Sashe 120
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kayi hakuri Ya Emzee" ta kira shi yadda taji Zayyana na fada.
"Kowa fa ya fada ke kadai ce banji kince komai ba"
"Kayi hakuri yayi kyau"
"Sosai?" Yace excitedly
"Sosai sosai"
Murmushin fuskarsa ya dauke "kai duk da haka ban hakura ba. Yau idan an shirya za'a tafi idan baki ganni ba a wurin kada ki shiga motar kowa I will come for you"
Idanunta ta zare tana kallonsa ya nuna mata kasa da ake jiranta suma jin Mama na cewa ya fada mata ta taho da kayan lallenta.
"Idan baki jirani ba zamu dena kawancen nan so please ki jira ko bana nan zan dawo" Kallonsa tayi ta dauke kai ya dan sake matsowa ya rage murya "Rahima please do this for me"
Bai jira amsarta ba ya sauka ita kuma ta koma ta dauko kayan lallen ta sauka gabanta na wata irin faduwa tana jin kamar rayuwarta bazata taba dadi ba idan babu shi a cikinta. Sai dai kuma tunanin yafi karfinta ta kowace fuska yana karyar mata da gwiwa.
Jikinta ne yayi sanyi da Ummi ta nuna mata su wa za ta yiwa. Da wane hannun za ta taba wadannan matan masu kwarjini haka. Da kyar ta iya cewa bari ta kwaba wani saura kadan wancan.
Yawun bakinta har bushewa yayi tana tsoron kada taje tayi musu mistake. Ummi ta lura da ita sai ta tashi tabi bayanta zuwa kitchen din da ta shiga da ledar kayan lallen. Salame ma sai ta bisu da sauri kafin Mairama taje ta bata dubu biyar ta murkushe sauran ta cinye ita kadai. A fusace take tazo shiga maganarsu ta dakatar da ita.
"Ummi kingansu kuwa? Ni dai tsoro nake ji"
Ummi ta tayata dibo ruwa tana tsiyaya mata a robar da ta zuba lallen da kayan hadi "na fiki tsorata in fada miki wai nice da matan gwamnoni a gidana"
Rahima tayi murmushi "kema da kanki?"
"Ahh tabdi to ni na taba ganinsu ne?"
Murmushi ta sake yi sai kuma damuwa ta bayyana "kada hannuna ya rinka rawa"
Kafadunta Ummi ta dafa "Rahima! So nake kasuwa ta bude miki ace matan manyan nan kike yiwa kunshi kina jina. Ki ajiye tsoro ki tuna cewa neman halak kike yi zaki taimaki Baffanki ko?"
"Eh"
"To ki nutsu yanzu haka dubu dari aka baki amma zan ajiye sai zaki koma gida na baki"
"Dubu dari Ummi?" Rahima tace mamaki ya isheta ta rungume Ummin tana murna "in bawa Baffana da ke da Umma sai mu raba sauran da kannena"
"Kut..." Salame tace tana yunkurin shiga kitchen din.
"Banda ni ki bawa Baffanki da Addata su sa miki albarka kinji Rahima. Allah Yasa budi ne zai zo miki da hakan."
Kasa boye murnarta tayi ta kuma rungume Ummi "Ummi nagode...dama kece Ummana da naji dadi"
Dammm zuciyar Salame ta buga taji wani irin abu ya tokare mata wuya. Ka haifi da ya rinka fatan dama wata ta haifeshi...kenan fa Rahima bata sonta ko?
"Kada na sake jin magana makamanciyar wannan kina jina. Ko me Adda Salame za ta yi miki kiyi hakuri domin duk duniya ba ka da masoyi sama da mahaifiyarka. Allah Yana fushi da mai sabawa iyaye"
Hawaye ne ya ciko idanun Rahima ta fashe da wani irin kuka "Ummi bata sona"
Da sauri Mairama ta sake rungumeta ko damuwa da lallen da ta cambala mata a jikin riga bata yi "tana sonki Rahima, nima kuma ina sonki. Baki san kece autar Ummi ba...Karami da kike gani dan karo ne kece autar"
Murmushi Rahima tayi saboda Emzee da Ummi ta ambata.
