Sashe 80
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"This way Sir" Chief Warden yace masa ya bi bayansa. Sun fara tafiya ya juya ya kalli prison din da jama'ar cikinsa sai ya tsaya at attention ya kame yayi saluting dinsu. Da yawansu su ma sai suka yi masa wadanda suka taba jin cewa soja ne suna taya shi murna.
Wani office aka kaishi Chief Warden ya bashi takarda ya saka hannu a kai sannan ya kuma gyara tsayuwa.
"Kai jarumi ne da ban taba ji ko ganin kamarsa ba. Kasarka bata san kana raye ba tsahon shekaru ashirin da biyu sai yau zaka koma gida. Ba kai nake tausayi ba sai ire irenka da dama da suke da rai a hannun abokan gaba ko kurkuku irin wannan batare da an sani ba. Goodbye Lieutenant"
Musabaha suka yi sannan ya kuma nuna masa kofa suka fito tare. Wani gate da bai raba sanin akwai shi ba duk tsayin zamansa a wurin suka bi sai ga motoci biyar a jere na Nigerian Embassy dake Liberia a baya kuma wasu uku ne na sojojin kasar.
Motar tsakiya aka nuna masa ya shiga yana jin kansa kamar a ire iren mafarkan da yake yi na komawa gida. Cikinta ma sojoji ne da sai suka yi saluting dinsa suka shiga aka tayar. Jiniya ce tun daga prison din har babban ofishin jakadancin Nigeria dake Liberia.
Awwab ya kasa zaune ya kasa tsaye haka ma Excellency. Duka a waje suke daidai kofar shiga tare da Ambasadan suna tsaye zugar motocin nan suka jeru a gabansu.
Kafin ya yunkura an bude masa kofa ya sako kafarsa waje sanye da takalmin roba da ya mutu murus. Kayan jikinsa a kode suke sosai. Fatarsa kuwa bai san cewa ta shiga wani yanayi ba sai da ya ga mutanen dake tsaye a wurin sun zuba masa ido.
"Uncle" yaji ance da muryar da ya sani. Chibuzor ne ya taho wurinsa da hawaye yabe yabe a fuska. Zayyan ya rungume shi.
"My son I owe you my life"
"And I owe you mine" yaji wani ya fada daga bayansa.
Sannu a hankali ya juya yana kallon mutumin dan lukuti ga tumbi amma komai nasa yana nuni da cewa ba karamin mutum bane. Ina yasan fuskar nan yake ta tunani.
"Baban Alheran kayi hakuri banzo da wuri ba"
Zuciyarsa ta nemi bugawa don bai manta mutumin da yake kiransa da wannan sunan ba. Sai yanzu yaso ganin kama. Bakinsa yana rawa yace "Baban Arifah? Col. Nasiruddeen?"
Rungume shi yayi suka fashe da kuka a tare mutane na kallonsu wasu suna yi.
Ga Awwab kuwa babu inda baya rawa a jikinsa. A yau ya yarda soja daban namiji daban. Duk yadda yake son ya dake kwanansa nawa yana kuka saboda jin cewa Babansa Zayyan yana nan amma babu tabbas sai ido ya gani. Shekarun da yawa amma tabbas shine wannan mutumin da ya ga duniya kuma duniya ta ganshi.
Muryarsa tana rawa yace "kaine Tureta?" Yadda ya taba yi masa farkon haduwarsu.
Zayyan ya dago kansa daga kafadar Excellency yayi masa murmushi "nine yaro. Ka sanni ne?"
Tsigar jikin Awwab har tashi tayi a lokacin da ya kamo hannuwan Zayyan duka biyun "sunana Muhammad Awwab Mustapha...ka tuna ni?" Ya kare tambayar da kuka.
Wasu sababbin hawayen suka sauko daga idanun Zayyan jikinsa shima yana rawa ya sanya hannuwansa biyu a gefen kumatun Awwab da suke tsayi kusan daya.
"Awwab din Mairamata?"
