← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 157

Sashe 68

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ga mamakin su duka ukun Radhiya ta gyada kai. Daddy kansa sai da ya girgiza ba Awwab da ya daga murya yace "karya take yi Daddy"

Daddy yace "Awwab ka nutsu ko ka fita"

Zama ya koma yayi amma babu nutsuwa bare kwanciyar hankali. Ita wadda akeyi dominta kuka kawai take yi idanunta sunyi luhu luhu dama shi ta kwana tana yi.

"Muna sauraronki Radhiya"

"Daddy karatu nake son yi"

"Banda abinki Radhiya waye yace miki aure na hana karatu?" Mami ta tambayeta tana dan sakin rai a zatonta wautar ce ta motsa.

"Ba nace miki zan samar miki admission a Abuja ba?" Awwab ya ce muryarsa tana rawa yana kokarin danne bacin ransa.

"Daddy ni dai don Allah bana son auren nan gabadaya"

"Alheran!!!" Awwab ya daka mata tsawa ta kuwa sake tsorata ta fashe da wani kukan.

Gaban Daddy ya koma ya durkusa "don Allah kada ka saurareta wallahi karya take yi Daddy. Ka aura min ita ko ranar asabar ne tare dasu Zahra please Daddy"

Ummi ma dai kukan take yi tana tausayawa yaran har ta fara jin ko dai tayi kuskure ko matakin da ta dauka yayi tsanani da yawa.

"Ba kya son auren ko Radhiya?"

"Eh Daddy"

"To tashi ki tafi wurin 'yan uwanki na kashe maganar zan nemeki daga baya"

Baki Awwab ya saki yana karyata abinda kunnuwansa suka ji daga gareta da kuma Daddy. Jiki a mace ta tashi zata fita yasha gabanta.

Da fada ya fara cewa "Ni zaki yiwa haka Alheran? Ba sai da na nemi izininki ba kafin nazo na fadi cewa zan hadaki da Ghazalatu ba? Kuma yanzu ta fasa bazan hadaki da wata ba I promise" ya kare da kwantar da murya.

Daddy sai da yayi masa tsawa ya fita a fusace jikinsa yana rawa. Dakinsa ya tafi yana shiga sai ga hawaye. Ransa yaji ya kuma baci ya rasa me zaiyiwa kuka tun girmansa sai mace. Macen ma Alheran da ya bawa dukkan soyayyarsa a cikin abinda baifi wata daya ba amma tasa kafa ta ture saboda dalilin da bashi da muradin sani. Itama tana fita dakinsu Zahra ta nufa tana nata kukan kamar ranta zai fita. Bata hangowa kanta sauran farinciki tunda ta rasa Awwab.

Shiru falon yayi Ummi na goge hawaye Mami ta rasa me zata ce ma. Tashi Ummi tayi zata fita taji muryar Daddy a sojansa.

"Mairama dawo ki zauna ki fada min dalilinki na raba yaran nan"

Gabanta ne ya fadi Mami ta bita da kallon mamaki. Soja ba abin rainawa bane. Yanayinta kadai ya sa shi saurin fahimtar tana da hannu a abinda Radhiya tayi. Zama tayi ta nuna musu babban kuskuren da yake tattare da batawa da 'yan uwansu saboda yara. 

"Yau da Allah Ya dauki raina bayan rasuwar babansu Karami ina mai tabbatar muku dawowar nan da kuka yi zaku sami yaran nan cikin mafi munin yanayi ne saboda babu wanda zai tsaya min ya kula dasu a gidanmu yadda ya dace. Gidan nawa mahaifin babu shakuwa babu sabo tsakaninmu sama da mutum ashirin. Wadda muke tamkar 'yan biyu da ita komai namu tare tazo ta juya min baya a dalilin son da ta yiwa Zayyan tun yana raye. Tun kafin muyi aure ta dauki gaba dani har yau bata sake zani ba. Ba yau da muke tare da 'ya'yanmu bace abin ji, gaba da bata da kadan Daddy ita ce abin dubawa. Mami don Allah ki sasanta da 'yan uwanki kafin kiyi tunanin auren nan. Kada ki manta a dalilinsa rigimar ta faro na tabbata ana yinsa sai abin yafi haka"

Sai yanzu Mami ta soma hawaye itama ta san cewa gaskiya Ummi ta fada. Duk da haka Daddy yace "da sai kiyi mana bayani ba sai kin raba su ba. Ummi yau kinsa Awwab da Radhiya kuka anya bazamu hukuntaki ba?" Ya kare da murmushin dattako.

