← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 124 OF 157

Sashe 124

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Hamma manaa" ta langabe kai.

"Allah bazaki je kiyi rawa a wurin nan ba"

Idanu ta zaro "harda rantsuwa?"

"Kinga ya dace?"

Juyawa tayi ta hango Yousuf yana cewa Arifah wai zaiyi rawa tazo tayi masa video.

Kuka take shirin yi tace "Ka gani fa kowa yana yi"

"Mu ba kowa bane. Sunana Awwab sunki Alheran...don't tell me you expect me to seat here and watch you dance a gaban mutane"

"To...to..." kasa karasawa tayi sai dai ya sani ran ta ya baci. Dauke kai yayi ta gama kunkunin ta yana tunanin ma harda hawaye amma yaki bari ta tashi saboda indai akan tayi rawa gaban mutane ne ya yarda tayi ta fushin ya rarrasheta daga baya.

Tana ji tana gani wakar ta kare aka sako wata Awwab ya tashi dama magrib ta gabato "ki jirani a nan zanje na shigo da mota ciki na kiraki mu tafi"

Shan kunu ta sake yi harda kawar da kai gefe ya sunkuyo da kansa wurin kunnenta "you still look sweet" ya yafi. Murmushi tayi duk da ba wai ta hakura bane. 

To filin rawa ma Zayyana na hada ido da Ibrahim yana zaune da robar ruwa a hannunsa ya sha kunu yana mata nuni da ta fita da hannu. Kafada ta noke ya kuma hade girar sama da kasa dole ta fita tazo wucewa ta gefensa ta murguda masa baki.

"Naji dai, rawa ce ban yarda ba" taji yace yana murmushi.

Rahima dama bata shiga ba don bata iya ba tayi zamanta sai jakunkunan su Hibbah da Zayyana da su ka bar mata. Karamar wayarta kirar samsung sabuwa mai torchlight ce a hannunta tana game din snake jikinta ya bata kallonta ake yi ta baya. Juyawa tayi a hankali ta ga Emzee yana murmushi.

Kujera yaja a kusa da ita ya juyata ya ware dogayen kafafunsa ya zauna ta yadda gabansa ne ke fuskantar bayan kujerar ya dora hannuwa a samanta kansa akan hannuwan.

"Kinsan saurin da na rinka yi kuwa da naje raka abokai na?"

"Meya faru?"

"Kawai waka na jiyo nace Allah Yasa kada Rahiman Muhammad tayi rawa if not tear gas zan saki a wurin nan bayan na kai su Daada gida"

"Meye tear gas kuma?"

Yadda tayi tambayar kadai yasa shi shagala da kallonta kafin ya yi mata bayani. Kanta a kasa take dariya da yace shi fa kishi gareshi "samarinki nawa ki kawo numbers dinsu yanzu duk na kirasu na fada musu anyi miki miji"

"Goma ne ba yawa kasan ba wani farin jini gareni ba" Rahima tayi dariya saboda kafin ta kai karshe ya kusa tuntsirewa daga kan kujera.

Gyara zamansa yayi yace yana bata fuska "Kasheni ki huta" 

Shiru yaji tayi ya kira sunanta bata amsa ba. Tashi yayi ya dawo gabanta ya tsuguna yana leken fuskarta. Hawaye ya gani suna gudu akan fuskar da yake matukar so yaji hankalinsa ya tashi. Ya san iyakarsa ba don haka ba da ya rungumeta ya rarrasheta.

"Rahiman Muhammad?"

"Uhmm" tace da muryar kuka.

"Na bata miki rai ne?"

Gyada kai tayi "eh"

Zuciyarsa yaji tayi masa nauyi "Ya Salaam me nayi miki?"

"Cewa kayi fa na kasheka" ta fashe da kuka sosai.