"Ko ke fa...wanke fuskar muje mu caski naira"
Da gudu gudu Salame ta bar wurin kafin su fito ta nufi dakinsu. Abin da ya zame mata sabo a rayuwarta tayi wato kuka akan yadda Rahima ta dauketa. Yanzu ashe abinda take yi mata ya isa ya sanya Rahima jin inama ba ita ce mahaifiyarta ba? Hawaye sosai take yi zuciyarta ta kuntata. Tabbas ta cutar da 'yarta saboda wani dalili mara tushe wato rashin arzikin mahaifinta. Zama tayi a dakin tana ta tunane tunanen abubuwan da ta rinka yiwa mata. Sai kuma shaidan ya tuna mata da kudin da aka bada na kunshi. Kamar an tsikareta ta tashi tayi sama saboda bata ga Ummi a falon ba. Gara ta samu ta daidaita da 'yarta yadda ko arzikin yazo tare zasu ci abinsu.
Banka kai tayi cikin dakin kai tsaye ta sameta tana nade gift da wrapping paper. Kallon banzan da ta saba tayi mata sannan ta rike kugu ta mika mata hannu.
"Bani kudin"
Sai da Ummi ta bawa iska ajiyarta na cikakken minti daya ta karasa abinda take yi kafin ta dago kai "kin bani ajiyar kudi ne Adda?"
"Kada ki raina min hankali Mairama ina kokarin muyi komai cikin lumana tunda gidan da mutane. Kudin da aka bawa 'yata ta cikina Rahima na kunshi dubu dari nake magana a kai"
Ummi ko ci kanki bata ce mata ba ta tashi ta dauko kudin a cikin wani kit ta mika mata.
"Wato da har kinyi musu mazauni a cikin kayanki saboda bakar mugunta"
"Adda Salame..."
"Sunana kenan. Idan kinso kice Salamen kai tsaye ba damuwa zanyi ba"
"Kudi kika zo karba kuma na baki saboda haka ki fice min daga daki kafin ranmu yafi haka baci" Ummi tace a haka ma kokarin danne zuciyarta take yi sosai akan halin yayarta da yadda take yiwa Rahima.
"Oho dai, da fa bamu san asali bane sai ayi mana burga. Kunje kuna ta kwantar da kai a gaban mutane saboda ace kuna da kudi"
Kashingida Ummi tayi akan gado ta nuna mata kofa "sauka kije ga irinsu can kema ki kwantar da kan ko za'a dace"
Gani tayi da gaske bazata biye mata ga bakar magana ta yaba mata sai ta sauka kawai tana kunkuni. Rahima na ganinta da envelop din kudin taji wani irin kunci a zuciyarta don tayi imani da wuya ko kwandala ta bata a ciki wanda zata bawa Baffanta da Iya. Hawaye ke neman subuce mata taji sallamar Emzee.
Matan wurin ke ta yabon abinda su ka yi jiya ana cewa iyayensu sunji dadi shi da yayarsa kowa da baiwarsa. Duk zancen da akeyi Rahima yake kallo da take duke tana yiwa wata lalle a kafarta. Kin kallonsa tayi saboda a haka ma da kyar take yi jikinta ke rawa. Yadda take motsa hannuwanta yayi ta kallo har ta gama yiwa matar ta soma na wata sannan ya tafi.
**********
Karfe uku da rabi Awwab, Raji, Yousuf da Bilal suka fito daga gidan Mami kowa sanye da fararen kaya masu ado da koren zare da hula koriya. Saidai kowa dinkinsa daban ne amma shigar kenan kore da fari.