Awwab ya gyada kai nasa hawayen suna gudu kamar famfo baya tunanin yin komai domin tsayar dasu.
"Major da Hadir fa?"
"Suna cikin koshin lafiya"
"Mairama?"
"Na barota lafiya"
"Alheran dinka?"
"Tana jiran Daadaa yazo ya aura mata Awwab" yace yana murmushi mai hade da kuka. Zayyan ma sai ya fadada murmushinsa.
"Cikin jikin Umminka?"
"Alive and well sai munje gida zaka ga ko mene"
"Awwab?"
"Daadaa"
"Nayi kewarku, nayi kuka, nayi hakuri nayi hauka duka a rashin sanin makomar rayuwata. Ku kaini gida...ku kaini wurin iyalina"
Kankameshi Awwab yayi suna kuka sosai abin tausayi da tsinka zuciya.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Da ya fito Chibuzor yana tsaye can gefe ya gaji da magana ya koma yana sabunta tunani da nemarwa kansa mafita. Baiyi zaton haka abin zai zama ba gabadaya ya shiga cikin tashin hankali saboda tsoron kada ya kasa fitar da Zayyan.
Wancan mutumin ne ya dawo gareshi yace masa akwai mai wannan sunan da ya taba zama amma yanzu baya nan.
Wani sanyi yaji ya ratsa zuciyarsa "a ina zan same shi? Sako nake dashi mai mahimmanci"
"Kana iya fada min sai na gani sakon yana da amfani ko babu"
Da dukkan murnarsa yace "na hadu da dan uwansa ne a prison...."
"You must be crazy" Sojan ya daka masa tsawar da ta janyo hankalin sauran da suke gefe. Shi kuwa Chibuzor jikinsa rawa ya soma yi. Tun ba yau ba yaki jinin duk wani abu da zai hada shi da hukuma. Sauran suka taru a kansa ana ta daga murya ya gigice. Fada suke yi kawai akan yazo musu da zancen banza. Meye hadinsu da prison da zai ce ya hadu da dan uwan dayansu. Dadin kayan haushin ma wanda yake magana a kai baya nan. Basuyi masa uzuri yayi musu bayanin da ya dace ba suka nemi dukansa ya gudu. A gajiye ya koma hotel din da yayi masauki ya kira matarsa Emma ya fada mata yadda ta kasance.
"Ka koma gobe ka dage sai sun barka kayi magana da wani mai mukami a ciki. Banda abinsu waye yake yanke hukunci babu sauraron bayani?"
"Gaskiya bazan iya komawa ba. Akwai matsalolin tsaro a kasar nan. Nayi sa'a da basu kamani sun rufe ba. Kallon wani mara hankali ina jin suke yi min"
"Yanzu me kake tunanin yi a kai?"
"Ban sani ba" ya fada cike da damuwa.
"Darling, me zai hana kayi amfani da media? Ka tuna nima fa a TV kawata ta ganka a news lokacin da aka kamaka a airport shine ta fada min"
Ihun murna Chibuzor yayi yana gode mata. Sam baiyi wannan tunanin ba yaje zai jefa kansa ga wahala.
Karfe goma washegari a gidan talabijin na NTA reshen garin tayi masa. Filin cigiya da sanarwa ya nema saboda a ganinsa gidan TV musamman na kasa wato NTA zai fi saurin zama hanyar yada cigiyar. Idan ya gama da nan niyarsa ya nemi gidan rediyo kuma a nan Sakkwato da Kano. Wata ma'aikaciya ce tayi masa bayanin cewa zai biya bayan ya fadi na kwana nawa yake so a rinka sanya sakon. Da suka gama da wannan ya fahimci komai ta bashi form da zai cike abinda yake nema.
"Idan akwai hoton wanda kake nema ko naka idan sun san fuskarka sai ka kawo"
"Babu hoto sai sunaye"
"Rubuta min a nan..." ta saka yatsanta a inda take bukata.
Chibuzor bai rike sunayen duka ba amma ya rubuta abinda ya tuna.
