya idan ba cikinsu bane. Mu muna gida muna jiran tsammani bayan ko su a junansu sun sani kila fa idan na tafi nine bazan dawo ba ko abokin aikina wane. Babban tashin hankali shine kiga wasu sun fara dawowa baki da cikakken bayani game da naki mijin. Kullum kina cikin shiri kiyi wanka kiyi girki ki gyara gida kina sa rai yau ne, gobe ne, jibi ne zai dawo gareki. Idan da rabo ya dawo idan babu kuma sai dai sakon mutuwarsa" ta karashe da wani irin matsanancin kuka.
Da dukkan gaskiyarsa Ibrahim yace "Wane irin ciwo ne yake damunta haka kullum sai ace bata da lafiya" don duk laulayin da ake cewa tana yi yayi zaton ana nufin ita mutum ce mai yawan rashin lafiya.
Zayyana sai ta sake biris dashi ta tambayi Emzee ko zai ci abinci yace ya koshi labari yazo ji. Shagwabe fuska tayi Ibrahim yaji wani azababben bacin rai da bai san dalilinsa ko daga ina yake ba ya dirar masa a zuciya. A gaban Emzee take wannan kwabe fuskar...to me take so yayi mata? Maganarta ya tsinkayo tana cewa
"Hibbah ta takura min Ya Emzee wai zata fadawa Alhajinsu ya hadamu a kaimu Dubai karatu. Ita bata ma gama ba amma take nacin kada na karbi admission din Baze. Yanzu idan taje ta fada akayiwa Daddy magana fada zaiyi min nasan" ta kare maganar muryarta na rauni.
"Ki fada mata ba kya so kawai na kula tana da rawar kai." Emzee yace bayan gajeren tunani.
"Na fada fa har kusan fada muka yi taki yarda. Jiya da mukayi magana da Ya Halifa..."
A fusace Ibrahim ya harareta bai ma san yana daga murya ba yace "Halifa kuma? Me ya hadaki waya da Halifa?"
Idanunta ne suka yi kwal-kwal za tayi kuka ta kara narkewa za ta kai kararsa wurin Emzee.
"Ya Emzee ka ...."
"Emzee pls bamu wuri yarinyar nan is trying my patience" Ibrahim yace yana hade girar sama da kasa.
"Anzo wurin" Emzee yace da shakiyanci ya dauki Jawad yayi waje abinsa.
Tsilli Zayyana tayi da idanu a tsorace saboda babu alamun wasa ko kadan a fuskar Ibrahim.
"Zayyana" ya kira sunanta rai a bace. Wai har waya take da Halifa shi yana zaune hoto.
A hankali ta dago idanunta suka sauka acikin nasa. Nasa sun kankance da kishi ita kuma nata sai girma da suka kara cike da hawaye. Fuskarta so cute bakin nan ta gama shirin kyabe masa shi da yayi mata magana mara dadi ta saki kuka. Kamar wanda aka sokawa kibiya haka idanun Zayyana da fuskarta suka shiga zuciyar Ibrahim. Abin da bai yarda shi yake ji ba game da ita ya yunkuro masa gabaki daya. Fadan da ya so yi mata ya makale a makoshi sai samun kansa yayi da narke fuska irin nata.
"You look beautiful" yace da taushin murya idanunsa a kanta.
Tsigar jikinta ce taji ta tashi ba shiri ta tashi a guje za ta bar falon ya sake cewa.
"Zayyana me yasa kika dena yi min magana?"
"Ba kaine ba" tace fuskar nan a shagwabe.
Da sauri yace "Na dena"
"Me din?"
"Ko ma meye please kada ki sake yi min irin haka"
Murmushi tayi da ya sake tafiya da sauran kuzarin Ibrahim ta shige daki ta barshi yana ta sakin murmushi shi kadai. Da dan gudu ya koma gida ya sami Mama da Emzee suna hira. Wani tsalle ya daka ya mikawa Emzee hannu suka tafa.
"An kashe boss kenan" Emzee yace yana dariya.