Awwab nasa kayan wani lallausan yadi ne fari kal mai kyau anyi masa riga iya gwiwa sai hannu dogo ya saka links masu wani stone green. Aljihun gaban rigar rabin yadin da aka yi shi fari ne daya rabin kuma green sai yayi kamar triangle. Maballan rigar har wuya su ma duka green dinne sai wani siririn ado na green din zare daga gefe saya. Hular kansa da tasha kari hadin zare green da fari ce dai. Kafarsa farin takalmi cover shoe sai silver agogon dior. Kamshi yake fitarwa mai dadi shi kadai yake murmushi yana tsaye a gefen mota ya zura hannu daya a aljihun wandonsa yana danna waya.
Text ya turawa amaryarsa cewa zasu dauko Arifah su biya su dauketa sannan su wuce.
(Ni kunyar ganinka nake yi) ta rubuta masa.
(Ni kuwa kwana nayi mafarkinki...can't wait to see you baby)
Hoton fuskar kunya ta tura masa na whatsapp shine yake murmushi.
"Mintuna kadan ya rage ka ganta kake wannan murmushin kai kadai" Bilal yace yana bude gaban motarsa.
"Bazaka gane bane dan uwa....I love her to the moon and back" yayi maganar yana lumshe idanu.
"Yau da bani da Fauziyya da ka saka ni neman aure amma yanzu sai dai nayi maka dariya don duk abinka sai ka jira anyi biki zamu bari ka dauketa"
"Kayi hankali kada ku ja mu bar abin fada har jikoki"
"Me kenan?" Yousuf yace yana bude motar da zasu tafi shi da Awwab.
"Bari dai nayi shiru wadannan mazajen kannena ne kada su raina ni"
Sai da suka gama barkwancin Raji da Bilal suka shiga mota daya Awwab da Yousuf guda daya.
Su Awwab gidan Excellency suka wuce ko shiga basu yi ga Yousuf ya kira Arifah. A shirye take ta fito daidau gate inda suka yi parking. Shaddarta fara ce itama sai paint work green da stones daga wuya har kasa amma ba'a cika adon ba. Ashoke aka yi mata dauri dashi mai hawa-hawa tayi matukar kyau fuska tasha make up. Ga mayafinta green ta yafa a wuyanta. Yousuf gabadaya ya rikice ya fita ya bude mata kofar baya tana zama Awwab ya fito ya karbe key din motar.
"Ina hauka ne zan bari ka tuka ni idanunka suna bayan mota? Shiga kawai muje kada kayiwa matata asara"
Arifah dai kunya take ji murmushi kawai tayi tana gaisheshi. Yousuf dama jira yake yana shiga ya rungumota yana mata rada a kunne wai jiya basu gama taya juna murna ba. Da hannu ta rinka nuna masa saitin Awwab dake tuki.
"Wannan yafi kowa fitina ki kyale shi kawai"
Shiru yayi bai ce komai ba albarkacin Arifah da yake ganin mutumcinta sosai. Suna zuwa gidan an shimfida katuwar darduma wadda su Daada suka yi jam'in sallar la'asar. Su biyu suka tada tasu Arifah ta shige ciki.
Yau ma Mairama da kanta ta shirya Zayyan kamar kullum ya saka shadda army green dinkin tazarce. Dayake tsayi gareshi ba karamin kyau yayi ba. Sai da ta tabbatar ya gama fitowa ta rinka masa wankan turare sannan ta dauko nata kayan. Itama farar shadda ce riga da zani amma dinkin Nijar anyi mata aikin green din zare ga mayafinta to-match. Ankon kenan dama su fito a 'yan Nigeria sak banda masu taro wato Major General Zayyan, Muhammad Zayyan (Emzee), Zayyanatu Mustapha da Zayyan Hadir. Nasu kayan iri daya ne army green shadda.
Suna fitowa daga dakin Radhiya ta fito da ashokenta a hannu tayi wata kwana da ribas ta dawo kawai sai ta daga tsalle ta dane Daada.