(Ina neman iyalin Lt. Zayyan Muhammad Tureta na Giginya Barrack Sokoto wanda ya tafi Liberia a 1993. Sunan matarsa Mariyama, yarinyarsa Al.....) duk yadda yaso ya kasa tuna sunan Radhiya da Zayyan ya fada masa wato Alheran (abokinsa Hadir da Mustafa da kuma Col. Nasiruddeen Aliyu). Sunan karshe shine wanda yafi zama sosai a kansa. Matar ya mikawa takardar zata duba domin tsara yadda sanarwar zata kasance ta karanta bayanin nasa bai wani gamsar da ita ba. Dole sai sunyi masa tambayoyi kenan yadda zai iya fadar me yake bukata kada ayi asarar kudi.
"Su wadannan baka san sunayen iyayensu ba domin saurin gano su?"
"Akwai matsala ne? Ban sani ba" ya bata amsa yana fatan kada tace bazai yiwu ba. "Amma ai wannan na rike, Col Nasiruddeen Aliyu.."
Daga bayansa wani ya taho rike da takardu ya dakata da sauri "Col Nasiruddeen Aliyu dai gwamnan Plateau? Me yayi? Ke akwai sabon news ne?"
"Ka sanshi ne? Nemansa nake" Chibuzor yace shima da sauri.
"Gwamna ne fa, waye bai sanshi ba? Me yake faruwa ne?" Ya tambayi matar.
Hannunsa Chibuzor ya rike "shi gwamnan soja ne? Yaje Liberia tsakanin 1993 da 1994?"
A dan tsorace mutumin ya zame hannunsa "tsohon soja ne yayi retire, amma ban sani ba ko yaje Liberia"
A gigice Chibuzor ya fito da wayarsa daga aljihu ya rattaba sunan Col. Nasiruddeen Aliyu a google search. Tashin farko sai ga bayanai sun bayyana game dashi. Inda yasan ana saurin samun bayani ya fara dubawa wato wikipedia. Karatu yake yana tsallaken layi kamar wani zai riga shi.
(Tsohon sojan kuma kwararren likita a wancan zamani ya tsunduma cikin siyasa ne wajajen 1996 inda tauraronsa ya rinka haskawa yayi suna cikin kankanin lokaci. Mutane suna alakanta wannan nasara tashi da cewa an sanshi a matsayin sojan da ya kwashi kimanin watanni takwas a hannun 'yan tawayen kasar Liberia kafin Allah Ya kubutar dashi wani dare da sojoji suka kai sumame a mabuyarsu. Tausayi da jarumtarsa da aka gani yasa bai taba tsayawa takara ya fadi ba)
Mahaukacin ihu Chibuzor ya saki yana dariya "thank you Jesus" sannan ya kaiwa mutumin nan wawura ya rungume shi kamkam sai da takardun hannunsa suka fadi. Bai tsaya bata lokaci ba ya dire mutumin ya fita daga ofishin a guje.
Kai tsaye hotel din ya koma ya tattaro kayansa ya tafi airport. Ba shi ya sami kansa a kofar gidan gwamnatin dake Jos ba sai yamma. Tunda ya gane wurin shawara ita ce ya nemi masauki gobe ya dawo. Haka kuwa akayi domin washegari takwas ma a bakin gate din ta riske shi. Ganin gwamna ba abin wasa bane. Masu gadi suka saka shi a gaba aka fara masa tambayoyi akan dalilin zuwansa.
"Sako ne zan bawa Col. Nasiruddeen"
Ganin wani mara da'a suke yi masa. Idan ba mara da'a ba ya za'ayi ya kira sunan gwamna a kofar gidansa kai tsaye irin haka. Shi kuwa dadewa rabonsa da Nigeria da kuma idan yazo ba yawo yake irin haka ba yasa ya manta abubuwa.
"Nasha wahala ku taimaka min"
"Ka koma ka nemi appoitment dashi ba wai kazo haka kawai gida ba. Idan kowa na iya ganinsa a gida duka garin nan zasu tare a nan kenan"
"Naji ta yaya ake neman appointment din?"