Kafadarsa Ibrahim ya daka yana nuna masa Mama. Girgiza kai tayi abinta tana murmushi tasan ko ma meye da kansa zai dawo ya fada mata don baya iya boye mata komai. Ba don kada tayi azarbabi ba ma sai tace yayi mata kama da sabon shigar soyayya.
Da kyar Ibrahim ya nutsu suka yi maganar daraktan da ya dace su nema. An sha buge bugen waya da abokan Ibrahim na Kano kafin Allah Yasa suka sami nambar wani Nafi'u Bigman. Shi Bigman ba'a ma gama sanin sunansa cikin daraktocin ba amma akwai kokari da himma duk da bako ne a harkar. Rashin suna da yayi yasa bashi da ayyuka a gabansa har ya amsa gayyatar gaggawa da aka tura masa. Bai yarda aikin gaske bane sai da Zayyan yayi magana dashi yaji muryar babba. Emzee yayi masa sauran bayani aka bukaci ya tafi Kwara jibi sannan aka bashi nambar wayar Radhiya. Karamin aiki ne ya koma babba domin tana gama yi masa bayani yaji gabadaya ta kwadaita masa son aikin. Email dinsa ya tura musu a take Arifah ta tura masa sauran bayani da kuma tsarin kalmomin tambaya na hira da Radhiya zata rinka yi musu. Kusan kwana yayi yana bincike mai zurfi akan harkar rayuwar sojoji da irin matsalolin da suke fuskanta na yau da gobe.
Gari na wayewa ya nemi Assistant dinsa suka tafi Kwara. Shi da ba kowan kowa ba sai gashi a gidan gwamnati ana karrama shi. Takarkar contarct wadda Ibrahim ya tsara aka tura musu suka yi printing a take Bigman yasa hannu Radhiya ma ta saka sai Arifah da Assistant dinsa a matsayin shaidu. Gyare gyare suka kawowa aikin ta fannin yanayin presentation da dialogue (maganar da zasu rinka yi idan camera na kansu). Karin bayani yayi musu cewa ba shirin film bane amma ko documentaries ana tsari sosai kafin ayisu idan ba haka ba zai zama kara zube karshe a kasa isar da sako sai asarar lokaci da kudi.
Wannan abu ya yiwa Radhiya da Arifah dadi. Sun dauki lokaci a wani falo da aka basu suka gama gyara komai washegari sai wurin Maman Dolapo.
Motar da aka basu bus ce wadda camera man ya sako kayan aikinsa suka taho tare da dan gari wanda yake musu rakiya da kwatancen da aka basu. Layin da suka shiga a cabalbake yake da ruwa kamar tsakiyar kasuwa. Tambaya ya rinka yi har aka kaisu gaban wani gida mai karamar kofa da shago a jikinsa. Babbar mace ce zaune a kan benci a kofar shagon da aka zubawa provision irisu kayan shayi da lemo. Ganin mutane cikin shigar alfarma ta fito da sauri tana dariya ciniki yazo. Da pidgin English tace musu.
"Una welcome, wetin u wan buy?" (Sannunku da zuwa. Me zaku saya?)
Zuciyar Radhiya ta bata wannan ce Maman Dolapo din haka kawai sai taji kwalla ta taho mata. Shagon fa babu wani abin arziki a ciki duk kankantarsa ko rabi bai cika ba.
"Mama Dolapo?"
"Yes, yes" tace a dan tsorace don bata ganesu ba kada ace 'ya'yanta sunyi laifi ne.
Hoton da Ummi ta bata ta ciro daga jaka ta mika mata "kin gane wannan da kuka zauna a Sokoto Mairama."
Hoton ranar sunanta ne da akayi da su Ummi da yawancin matan da suke makotaka dasu. Namiji daya ne a cikinsu Awwab yana manne da Mama saboda a hannunta Radhiya take ya dora nasa hannun ya tallefota ta kasa.