"Kowa fa ya fada ke kadai ce banji kince komai ba"
"Kayi hakuri yayi kyau"
"Sosai?" Yace excitedly
"Sosai sosai"
Murmushin fuskarsa ya dauke "kai duk da haka ban hakura ba. Yau idan an shirya za'a tafi idan baki ganni ba a wurin kada ki shiga motar kowa I will come for you"
Idanunta ta zare tana kallonsa ya nuna mata kasa da ake jiranta suma jin Mama na cewa ya fada mata ta taho da kayan lallenta.
"Idan baki jirani ba zamu dena kawancen nan so please ki jira ko bana nan zan dawo" Kallonsa tayi ta dauke kai ya dan sake matsowa ya rage murya "Rahima please do this for me"
Bai jira amsarta ba ya sauka ita kuma ta koma ta dauko kayan lallen ta sauka gabanta na wata irin faduwa tana jin kamar rayuwarta bazata taba dadi ba idan babu shi a cikinta. Sai dai kuma tunanin yafi karfinta ta kowace fuska yana karyar mata da gwiwa.
Jikinta ne yayi sanyi da Ummi ta nuna mata su wa za ta yiwa. Da wane hannun za ta taba wadannan matan masu kwarjini haka. Da kyar ta iya cewa bari ta kwaba wani saura kadan wancan.
Yawun bakinta har bushewa yayi tana tsoron kada taje tayi musu mistake. Ummi ta lura da ita sai ta tashi tabi bayanta zuwa kitchen din da ta shiga da ledar kayan lallen. Salame ma sai ta bisu da sauri kafin Mairama taje ta bata dubu biyar ta murkushe sauran ta cinye ita kadai. A fusace take tazo shiga maganarsu ta dakatar da ita.
"Ummi kingansu kuwa? Ni dai tsoro nake ji"
Ummi ta tayata dibo ruwa tana tsiyaya mata a robar da ta zuba lallen da kayan hadi "na fiki tsorata in fada miki wai nice da matan gwamnoni a gidana"
Rahima tayi murmushi "kema da kanki?"
"Ahh tabdi to ni na taba ganinsu ne?"
Murmushi ta sake yi sai kuma damuwa ta bayyana "kada hannuna ya rinka rawa"
Kafadunta Ummi ta dafa "Rahima! So nake kasuwa ta bude miki ace matan manyan nan kike yiwa kunshi kina jina. Ki ajiye tsoro ki tuna cewa neman halak kike yi zaki taimaki Baffanki ko?"
"Eh"
"To ki nutsu yanzu haka dubu dari aka baki amma zan ajiye sai zaki koma gida na baki"
"Dubu dari Ummi?" Rahima tace mamaki ya isheta ta rungume Ummin tana murna "in bawa Baffana da ke da Umma sai mu raba sauran da kannena"
"Kut..." Salame tace tana yunkurin shiga kitchen din.
"Banda ni ki bawa Baffanki da Addata su sa miki albarka kinji Rahima. Allah Yasa budi ne zai zo miki da hakan."
Kasa boye murnarta tayi ta kuma rungume Ummi "Ummi nagode...dama kece Ummana da naji dadi"
Dammm zuciyar Salame ta buga taji wani irin abu ya tokare mata wuya. Ka haifi da ya rinka fatan dama wata ta haifeshi...kenan fa Rahima bata sonta ko?
"Kada na sake jin magana makamanciyar wannan kina jina. Ko me Adda Salame za ta yi miki kiyi hakuri domin duk duniya ba ka da masoyi sama da mahaifiyarka. Allah Yana fushi da mai sabawa iyaye"
Hawaye ne ya ciko idanun Rahima ta fashe da wani irin kuka "Ummi bata sona"
Da sauri Mairama ta sake rungumeta ko damuwa da lallen da ta cambala mata a jikin riga bata yi "tana sonki Rahima, nima kuma ina sonki. Baki san kece autar Ummi ba...Karami da kike gani dan karo ne kece autar"
Murmushi Rahima tayi saboda Emzee da Ummi ta ambata.