"Ka je office dinsa ka nema a can. Idan kayi sa'a ka ganshi a wata daya"
Wani office aka kaishi Chief Warden ya bashi takarda ya saka hannu a kai sannan ya kuma gyara tsayuwa.
"Kai jarumi ne da ban taba ji ko ganin kamarsa ba. Kasarka bata san kana raye ba tsahon shekaru ashirin da biyu sai yau zaka koma gida. Ba kai nake tausayi ba sai ire irenka da dama da suke da rai a hannun abokan gaba ko kurkuku irin wannan batare da an sani ba. Goodbye Lieutenant"
Musabaha suka yi sannan ya kuma nuna masa kofa suka fito tare. Wani gate da bai raba sanin akwai shi ba duk tsayin zamansa a wurin suka bi sai ga motoci biyar a jere na Nigerian Embassy dake Liberia a baya kuma wasu uku ne na sojojin kasar.
Motar tsakiya aka nuna masa ya shiga yana jin kansa kamar a ire iren mafarkan da yake yi na komawa gida. Cikinta ma sojoji ne da sai suka yi saluting dinsa suka shiga aka tayar. Jiniya ce tun daga prison din har babban ofishin jakadancin Nigeria dake Liberia.
Awwab ya kasa zaune ya kasa tsaye haka ma Excellency. Duka a waje suke daidai kofar shiga tare da Ambasadan suna tsaye zugar motocin nan suka jeru a gabansu.
Kafin ya yunkura an bude masa kofa ya sako kafarsa waje sanye da takalmin roba da ya mutu murus. Kayan jikinsa a kode suke sosai. Fatarsa kuwa bai san cewa ta shiga wani yanayi ba sai da ya ga mutanen dake tsaye a wurin sun zuba masa ido.
"Uncle" yaji ance da muryar da ya sani. Chibuzor ne ya taho wurinsa da hawaye yabe yabe a fuska. Zayyan ya rungume shi.
"My son I owe you my life"
"And I owe you mine" yaji wani ya fada daga bayansa.
Sannu a hankali ya juya yana kallon mutumin dan lukuti ga tumbi amma komai nasa yana nuni da cewa ba karamin mutum bane. Ina yasan fuskar nan yake ta tunani.
"Baban Alheran kayi hakuri banzo da wuri ba"
Zuciyarsa ta nemi bugawa don bai manta mutumin da yake kiransa da wannan sunan ba. Sai yanzu yaso ganin kama. Bakinsa yana rawa yace "Baban Arifah? Col. Nasiruddeen?"
Rungume shi yayi suka fashe da kuka a tare mutane na kallonsu wasu suna yi.
Ga Awwab kuwa babu inda baya rawa a jikinsa. A yau ya yarda soja daban namiji daban. Duk yadda yake son ya dake kwanansa nawa yana kuka saboda jin cewa Babansa Zayyan yana nan amma babu tabbas sai ido ya gani. Shekarun da yawa amma tabbas shine wannan mutumin da ya ga duniya kuma duniya ta ganshi.
Muryarsa tana rawa yace "kaine Tureta?" Yadda ya taba yi masa farkon haduwarsu.
Zayyan ya dago kansa daga kafadar Excellency yayi masa murmushi "nine yaro. Ka sanni ne?"
Tsigar jikin Awwab har tashi tayi a lokacin da ya kamo hannuwan Zayyan duka biyun "sunana Muhammad Awwab Mustapha...ka tuna ni?" Ya kare tambayar da kuka.
Wasu sababbin hawayen suka sauko daga idanun Zayyan jikinsa shima yana rawa ya sanya hannuwansa biyu a gefen kumatun Awwab da suke tsayi kusan daya.
"Awwab din Mairamata?"
Awwab ya gyada kai nasa hawayen suna gudu kamar famfo baya tunanin yin komai domin tsayar dasu.
"Major da Hadir fa?"
"Suna cikin koshin lafiya"
"Mairama?"