A take Maman Dolapo ta saki kuka tana tuno shekaru masu yawa da suka gabata. Idanu ta zubawa Radhiya kafin cike da rashin yarda tace "kene yarinya wannan ko?" Ta nuna Mairama.
Kai Radhiya ta gyada da mamakin yadda matar tayi saurin ganeta. Ji tayi ta tattarota gabadaya ta rungume tana ihun murna. Makota kuwa da masu shaguna aka taro a kofar gidan tana kuka tana dariya tace 'yarta ce tazo daga Sokoto. Cikin gidan ta ja su ta rasa inda zata saka kanta don murna. Nan ta tura aka kira Dolapo daga garejin da yake aikin makanike da sauran yaranta.
Duka bayanin Radhiya ta gane ga kukan da taci na jin dawowar Zayyan daga prison. Canja kaya taje tayi aka hada yaran duka sannan aka fara shirin daukar kashi na farko na shirin Military Voice. Ana dora camera akan Radhiya a kofar gidan inda zata gabatar da gidan waye suka zo jikinta ya fara bari. Anyi ya kai sau biyar sai tayi kamar zata daure sai murya ta fara rawa. Arifah ta gaji ta kira Awwab.
"Matarka fa zabuwa ce ta kasa yin abinda ya kawota sai rawar jiki take yiwa mutane"
"Bani ita" Yaso ace tare suka zo Allah bai nufa ba.
"Schatzi" ya kira sunanta a hankali.
Hawaye ne ya digo mata ba shiri "Hammana"
"Mw kike tsoro hmm? Ashe baki damu da rayuwar da families din sojoji suke yi ba."
"Na damu mana"
"Then do your best my baby..go on and make soldiers proud"
Wani irin dadi da karfin gwiwa taji gami da kunya tace masa "kayi ta min addu'a har mu gama na sake kiranka"
"Alwala ma zanyi yanzu kinji. Jeki kada ki bata musu lokaci"
Rigar da ta dora akan kayanta mai karamin hannu da tambarin makarantarsu ta gefen dama a gaba kuma an rubuta AZM Tureta. Gyara tsayuwarta tayi ta gabatar da kanta da kyakkyawan murmushi.
"Alheran welcomes you to the Military Voice"
Daga nan tsarin Darakta Bigman da kalaman da Arifah ta rubuta ta rinka bi har suka shiga cikin gidan inda Mama Dolapo take zaune a tsakiyar 'ya'yanta guda shida. Ta amsa tambayoyi game da sunayensu, aikin mijinta da shekarar da ya rasu. Sai kuma irin yadda suka rayu da wahalhalun da ta jurewa domin 'ya'yanta.
"A iya zaman da kuka yi da mijinki ko zaki iya fada mana wane abu ne yafi tsaya miki a rai game da aikinsa na soja"
Kwalla Mama Dolapo ta share tana murmushi mai ciwo tana magana da pidgin dai wanda a wurin tacewa zasu rubuta abinda take fada da turanci mai kyau a kasa saboda mutane su fahimta "kinsan kowane maaikaci yana fita yaje wurin harkokinsa ya dawo gida ga iyalansa. Idan tafiya ce zai ce kwana kaza zanyi na dawo. Amma mu indai miji yace zashi aiki fieldwork to fa dake matar dashi sai kun ga juna kawai musamman wurin rikici ne. Mafiya yawan lokuta duk inda sojoji suka je kai taimako na tsaro indai wata mushkila ta taso da za'aji rauni ko rasa rai da wuya idan ba cikinsu bane. Mu muna gida muna jiran tsammani bayan ko su a junansu sun sani kila fa idan na tafi nine bazan dawo ba ko abokin aikina wane. Babban tashin hankali shine kiga wasu sun fara dawowa baki da cikakken bayani game da naki mijin. Kullum kina cikin shiri kiyi wanka kiyi girki ki gyara gida kina sa rai yau ne, gobe ne, jibi ne zai dawo gareki. Idan da rabo ya dawo idan babu kuma sai dai sakon mutuwarsa" ta karashe da wani irin matsanancin kuka.