"Oh my God...am sorry kinji wasa nake yi"

Soyayyar da suke yiwa juna ba ta wasa bace. Kowa na damuwa da damuwar dan uwansa. Hankalinsa ya tashi da kukanta ita kuma bata kaunar wani abu ya gifta tsakaninsu musamman mutuwa a yanzu da take jin ta samu farinciki irin wanda bata taba tunanin akwai ba.

Irin matar da yake mafarkin samu mai shagwaba ya gani a tattare da Rahima saboda yadda take yi da fuska da muryarta "To ka dena cewa in kasheka" 

"Na dena...ban karawa"

Wayar hannunta ya karba ya saka numbarsa yayi dialling layinsa yana cewa "in chanja miki waya?"

"A'a wannan ma sabuwa ce. Sai mun gama WAEC za'a bani wata" tace da murmushi tana tuna abinda Ummi tace mata ranar da ta bata wannan din.

"Ajinki nawa? No shekarunki nawa kada ace ina koyawa yarinya soyayya fa" Emzee yace yana dariya.

"Ajina hudu a primary kuma shekarata 13"

Kallonta yayi yasa yatsansa a baki ya ciza "da gaske? 13 amma kika iya kallon soyayya? Wannan idan kika 20 na zama sorry"

Rahima sai dariya take irin wadda bai taba gani tayi ba hankalinta a kwance "kuma babana yace kada na kula kowa sai nayi 25"

"Ba damuwa nima ba kulaki zanyi ba aurenki kawai zanyi sai ki karasa primary din a gidana" ya amsa mata don ya fuskanci tsokanarsa kuma take yi.

Kalmar aure da ya sako ita ta kashe mata baki. Ya samu ta fada masa ainihin shekarunta wato sha shida da ajinta a makaranta. A take yayi mata alkawarin yana yin POP zai fadawa Daada a nema masa aurenta.

Ko da wasa Rahima bata kawo cewa Emzee bai san ko ita wacece ba. Dadin hira ya saka shi mantawa da yi mata wannan tambayar tunda ta tabbatar masa da cewa tana nan a gidan sai bayan bikin Radhiya.

**********

Wayar ta kalla tana ringing tasan Awwab ne ta kuma tura baki kamar yana wurin sannan ta dauka "fito mu tafi" kawai yace.

Tafiyar kurame suka yi zuwa gidan ashe an fara komawa saboda iyayensu maza sun ce a gida za'ayi magriba babu wanda za'a bari a wurin taron. Yasan Yousuf da Arifah zasu tafi yau ma zaiyi rakiya shiyasa bai neme shi ba. Suna zuwa gida sai nishadinsa yake fushinta kamar baya damunsa ya fito ya zagaya ya bude mata itama ta fito. Hannunta ya kama kai tsaye ya wuce falon da su ka je jiya da ita.

Wayarsa ya dauko ya bude wakar yar amana ta youtube sannan ya kama mayafinta ya cire ya ajiye akan kujera.

"Kinsan wahalar da nasha kafin na sami wakar nan a youtube kuwa? Ni bana gane me suke cewa da kyar naji ance 'yar amana shine na nemo miki" idanunsa ya dora a kanta yana ganin yadda tayi kyau sosai kamar wata 'yar tsana "baby ga 'yar amana ki tashi muyi rawa"

Shan kunun ne ya kare ta soma dariya da Awwab yayi playing wakar.

"Wai da gaske nemo min kayi Chèri?"

"Anything to see your smile Schatzi" ya janyota jikinsa yana shafa gefen fuskarta.

Tsigar jikinta ke tashi ta soma rawar jiki ya rungumeta tsam a jikinsa.

"Calm down ba yau zan baki tsoron ba ai. Rawa zamuyi kuma bazan bari ki fita a falon nan ba sai kinyi"

Sai yanzu take jin kunya sosai "Hammana na tuba kayi hakuri" 

"Baby I want to see you dance...ba wai don na hanaki ba dazu wannan bazan taba yarda dashi ba amma between us harda kafi rawa zamu rinka yi a gidanmu"

"To ai dai nan ba gidanmu bane kayi hakuri" tace ido wiki wiki tana nadamar yi masa gardama don ya hanata rawa.