"Na barota lafiya"
"Alheran dinka?"
"Tana jiran Daadaa yazo ya aura mata Awwab" yace yana murmushi mai hade da kuka. Zayyan ma sai ya fadada murmushinsa.
"Cikin jikin Umminka?"
"Alive and well sai munje gida zaka ga ko mene"
"Awwab?"
"Daadaa"
"Nayi kewarku, nayi kuka, nayi hakuri nayi hauka duka a rashin sanin makomar rayuwata. Ku kaini gida...ku kaini wurin iyalina"
Kankameshi Awwab yayi suna kuka sosai abin tausayi da tsinka zuciya.
[7/4, 7:39 PM] +234 806 334 4334: Da ya fito Chibuzor yana tsaye can gefe ya gaji da magana ya koma yana sabunta tunani da nemarwa kansa mafita. Baiyi zaton haka abin zai zama ba gabadaya ya shiga cikin tashin hankali saboda tsoron kada ya kasa fitar da Zayyan.
Wancan mutumin ne ya dawo gareshi yace masa akwai mai wannan sunan da ya taba zama amma yanzu baya nan.
Wani sanyi yaji ya ratsa zuciyarsa "a ina zan same shi? Sako nake dashi mai mahimmanci"
"Kana iya fada min sai na gani sakon yana da amfani ko babu"
Da dukkan murnarsa yace "na hadu da dan uwansa ne a prison...."
"You must be crazy" Sojan ya daka masa tsawar da ta janyo hankalin sauran da suke gefe. Shi kuwa Chibuzor jikinsa rawa ya soma yi. Tun ba yau ba yaki jinin duk wani abu da zai hada shi da hukuma. Sauran suka taru a kansa ana ta daga murya ya gigice. Fada suke yi kawai akan yazo musu da zancen banza. Meye hadinsu da prison da zai ce ya hadu da dan uwan dayansu. Dadin kayan haushin ma wanda yake magana a kai baya nan. Basuyi masa uzuri yayi musu bayanin da ya dace ba suka nemi dukansa ya gudu. A gajiye ya koma hotel din da yayi masauki ya kira matarsa Emma ya fada mata yadda ta kasance.
"Ka koma gobe ka dage sai sun barka kayi magana da wani mai mukami a ciki. Banda abinsu waye yake yanke hukunci babu sauraron bayani?"
"Gaskiya bazan iya komawa ba. Akwai matsalolin tsaro a kasar nan. Nayi sa'a da basu kamani sun rufe ba. Kallon wani mara hankali ina jin suke yi min"
"Yanzu me kake tunanin yi a kai?"
"Ban sani ba" ya fada cike da damuwa.
"Darling, me zai hana kayi amfani da media? Ka tuna nima fa a TV kawata ta ganka a news lokacin da aka kamaka a airport shine ta fada min"
Ihun murna Chibuzor yayi yana gode mata. Sam baiyi wannan tunanin ba yaje zai jefa kansa ga wahala.
Karfe goma washegari a gidan talabijin na NTA reshen garin tayi masa. Filin cigiya da sanarwa ya nema saboda a ganinsa gidan TV musamman na kasa wato NTA zai fi saurin zama hanyar yada cigiyar. Idan ya gama da nan niyarsa ya nemi gidan rediyo kuma a nan Sakkwato da Kano. Wata ma'aikaciya ce tayi masa bayanin cewa zai biya bayan ya fadi na kwana nawa yake so a rinka sanya sakon. Da suka gama da wannan ya fahimci komai ta bashi form da zai cike abinda yake nema.
"Idan akwai hoton wanda kake nema ko naka idan sun san fuskarka sai ka kawo"
"Babu hoto sai sunaye"
"Rubuta min a nan..." ta saka yatsanta a inda take bukata.
Chibuzor bai rike sunayen duka ba amma ya rubuta abinda ya tuna.
