Sashe 91
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"In kin isa Allah shi tsinan. Kin kuwa san ko ni wanene da zaki cuceni haka? Kalleki fa babu body babu alamar body sai tumulin 'ya'ya. To ki tashi tun muna shaida juna kije ki tashesu ku bar min gidana"
Bata nuna masa ranta ya baci ba tana cin naman da ya soma kasa tace "ka dai yi hakuri mu wayi gari sai su koma gidanmu. Idan na tashesu cikin dare yanzun da wahala suke boye maitarsu. Idan naman kazar bai ishesu ba sai ka ga cikin mutanen gidan nan ana ciwo ya kama wane. Kaga bazan so ba"
Baki na rawa duka makaman yakin nasa suka bace yace "kina nufin wai...wai...wai ku din...kina dai nufin"
"Mayu ba. Nayi zaton ma Kawuna ya fada maka tun lokacin da ka tura wakilanka. Kada ka damu indai zasu ci nama su koshi wallahi babu mai sani a gidan nan. Idan ba haka ba....toh...don shi babban da na taho dashi ma cewa yake wai ya ga cinyoyinka kamar..."
A tsorace ya rike cinyoyin nasa ita kuwa ta ci naman nan duka ta cinye. Tun daga ranar kwanaki shida kenan kullum babban danta wanda ba ma a gidan yake ba zai je gonar Mamamijo ya debo kaji ko zabi kamar biyar su gyare shi da 'yan uwansa a tsakar gidan ayi dabge a ci sauran na gani. Malamijo bala'in tsoronsu yake ji ya kuma kasa fadawa kowa dom yanzu tsorata shi take yi har cikin dare duk da karyar maita tayi. Ya kara ramewa ya tsotse babu mamora a jikin. Hajiyayye banda nama sai tatike shi take da karyar maita yana bata kudi. Su Yadikko nasu ido ne babu mai cewa komai an barshi da sababbin iyalinsa.
**********
Kwana biyu da dawowar Zayyan sun buga soyayya shi da Mairama ko farkon aurensu albarka. Gaishe su kawai yaran ke zuwa yi babu mai zama a bangaren. Su Radhiya ma basa kwana sun koma tsakanin gidan Mama da Mami. A haka ance musu wai su barshi ne ya huta. Yau suke sa ran kiran 'yan uwa a waya a sanar dasu idan ya dawo daga headquarter. Zasu karasa hada duk abinda ya dace ne domin ya zamana komai anyi shi officially.
Awwab yaji sauki kuma nan da kwana biyu yake son komawa ya karasa abinda zaiyi ya dawo kafin hutun ya kare a aura masa Alheran. Raji da Zahra su ma zasu tafi Osun wurin dangin iyayensa. Daga can su je Katsina sannan su koma Germany.
Arifah da mamanta sunzo jiya yau kuma tace akwai fa zuwansu park ita bata hakura ba su shirya zata zo su tafi. A gidan kuwa tayi laasar washegari suna yin sallah suka shirya zasu tafi. Awwab ya dauki Raji a gaban mota sai ,Zayyana da Radhiya a baya. Ibrahim da Emzee a motar Mama sai su Fauziyya a motar Arifah. Wani sabon park ta kaisu na dan wane da wane. Ba tsada bace da shigarsa sai dai masu zuwa da irin abubuwan da ake saidawa kaji pure water guda daya naira ashirin ya sa ba kowa ke iya zuwa ba. Hakan ya kare shi daga zama matattarar 'yan kwaya kowa ka gani yana kokarin nuna shi din ya isa.
Wurin ya kawatu da flawoyi kwantacciyar ciyawa da mutum zai iya zama a kai ko babu shimfidar komai. Ga wani abu kamar korama ruwa yana wucewa da gudu. Akwai manyan bishiyu masu kara masa ni'ima da daddadar inuwa.
Suna fitowa Emzee da Ibrahim ne suka dauko carpets da za'a shimfida. Raji ya dauko cooler din da aka zuba robobin ruwa da gwangwanayen lemuka cikin kankara. Zayyana da Radhiya kwandunan abinci shi kuma Awwab ya nufi wurin masu gasa nama Arifah ta biyo shi.
"Captain yaushe ne komawar taka?"
"Jibi. Akwai sako ne?"
"Not really.."tace tana dan murmushi. Mayar mata yayi yana jinjina kai.
"Akwai wata a kasa kenan. Haba kanwata kada ki boye min komai"
Radhiya ya gani ta nufosu fuskarta babu walwala. Dama tun a gida ya kula kamar ma bata son fitowar. Shi kuma dama ce yake gani saboda baya samun chance din zama da ita suyi hira. Idan ba'a kirata ba to tana wani aiki. Tayi kyau sosai cikin pakistan da ta saka. Rigar baka da aikin zare pink sai pink din wando mai fadi da pink din mayafin da ta yafa.