"Ko ke fa...wanke fuskar muje mu caski naira"
Da gudu gudu Salame ta bar wurin kafin su fito ta nufi dakinsu. Abin da ya zame mata sabo a rayuwarta tayi wato kuka akan yadda Rahima ta dauketa. Yanzu ashe abinda take yi mata ya isa ya sanya Rahima jin inama ba ita ce mahaifiyarta ba? Hawaye sosai take yi zuciyarta ta kuntata. Tabbas ta cutar da 'yarta saboda wani dalili mara tushe wato rashin arzikin mahaifinta. Zama tayi a dakin tana ta tunane tunanen abubuwan da ta rinka yiwa mata. Sai kuma shaidan ya tuna mata da kudin da aka bada na kunshi. Kamar an tsikareta ta tashi tayi sama saboda bata ga Ummi a falon ba. Gara ta samu ta daidaita da 'yarta yadda ko arzikin yazo tare zasu ci abinsu.
Banka kai tayi cikin dakin kai tsaye ta sameta tana nade gift da wrapping paper. Kallon banzan da ta saba tayi mata sannan ta rike kugu ta mika mata hannu.
"Bani kudin"
Sai da Ummi ta bawa iska ajiyarta na cikakken minti daya ta karasa abinda take yi kafin ta dago kai "kin bani ajiyar kudi ne Adda?"
"Kada ki raina min hankali Mairama ina kokarin muyi komai cikin lumana tunda gidan da mutane. Kudin da aka bawa 'yata ta cikina Rahima na kunshi dubu dari nake magana a kai"
Ummi ko ci kanki bata ce mata ba ta tashi ta dauko kudin a cikin wani kit ta mika mata.
"Wato da har kinyi musu mazauni a cikin kayanki saboda bakar mugunta"
"Adda Salame..."
"Sunana kenan. Idan kinso kice Salamen kai tsaye ba damuwa zanyi ba"
"Kudi kika zo karba kuma na baki saboda haka ki fice min daga daki kafin ranmu yafi haka baci" Ummi tace a haka ma kokarin danne zuciyarta take yi sosai akan halin yayarta da yadda take yiwa Rahima.
"Oho dai, da fa bamu san asali bane sai ayi mana burga. Kunje kuna ta kwantar da kai a gaban mutane saboda ace kuna da kudi"
Kashingida Ummi tayi akan gado ta nuna mata kofa "sauka kije ga irinsu can kema ki kwantar da kan ko za'a dace"
Gani tayi da gaske bazata biye mata ga bakar magana ta yaba mata sai ta sauka kawai tana kunkuni. Rahima na ganinta da envelop din kudin taji wani irin kunci a zuciyarta don tayi imani da wuya ko kwandala ta bata a ciki wanda zata bawa Baffanta da Iya. Hawaye ke neman subuce mata taji sallamar Emzee.
Matan wurin ke ta yabon abinda su ka yi jiya ana cewa iyayensu sunji dadi shi da yayarsa kowa da baiwarsa. Duk zancen da akeyi Rahima yake kallo da take duke tana yiwa wata lalle a kafarta. Kin kallonsa tayi saboda a haka ma da kyar take yi jikinta ke rawa. Yadda take motsa hannuwanta yayi ta kallo har ta gama yiwa matar ta soma na wata sannan ya tafi.
**********
Karfe uku da rabi Awwab, Raji, Yousuf da Bilal suka fito daga gidan Mami kowa sanye da fararen kaya masu ado da koren zare da hula koriya. Saidai kowa dinkinsa daban ne amma shigar kenan kore da fari.