"Nasan idan da ta amince babu abinda zai hanaka daura musu aure. Radhiya dai 'yarka ce wani ma zaka iya bata bare Awwab. Alfarma daya nake nema ayi sulhu a daidaita zumuncin da yake neman lalacewa. Idan haka ta faru ko gobe ne wallahi ayi musu aure"

Tana kaiwa nan ta tashi ta bar falon. Mami tana kuka tacewa Daddy hakika Mairama tayi zurfin tunani bata so kanta ba ta hakura da farincikin 'yarta dominsu. Sun yabawa Zayyan a baya yau suna yabawa matar Zayyan saboda a karo na biyu wannan iyali sun sadaukar da nasu jindadin don su kyautata musu.

BAYAN SHEKARA DAYA

Matashiya ce kyakkyawa sanye da riga mai dogon hannu baka mai kanun fulawoyi jajaye wadda ta tsaya mata a rabin cinya da skirt mai fadi shima baki tayi rolling da mayafi ja. Takalmanta loafers ne bakake da bakar jaka mai fadi wadda ta saka computer da tarkacen litattafai. Siririn agogon hannunta ta kalla tasan cewa kowane lokaci daga yanzu Yousuf zai iya kiranta su tafi gida.

Watanta tara tana daukar kos na koyon turanci da faransanci sannan aka samar mata gurbi a University of Grenoble dake kasar Faransa inda ta fara karatu sati uku da suka wuce a fanin aikin jarida wato mass communication. 

Kamar yadda tayi hasashe wayar Yousuf ce ta shigo mata ta taso tana tafiya kai baka taba cewa Radhiyan rugar Barkindo bace. Ta koma hadaddiyar budurwa mai ji da gayu da wata irin nutsuwa kamar ba ita ba.

Kamar kullum sai da ya bude mata ta zauna sannan ya shiga ya tayar da motar. Gaishe shi kawai tayi ta soma waya da Umminta wadda take karatun jarabawa saboda tuni itama ta koma karatu ta sami gurbi a jami'ar Bayero ta Kano tana karanta Adult Education. Mairama Ali Gidado ta zama babbar mace da maza suke kawowa hari ta kowane fanni suna neman aurenta. Da yawa basa yarda ma tana da yara biyu matasa da suke karatu a jami'a.

"Ina Tante din taki ko kina makaranta ne?"

"Ina hanyar komawa dai Ummi"

"Kice ina gaisheta. Gobe zamu je NDA na fada miki za'ayi taro kuma Karami yana cikin masu yin match pass"

Turo baki tayi cikin shagwabar da Tante dinta take kara ingizata take yi yanzu tana biye mata tace "ni yanzu bazan gani ba kenan? To ku daukar min video kinji Ummina"

Dariya Ummi tayi ta rasa yaushe Radhiyanta zata girma "zan dauka in sha Allahu 'Yar soja rigima"

Dariya tayi mara sauti Yousuf ya kalleta yana jin lokaci yayi da zai sanar da mamansa ya mugun kamuwa da son 'yarta. Sun cigaba da hirarsu da suka gama ta kira Ibrahim tana tambayarsa progress din jikin Baba Hadir.

"Akwai babban albishir sai na koma gida zamuyi skype. Ke dai bari kawai na tsakura miki, ya fara tafiya babu sanda"

Wata dariya da tayi sai da Yousuf ya manta me yake yi na dan lokaci. Tana zuwa gida da sauri ta shiga ta haye sama dakin 'yar Mammee wadda ta kasance kanwa kenan ga mahaifinta Zayyan mai suna Nasara ta fada jikinta tana murna.