"So cute" ya furta a hankali gabadaya hankalinsa ya koma gareta.
"Muna komawa gida zan bada shawarar ayi ayi bikin nan naku kafin a nemi 'yar mutane a rasa" Arifah tace tana dariya.
"Da kin kyauta. Yanzu dai zaki fada min me kike son fada ko we talk some other time? Schatzi akwai kishi yanzu haka sai nayi lallashi"
"Ahhh to bari na gudu kada ta hanani yayanta"
Wurin wasu kujeru da aka baza a karkashin bishiyon Radhiya ta koma ta zauna takaici ya isheta da kishi.
Awwab na jin me Arifah tace ya gama karbae ledojin naman yace "wanne? Emzee fa kaninta ne"
A kunyace tace "ba shi ba...how much do you know about Yousuf? Yana kirana kuma dai nima I like him"
Da farinciki yace "in sha Allahu baki da matsala kanwata. Maybe maganarki yace yana son muyi"
Amma wannan hadi yayi masa sosai. Tare suka taho inda Radhiya take Arifah ta karbi ledojin don bata da girman kai shi kuma ya zauna a kujerar dake kallonta.
"Schatzi, kishi?"
Tsuke baki tayi taki yi masa magana ya tashi yaje ya dauko musu maltina guda daya ya dawo. Bai ce komai ba ya bude ya sha ya tura mata. Sai da ta dan murguda baki wannan dimple din mai bashi sha'awa ya motsa ta dauka ta sha itama ta tura masa. Haka suka yi har ta kare.
"Zaki kara?" Ta noke kafada. Haushin nata da biyu ne dama. Ga dariyar da yake yiwa Arifah ga tafiyarsa jibi duk ya dagula mata lissafi. Tun bai tafi ba ta soma jin kewarsa. Sati uku yace zaiyi mafi karanci ko yayi wata guda. Duka duka yaushe suka daidaita yake tunanin sake tafiya ya barta.
Yatsa taji ya kada a kusa da fuskarta ta dago daga tunanin da take yi tana kallonsa.
"Indai Arifah kike yiwa wannan fushin ki dena zancen Yousuf muke yi. It seems sun daidaita"
Duk da tana kokarin boyewa ya kula da dadin da hakan yayi mata amma sai ta sake dinke fuska.
"Me kuma nayi? Kinga tafiya ce a gabana bana son wannan fushin"
Kwallah ya gani ta ciko idon ya sosa mata inda yake kaikaiyi.
"Ya Allah" yace ya soma damuwa "Alheran ba kya son na tafi ne?"
Kifa kanta tayi akan teburin gabanta bayan tace eh.
"Kada ki bari hawayen nan ya fito"
"Me yasa?"
"Zaki sani rarrashin da bai kamata nayi ba with a hug and maybe a..."
Dagowa tayi da sauri "na dena don Allah. Sai ta ga yana kallon fuskarta shine ta taba idonta taji danshi "kadan ne ya digo Hammana kuma ba ni na fito dashi ba"
Tasowa yayi daga wurin zamansa yana zagayawa gabanta a hankali "ya na iya tunda ya fito sai na rarrashe ki....come here"
Ba shiri ta mike itama tana ja da bayan "Allah na dena fa...ka tsaya a inda kake"
Bai dakata ba ya cigaba da matsowa "ga wani nan ma yana zuba. Schatzi tana bukatar rarrashi irin wanda ni kadai zanyi mata ko"
Ga kunya tana ji ga zancen yayi mata girma sauri ta kara ta na neman ina sauran suke "ba hawaye bane ruwa ne"
Idanunsa har wani ciki suka yi yace "kin fara karya ne? Ina kika ga ruwan?"
"Uhmn, uhmm yawu ne kaga" ta tabo idon ta nuna masa.
Cak ya tsaya ya kwabe fuska "ashe baki dena kazanta ba"
Dariya ta koma yi "zaka taka danyen..."
"Stop Alheran, bana son kazantar nan taki"
Ta kuwa cukule tana jindadin yadda ta dawo ita yake gudu "kalli mana ka gani danyen...."
"Schatzi!"
"Oui ma Chérie" ta amsa innocently kamar bata san me take yi masa ba.
"Ko ki bari...."
"Ko kayi me?"
"Kada ki kureni ki ga me zanyi din fa" ya gargadeta da hannu yana dawowa kusa da ita suka soma jerawa suna gangarawa hanyar inda sauran suke.