Awwab nasa kayan wani lallausan yadi ne fari kal mai kyau anyi masa riga iya gwiwa sai hannu dogo ya saka links masu wani stone green. Aljihun gaban rigar rabin yadin da aka yi shi fari ne daya rabin kuma green sai yayi kamar triangle. Maballan rigar har wuya su ma duka green dinne sai wani siririn ado na green din zare daga gefe saya. Hular kansa da tasha kari hadin zare green da fari ce dai. Kafarsa farin takalmi cover shoe sai silver agogon dior. Kamshi yake fitarwa mai dadi shi kadai yake murmushi yana tsaye a gefen mota ya zura hannu daya a aljihun wandonsa yana danna waya.
Text ya turawa amaryarsa cewa zasu dauko Arifah su biya su dauketa sannan su wuce.
(Ni kunyar ganinka nake yi) ta rubuta masa.
(Ni kuwa kwana nayi mafarkinki...can't wait to see you baby)
Hoton fuskar kunya ta tura masa na whatsapp shine yake murmushi.
"Mintuna kadan ya rage ka ganta kake wannan murmushin kai kadai" Bilal yace yana bude gaban motarsa.
"Bazaka gane bane dan uwa....I love her to the moon and back" yayi maganar yana lumshe idanu.
"Yau da bani da Fauziyya da ka saka ni neman aure amma yanzu sai dai nayi maka dariya don duk abinka sai ka jira anyi biki zamu bari ka dauketa"
"Kayi hankali kada ku ja mu bar abin fada har jikoki"
"Me kenan?" Yousuf yace yana bude motar da zasu tafi shi da Awwab.
"Bari dai nayi shiru wadannan mazajen kannena ne kada su raina ni"
Sai da suka gama barkwancin Raji da Bilal suka shiga mota daya Awwab da Yousuf guda daya.
Su Awwab gidan Excellency suka wuce ko shiga basu yi ga Yousuf ya kira Arifah. A shirye take ta fito daidau gate inda suka yi parking. Shaddarta fara ce itama sai paint work green da stones daga wuya har kasa amma ba'a cika adon ba. Ashoke aka yi mata dauri dashi mai hawa-hawa tayi matukar kyau fuska tasha make up. Ga mayafinta green ta yafa a wuyanta. Yousuf gabadaya ya rikice ya fita ya bude mata kofar baya tana zama Awwab ya fito ya karbe key din motar.
"Ina hauka ne zan bari ka tuka ni idanunka suna bayan mota? Shiga kawai muje kada kayiwa matata asara"
Arifah dai kunya take ji murmushi kawai tayi tana gaisheshi. Yousuf dama jira yake yana shiga ya rungumota yana mata rada a kunne wai jiya basu gama taya juna murna ba. Da hannu ta rinka nuna masa saitin Awwab dake tuki.
"Wannan yafi kowa fitina ki kyale shi kawai"
Shiru yayi bai ce komai ba albarkacin Arifah da yake ganin mutumcinta sosai. Suna zuwa gidan an shimfida katuwar darduma wadda su Daada suka yi jam'in sallar la'asar. Su biyu suka tada tasu Arifah ta shige ciki.
Yau ma Mairama da kanta ta shirya Zayyan kamar kullum ya saka shadda army green dinkin tazarce. Dayake tsayi gareshi ba karamin kyau yayi ba. Sai da ta tabbatar ya gama fitowa ta rinka masa wankan turare sannan ta dauko nata kayan. Itama farar shadda ce riga da zani amma dinkin Nijar anyi mata aikin green din zare ga mayafinta to-match. Ankon kenan dama su fito a 'yan Nigeria sak banda masu taro wato Major General Zayyan, Muhammad Zayyan (Emzee), Zayyanatu Mustapha da Zayyan Hadir. Nasu kayan iri daya ne army green shadda.
Suna fitowa daga dakin Radhiya ta fito da ashokenta a hannu tayi wata kwana da ribas ta dawo kawai sai ta daga tsalle ta dane Daada.