"Tunda ance sai anyi biki zaki tare kowa sai ya rufe ido kawai a barni duk inda kike muna tare"

"Naji amma na fasa banda rawa...kunyarka nake ji"

Fuskar tausayi yayi "Inje gida inyi kuka?" 

"A'a"

Kashe wakar yayi ya kunna wata ta cikin wayarsa da yake yawan kunnawa idan yana tunaninta lokacin da suka yi fada mai suna You and I. Kidanta cikin taushi yake tashi babu hayaniya ko kadan sai kalmomi masu tasiri a zuciya. Takalmanta ya fara cire mata matsu tsini shima ya cire nasa sai safa. Wani irin riko Awwab yayi mata ya duko da kansa ya hade goshinsu. Hannuwansa na kugunta nata a kafadarsa sun zagaye wuyansa a hankali yace "hau kan kafafuna"

Runtse idanunta tayi ta dora kafa daya a hankali tana jira taji ko zaice tayi nauyi ko ta cire sai taji yace "dora dayar"

A tsaye take amma akan kafafun mijinta sannu a hankali yake bin kalaman wakar yana fada a saitin kunnenta yayin da yake tafiya a nutse suna takun rawa amma shi yake yin duka motsin. A haka suka kwashe kusan minti hudu bai nuna gajiya ba yana rike da ita suna musayar numfashi har wakar ta kare.

"Duk lokacin da kike son yin rawa baby zan tayaki, a gaban wasu ne kawai ban yarda ba saboda ina kishinki. Da sonki na girma a zuciyata kina tunanin akwai ranar da zanso bata miki rai da gangan?"

Girgiza kai tayi a hankali kalamansa na shigarta sosai kawai ta rungumeshi tana masa kukan da ake kira na kissa batare da tasan ma'anarsa ba. Idan an barta bata san dalilin hawayen nata ba idan ka cire tsantsar soyayyar Captain Muhammad Awwab Mustapha.

Habarta ya dago suna kallon juna ta kasa tsayar da hawayenta.

"Kukan na meye?"

"I. Love. You Chèri"

Kamar jira yake ta fada ya soma kissing dinta sosai. Karatu suka ji alaman an kusa kiran sallah ya dawo dasu duniyar da suke ya shafi gefen fuskarta "Da nasan hanaki rawa ne zai sa naji da kanki kin fada min wadannan kalmomin da na dade da cewa ban yarda da rawa ba"

Duka ta kaiwa kirjinsa ya saketa ta dauki takalminta ta saka sannan ta bude jakarta ta fito da janbaki za ta kara sakawa.

"Ana kiran sallah za ki sake kwalliya?"

Kunya taji tayi saurin mayarwa sai da ya matsa mata tace "Jiya Adda Fauzy cewa tayi wai an shanye min janbaki" 

"Mata. Mata sai a barku...an fada min kuna zuwa ma ganin tafiyar amare washegarin da aka kaisu ko" yace yana tsareta da ido.

Ba karamin rikicewa tayi ba kuwa don babu karya ko ita sun gama JS3 da akayi bikin wata 'yar ajinsu kawayensu suka ce wai azo aje gulma. Da ita aka je din amma babu abinda chanjin tafiyar kawar tasu ya sa mata a rai sai tunanin ko duka mijin yayi mata. A lokacin ta yiwa kanta alkawarin idan tayi aure miji ya kawo mata wargi sai dai su daku don ba kyalewa zata yi yaci zalinta ba. Murmushi ne ya subuce mata da ta tuna lokacin da sharrin kuruciya.

Hannuwansa duka ya dora a ka "Na shiga uku kin taba zuwa kenan nima za'a zo mana"
Chapter 124 · 0% Book details