"To nayi shiru."
"Better. Call me that name again. Dama na gaji da Hamman nan. Su Zayyana su fada kema ki fada babu bambanci"
"Chérie" tace da wata irin siga mai shiga zuci.
"Meaning?"
"Daidai da Schatzi amma french version"
Tsayawa yayi a gabanta ya hanata cigaba da tafiya "idan na dawo bana son ko sati muyi ba'a daura aurenmu ba. So tun yanzu ina fada miki zan sanar da su Baba. Idan kinso ana tambayarki ki sake cewa baki shirya ba"
Dariya ya bata tace masa ko gobe yake so ta shirya.
"Da kin raina kanki kuwa"
Nutsuwa tayi a ladabce tace "Me yasa? Dukana zaka yi?"
Sai da tasa shi dariya "Matsoraciya ina kika baro 'Yar Soja nasan da ita ce cewa zata yi bismillah "
" 'Yar Sojan lafiya bayan ta kare min ina nan ina son dreba"
Yana juyowa suka hada ido ta gudu duk kiran da yake mata kunya ta hanata tsayawa. Bata sake bari sun zauna su kadai ba saboda kunyarsa da ta rinka ji. Da ana daukar hotuna kuwa fafur taki yarda ayi musu su biyu.
**********
Rama 'yar asali ba bogi ba Malamijo ya sake yi gabadaya ya sake karewa sai kasusuwa sai kayi zaton mayun gidansa sun fara lasarsa ne. Gidan gonarsa yaje za'ayi lissafin abincin dabbobin da kuma ware wadanda za'a kai Enugu karshen sati.
Yana zuwa babban yaronsa Talle ya soma cewa "Yallabai an fitar da shanun da ka turo a dauka. Gaskiya kayi dabara da kace a rage wasu saboda nan din ya soma matsarsu basa walawa sosai"
A take ya soma zufa duk da sanyin gari "wadanne shanu kenan?"
"Wanda ka turo dan wajen amaryarka mai zuwa daukan kaji ya dauka mana. An bashi ashirin da uku yanzu saboda motocin sunyi kadan zai dawo a cike hamsin din"
Jiri ne kawai ya soma dibar Malamijo saboda tashin hankali jikinsa yana rawa yace "ni ne zan turo a kwashe shanu? Da can a ina suke ban ce a raba ba sai yau?"
"Ba dai karya yayi min ba yaron nan? Kusan awa guda da tafiyarsa"
Bata nuna masa ranta ya baci ba tana cin naman da ya soma kasa tace "ka dai yi hakuri mu wayi gari sai su koma gidanmu. Idan na tashesu cikin dare yanzun da wahala suke boye maitarsu. Idan naman kazar bai ishesu ba sai ka ga cikin mutanen gidan nan ana ciwo ya kama wane. Kaga bazan so ba"
Baki na rawa duka makaman yakin nasa suka bace yace "kina nufin wai...wai...wai ku din...kina dai nufin"
"Mayu ba. Nayi zaton ma Kawuna ya fada maka tun lokacin da ka tura wakilanka. Kada ka damu indai zasu ci nama su koshi wallahi babu mai sani a gidan nan. Idan ba haka ba....toh...don shi babban da na taho dashi ma cewa yake wai ya ga cinyoyinka kamar..."
A tsorace ya rike cinyoyin nasa ita kuwa ta ci naman nan duka ta cinye. Tun daga ranar kwanaki shida kenan kullum babban danta wanda ba ma a gidan yake ba zai je gonar Mamamijo ya debo kaji ko zabi kamar biyar su gyare shi da 'yan uwansa a tsakar gidan ayi dabge a ci sauran na gani. Malamijo bala'in tsoronsu yake ji ya kuma kasa fadawa kowa dom yanzu tsorata shi take yi har cikin dare duk da karyar maita tayi. Ya kara ramewa ya tsotse babu mamora a jikin. Hajiyayye banda nama sai tatike shi take da karyar maita yana bata kudi. Su Yadikko nasu ido ne babu mai cewa komai an barshi da sababbin iyalinsa.
**********
Kwana biyu da dawowar Zayyan sun buga soyayya shi da Mairama ko farkon aurensu albarka. Gaishe su kawai yaran ke zuwa yi babu mai zama a bangaren. Su Radhiya ma basa kwana sun koma tsakanin gidan Mama da Mami. A haka ance musu wai su barshi ne ya huta. Yau suke sa ran kiran 'yan uwa a waya a sanar dasu idan ya dawo daga headquarter. Zasu karasa hada duk abinda ya dace ne domin ya zamana komai anyi shi officially.