"Tante Babana Hadir ya soma tafiya babu sanda"

"Da gaske Alheran" tace tana tayata murna.

"Oui Tante" (eh anti) tace tana rungumeta.

"To maza kije kici abinci kizo"

Radhiya na fita Nasara tana kallonta zuciyarta fes. 

Bayan fasa aurenta da Awwab wanda yayi sanadiyar da ya bar gidan ana dawowa daga daurin auren kannensa ya koma Abuja kwana uku kafin hutunsa ya kare. Yayi fushi sosai da Radhiya wanda har Daddy yayi masa bayanin dalilin yin hakan bai dena jin zafin abin ba. To bayan komawarsu ne aka turo daukarsu daga Nijar inda suna zuwa Nasara diya ga Mammee tazo hutu da mijinta da dansa Yousuf wanda mahaifiyarsa ta rasu ta shiga rokon arzikin a bata ita. Bata taba haihuwa ba gashi tana da son yara. Ita tana yi mijinta na tayata aka kai maganar gaban Ummi ita kuma tayi kawaicin hadasu da Daddy. Ba tare da bata lokaci ba ya amince ko babu komai yana sa ran zata samu kyakkyawan sauyi a rayuwa. Zamanta tare dasu ba'a cewa komai sai son barka. Nasara tamkar ta goya Radhiya don so. Babu ta inda ta rageta ta fanin gyara shiyasa tun a yanzu tayi fice ta wuce raini nesa ba kusa ba. Kakaninsu ba a barsu a baya ba wurin yi musu aike ita da Emzee duk karshen wata.

Emzee ma sun so rike shi a Nijar amma fafur yaki shi soja yake son yi abinda bai taba fadawa kowa ba. Cikin dan kankanin lokaci Daddy da taimakon Captain Onomza suka samar masa admission. Ibrahim kuma ya sami Law a Buk itama Ummi ta sake WAEC shekara na zagayowa ta koma makaranta. Gidan Zayyan na Kano Alh Sidi yayi mata gyara na gani na fada ta koma tare da kanwarta daya da kaninta wadanda su ma suke karatu kuma take ta kokarin gyara zumuncin gidansu shiyasa ta taho dasu.

Baba Hadir kuma watansu uku suka dawo yana motsa hannuwansa da kafa amma tafiyar bata kankama ba sosai sai yau da Ibrahim ya fadawa Radhiya.

***********

"Dad please kaje dani mana"

"Ke komai kike so sai anyi miki ne kamar wata yarinya?" Inji mamanta

"Kina matsa mata da yawa fa. Meye a ciki don ta raka babanta taron karrama sojoji masu fita (POP)"

"Naga official taro ne your excellency " maman tace tana murmushi.

"Official baya nufin naki zuwa da 'yata. Arifah ki shirya dake zani Kadunan"

Bayan ta fita daga dakin nasa tana dariya mamanta ta sake sako masa zancen rashin aurenta da yake damunta.

"Kasanta da jin kai gashi masu yawan zuwa yanzu yawanci duka saboda mukaminka suke son ace sun zama surukan gwamna"

"Ki dena damuwa mijinta yana tafe in sha Allah. Ni fa tafiyar nan wani dadi nake ji game da ita na rasa dalili."

Murmushi tayi tana tunanin ko don yana kewar harkokinsu na sojoji ne. Gashi a matsayinsa na tsohon soja an gayyace shi bako na musamman a taron POP din sababbin jaruman da kasa zata yaye bana.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Harabar Nigerian Defence Academy  (NDA) ciki da waje cike yake da motoci kala kala na dunbin jama'ar da suka zo musamman domin taya 'yan uwansu murnar gama karatu da fita da mukamin second Lieutenant ga mafiya yawansu. Kalilan a ciki irin su Mairama sun zo ne domin karfafawa 'ya'yansu gwiwa.
Chapter 68 · 0% Book details