(Ina neman iyalin Lt. Zayyan Muhammad Tureta na Giginya Barrack Sokoto wanda ya tafi Liberia a 1993. Sunan matarsa Mariyama, yarinyarsa Al.....) duk yadda yaso ya kasa tuna sunan Radhiya da Zayyan ya fada masa wato Alheran (abokinsa Hadir da Mustafa da kuma Col. Nasiruddeen Aliyu). Sunan karshe shine wanda yafi zama sosai a kansa. Matar ya mikawa takardar zata duba domin tsara yadda sanarwar zata kasance ta karanta bayanin nasa bai wani gamsar da ita ba. Dole sai sunyi masa tambayoyi kenan yadda zai iya fadar me yake bukata kada ayi asarar kudi.
"Su wadannan baka san sunayen iyayensu ba domin saurin gano su?"
"Akwai matsala ne? Ban sani ba" ya bata amsa yana fatan kada tace bazai yiwu ba. "Amma ai wannan na rike, Col Nasiruddeen Aliyu.."
Daga bayansa wani ya taho rike da takardu ya dakata da sauri "Col Nasiruddeen Aliyu dai gwamnan Plateau? Me yayi? Ke akwai sabon news ne?"
"Ka sanshi ne? Nemansa nake" Chibuzor yace shima da sauri.
"Gwamna ne fa, waye bai sanshi ba? Me yake faruwa ne?" Ya tambayi matar.
Hannunsa Chibuzor ya rike "shi gwamnan soja ne? Yaje Liberia tsakanin 1993 da 1994?"
A dan tsorace mutumin ya zame hannunsa "tsohon soja ne yayi retire, amma ban sani ba ko yaje Liberia"
A gigice Chibuzor ya fito da wayarsa daga aljihu ya rattaba sunan Col. Nasiruddeen Aliyu a google search. Tashin farko sai ga bayanai sun bayyana game dashi. Inda yasan ana saurin samun bayani ya fara dubawa wato wikipedia. Karatu yake yana tsallaken layi kamar wani zai riga shi.
(Tsohon sojan kuma kwararren likita a wancan zamani ya tsunduma cikin siyasa ne wajajen 1996 inda tauraronsa ya rinka haskawa yayi suna cikin kankanin lokaci. Mutane suna alakanta wannan nasara tashi da cewa an sanshi a matsayin sojan da ya kwashi kimanin watanni takwas a hannun 'yan tawayen kasar Liberia kafin Allah Ya kubutar dashi wani dare da sojoji suka kai sumame a mabuyarsu. Tausayi da jarumtarsa da aka gani yasa bai taba tsayawa takara ya fadi ba)
Mahaukacin ihu Chibuzor ya saki yana dariya "thank you Jesus" sannan ya kaiwa mutumin nan wawura ya rungume shi kamkam sai da takardun hannunsa suka fadi. Bai tsaya bata lokaci ba ya dire mutumin ya fita daga ofishin a guje.
Kai tsaye hotel din ya koma ya tattaro kayansa ya tafi airport. Ba shi ya sami kansa a kofar gidan gwamnatin dake Jos ba sai yamma. Tunda ya gane wurin shawara ita ce ya nemi masauki gobe ya dawo. Haka kuwa akayi domin washegari takwas ma a bakin gate din ta riske shi. Ganin gwamna ba abin wasa bane. Masu gadi suka saka shi a gaba aka fara masa tambayoyi akan dalilin zuwansa.
"Sako ne zan bawa Col. Nasiruddeen"
Ganin wani mara da'a suke yi masa. Idan ba mara da'a ba ya za'ayi ya kira sunan gwamna a kofar gidansa kai tsaye irin haka. Shi kuwa dadewa rabonsa da Nigeria da kuma idan yazo ba yawo yake irin haka ba yasa ya manta abubuwa.
"Nasha wahala ku taimaka min"
"Ka koma ka nemi appoitment dashi ba wai kazo haka kawai gida ba. Idan kowa na iya ganinsa a gida duka garin nan zasu tare a nan kenan"
"Naji ta yaya ake neman appointment din?"
"Ka je office dinsa ka nema a can. Idan kayi sa'a ka ganshi a wata daya"