Awwab yaji sauki kuma nan da kwana biyu yake son komawa ya karasa abinda zaiyi ya dawo kafin hutun ya kare a aura masa Alheran. Raji da Zahra su ma zasu tafi Osun wurin dangin iyayensa. Daga can su je Katsina sannan su koma Germany.
Arifah da mamanta sunzo jiya yau kuma tace akwai fa zuwansu park ita bata hakura ba su shirya zata zo su tafi. A gidan kuwa tayi laasar washegari suna yin sallah suka shirya zasu tafi. Awwab ya dauki Raji a gaban mota sai ,Zayyana da Radhiya a baya. Ibrahim da Emzee a motar Mama sai su Fauziyya a motar Arifah. Wani sabon park ta kaisu na dan wane da wane. Ba tsada bace da shigarsa sai dai masu zuwa da irin abubuwan da ake saidawa kaji pure water guda daya naira ashirin ya sa ba kowa ke iya zuwa ba. Hakan ya kare shi daga zama matattarar 'yan kwaya kowa ka gani yana kokarin nuna shi din ya isa.
Wurin ya kawatu da flawoyi kwantacciyar ciyawa da mutum zai iya zama a kai ko babu shimfidar komai. Ga wani abu kamar korama ruwa yana wucewa da gudu. Akwai manyan bishiyu masu kara masa ni'ima da daddadar inuwa.
Suna fitowa Emzee da Ibrahim ne suka dauko carpets da za'a shimfida. Raji ya dauko cooler din da aka zuba robobin ruwa da gwangwanayen lemuka cikin kankara. Zayyana da Radhiya kwandunan abinci shi kuma Awwab ya nufi wurin masu gasa nama Arifah ta biyo shi.
"Captain yaushe ne komawar taka?"
"Jibi. Akwai sako ne?"
"Not really.."tace tana dan murmushi. Mayar mata yayi yana jinjina kai.
"Akwai wata a kasa kenan. Haba kanwata kada ki boye min komai"
Radhiya ya gani ta nufosu fuskarta babu walwala. Dama tun a gida ya kula kamar ma bata son fitowar. Shi kuma dama ce yake gani saboda baya samun chance din zama da ita suyi hira. Idan ba'a kirata ba to tana wani aiki. Tayi kyau sosai cikin pakistan da ta saka. Rigar baka da aikin zare pink sai pink din wando mai fadi da pink din mayafin da ta yafa.
"So cute" ya furta a hankali gabadaya hankalinsa ya koma gareta.
"Muna komawa gida zan bada shawarar ayi ayi bikin nan naku kafin a nemi 'yar mutane a rasa" Arifah tace tana dariya.
"Da kin kyauta. Yanzu dai zaki fada min me kike son fada ko we talk some other time? Schatzi akwai kishi yanzu haka sai nayi lallashi"
"Ahhh to bari na gudu kada ta hanani yayanta"
Wurin wasu kujeru da aka baza a karkashin bishiyon Radhiya ta koma ta zauna takaici ya isheta da kishi.
Awwab na jin me Arifah tace ya gama karbae ledojin naman yace "wanne? Emzee fa kaninta ne"
A kunyace tace "ba shi ba...how much do you know about Yousuf? Yana kirana kuma dai nima I like him"
Da farinciki yace "in sha Allahu baki da matsala kanwata. Maybe maganarki yace yana son muyi"
Amma wannan hadi yayi masa sosai. Tare suka taho inda Radhiya take Arifah ta karbi ledojin don bata da girman kai shi kuma ya zauna a kujerar dake kallonta.
"Schatzi, kishi?"
Tsuke baki tayi taki yi masa magana ya tashi yaje ya dauko musu maltina guda daya ya dawo. Bai ce komai ba ya bude ya sha ya tura mata. Sai da ta dan murguda baki wannan dimple din mai bashi sha'awa ya motsa ta dauka ta sha itama ta tura masa. Haka suka yi har ta kare.
"Zaki kara?" Ta noke kafada. Haushin nata da biyu ne dama. Ga dariyar da yake yiwa Arifah ga tafiyarsa jibi duk ya dagula mata lissafi. Tun bai tafi ba ta soma jin kewarsa. Sati uku yace zaiyi mafi karanci ko yayi wata guda. Duka duka yaushe suka daidaita yake tunanin sake tafiya ya barta.
Yatsa taji ya kada a kusa da fuskarta ta dago daga tunanin da take yi tana kallonsa.
"Indai Arifah kike yiwa wannan fushin ki dena zancen Yousuf muke yi. It seems sun daidaita"
Duk da tana kokarin boyewa ya kula da dadin da hakan yayi mata amma sai ta sake dinke fuska.
"Me kuma nayi? Kinga tafiya ce a gabana bana son wannan fushin"
Kwallah ya gani ta ciko idon ya sosa mata inda yake kaikaiyi.
"Ya Allah" yace ya soma damuwa "Alheran ba kya son na tafi ne?"
Kifa kanta tayi akan teburin gabanta bayan tace eh.
"Kada ki bari hawayen nan ya fito"
"Me yasa?"
"Zaki sani rarrashin da bai kamata nayi ba with a hug and maybe a..."
Dagowa tayi da sauri "na dena don Allah. Sai ta ga yana kallon fuskarta shine ta taba idonta taji danshi "kadan ne ya digo Hammana kuma ba ni na fito dashi ba"
Tasowa yayi daga wurin zamansa yana zagayawa gabanta a hankali "ya na iya tunda ya fito sai na rarrashe ki....come here"
Ba shiri ta mike itama tana ja da bayan "Allah na dena fa...ka tsaya a inda kake"
Bai dakata ba ya cigaba da matsowa "ga wani nan ma yana zuba. Schatzi tana bukatar rarrashi irin wanda ni kadai zanyi mata ko"
Ga kunya tana ji ga zancen yayi mata girma sauri ta kara ta na neman ina sauran suke "ba hawaye bane ruwa ne"
Idanunsa har wani ciki suka yi yace "kin fara karya ne? Ina kika ga ruwan?"
"Uhmn, uhmm yawu ne kaga" ta tabo idon ta nuna masa.
Cak ya tsaya ya kwabe fuska "ashe baki dena kazanta ba"
Dariya ta koma yi "zaka taka danyen..."
"Stop Alheran, bana son kazantar nan taki"
Ta kuwa cukule tana jindadin yadda ta dawo ita yake gudu "kalli mana ka gani danyen...."
"Schatzi!"
"Oui ma Chérie" ta amsa innocently kamar bata san me take yi masa ba.
"Ko ki bari...."
"Ko kayi me?"
"Kada ki kureni ki ga me zanyi din fa" ya gargadeta da hannu yana dawowa kusa da ita suka soma jerawa suna gangarawa hanyar inda sauran suke.
"To nayi shiru."
"Better. Call me that name again. Dama na gaji da Hamman nan. Su Zayyana su fada kema ki fada babu bambanci"
"Chérie" tace da wata irin siga mai shiga zuci.
"Meaning?"
"Daidai da Schatzi amma french version"
Tsayawa yayi a gabanta ya hanata cigaba da tafiya "idan na dawo bana son ko sati muyi ba'a daura aurenmu ba. So tun yanzu ina fada miki zan sanar da su Baba. Idan kinso ana tambayarki ki sake cewa baki shirya ba"
Dariya ya bata tace masa ko gobe yake so ta shirya.
"Da kin raina kanki kuwa"
Nutsuwa tayi a ladabce tace "Me yasa? Dukana zaka yi?"
Sai da tasa shi dariya "Matsoraciya ina kika baro 'Yar Soja nasan da ita ce cewa zata yi bismillah "
" 'Yar Sojan lafiya bayan ta kare min ina nan ina son dreba"
Yana juyowa suka hada ido ta gudu duk kiran da yake mata kunya ta hanata tsayawa. Bata sake bari sun zauna su kadai ba saboda kunyarsa da ta rinka ji. Da ana daukar hotuna kuwa fafur taki yarda ayi musu su biyu.
**********
Rama 'yar asali ba bogi ba Malamijo ya sake yi gabadaya ya sake karewa sai kasusuwa sai kayi zaton mayun gidansa sun fara lasarsa ne. Gidan gonarsa yaje za'ayi lissafin abincin dabbobin da kuma ware wadanda za'a kai Enugu karshen sati.
Yana zuwa babban yaronsa Talle ya soma cewa "Yallabai an fitar da shanun da ka turo a dauka. Gaskiya kayi dabara da kace a rage wasu saboda nan din ya soma matsarsu basa walawa sosai"
A take ya soma zufa duk da sanyin gari "wadanne shanu kenan?"
"Wanda ka turo dan wajen amaryarka mai zuwa daukan kaji ya dauka mana. An bashi ashirin da uku yanzu saboda motocin sunyi kadan zai dawo a cike hamsin din"
Jiri ne kawai ya soma dibar Malamijo saboda tashin hankali jikinsa yana rawa yace "ni ne zan turo a kwashe shanu? Da can a ina suke ban ce a raba ba sai yau?"
"Ba dai karya yayi min ba yaron nan? Kusan awa guda da tafiyarsa"