Sashe 153
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kunya sosai Rahima ta ji. Sai yanzu da maganganun Ummi ta soma rarrabe abubuwa ba kamar da ba da ta afkawa soyayya da ka babu wani ilimin sanin duniya. Ummi uwa ce ta gari kuma mace da ta san girman zumunci. Ba don zumuncin ba Allah kadai Ya san irin rayuwar da za tayi da 'ya'yanta. Mutane da dama sun taimaka mata albarkacin zumunci ba ta da dalilin kin kwatanta alkhairi bayan itama anyi mata.
Da Zayyan ya dawo Salame har kasa ta durkusa ta gaishe shi ta kuma roki gafararsa wannan karon da zuciya daya take yi saboda duk abinda zai kawo hawaye a idanun Rahima gudunsa take. Kwananta biyu ta tattara ta koma da shatara ta arziki daga wurin Mairama. Rayuwa bata da tabbas, yadda ka dauketa haka za ta zo maka.
Rayuwarsu ta cigaba da tafiya gidan Mami shiru da ga ita sai Zayyana su Fauziyya an koma Katsina, Zahra kuma rana daya ma su ka tashi da su Awwab sun koma Germany. Ibrahim yana Kano, Emzee a Kaduna kowa ya cigaba da harkokinsa.
***********
Zaune suke a cikin jirgi kamar Radhiya za ta shige kirjinsa ta dora kan ta a kafadar Awwab, yatsun hannuwansu na sarke da juna yana yi mata rada a kunne tana dariya.
Dago kai tayi tana tura baki "ka ga bana so"
"Ni ina so baby, ina jira ki kirani bayan na koma ki tabbatar min kawai"
Gabadaya zancen ma kunya yake bata so take a canja wani. Ta yaya zaiyi ta cewa wai yana jin tana da ciki zai fara siyayyar haihuwa tun yanzu.
"Wane suna kike son mu saka kinsan tun yanzu zamu fara shawara"
"Kai Hamma wai me yasa kake min haka ne. Ni wallahi kunyarka nake ji"
Ido ya bude yana mata wani irin kallo "Really? Da gaske kunyata kike ji with all the......"
"Shhhh" tayi saurin rufe masa baki da hannunta ya rinka cizon cikin hannun sai da ta dauke tana kai masa duka.
"Ke ce da wani abu za ki hanani fadar gaskiya"
"Ni dai mu bar zancen nan ko na canja seat"
Alamun zip ya yiwa bakinsa ya koma ya narke mata jiki tana biye masa suna hirarsu ta masoya. Kwanaki goman da su kayi a Greece sun kafa tarihi a rayuwarsu domin kuwa sunyi su ne cikin kulawa da tsantsar kaunar juna. Kowa kokarin zarta dayan yake wurin kyautatawa ga shakuwarsu ta kara karfi kusan komai tare suke yi. Wani lokacin sai su cinye rabin dare suna hira kawai da bawa juna labarai. Yawo kuwa anyi kamar kafafu zasu tsinke.
Shiru Radhiya ta ji Awwab ya dena magana ashe bacci ne ya kwashe shi. So da tausayinsa take ji saboda idan sun sauka a Abuja yau jibi da yamma zai tafi. Sabon da su ka yi da juna a kwanakin su tare yayi karfin da ba karamin ji zasuyi a jikinsu ba idan sun rabu. Gashi zaiyi a kalla sati uku ko hudu kafin ya sami kansa. Saboda tsarin aikin nasu mutum zaiyi aiki na wasu awanni ne masu yawa sannan ya sami break wani ya karba. Haka suke yi shiyasa su kan dauki kwanaki ko watanni batare da iyalansu ba. Kullum suna tare kamar cingam idan tayi nesa dashi bata san yadda zasu ji ba. Hannunsa ta kara damkewa a hankali itama bacci yayi gaba da ita.
Sanarwar saukar jirgin cikin mintuna kalilan ne ya tashesu. Radhiya ta gyara fuskarta ta gyarawa Awwab wuyan rigarsa da ya lankwashe su ka jira saukar jirgin.
Dreban Daddy ne yazo daukarsu tare da Zayyana da Rahima wadanda su ka kankame Radhiya suna murna. Anje shiga mota Awwab ya ja Radhiya gefe.
"Schatzi ki rage tsallen nan kada ki taba lafiyar ajiyata" yayi maganar yana kallon saitin cikinta.
Dariya ta yi "Na shiga dari Hammana idan ya zama gaske za ka barni na sakata na wala kuwa?"
"Sosai ma, indai ba zai dami babyna ba"
Gidan Mami su ka wuce Radhiya ta sami kanta da matsananciyar jin kunyarta kuwa. Mami ta taho da murnarta za ta rungumeta ta zube a kasa tana kwasar gaisuwa.
"Kaniyarki Radhiya, surukar ki na can Maitama" tayi nuni da kofar gidan tana nufin Ummi "zo nan in gani idan ya kula min da ke yadda ya kamata"
"Mami ni zaki fara dubawa ko tana kula dani" Awwab yace yana zama a hannun kujera.
"Waye yake ta katon mutum kamar ka? Zayyana dauko musu mukullinsu aje a huta abincinku ma yana can"
Duk wani nauyi ya kama Radhiya da kyar ta iya tashi bayan Mami ta matsa mata. Suna fita su ka shiga gidan Mama Radhiya ta dauki DK yaron sai girma yake karawa ga wayo. Da murna ta rungume Maman ita kuwa baki yaki rufuwa ganin 'ya'yan nata sunyi shar da su gwanin ban sha'awa. Abincin da ta dafa musu ita ma su Rahima sun kai musu nasu gidan.
Awwab ne ya bude kofar yana rike da hannunta "finally we are home...shiga da kafar dama kuma kiyi addu'a"
Umarninsa ta bi su ka shiga tare. Numfashinta ne ya tsaya a bakinta saboda irin dukiyar da mahaifinta ya narkar a falon kawai. Awwab ne ya ke janta sai da su ka shiga kitchen, store da dakunan gidan guda uku wanda daya da yafi kusa da kofa falo aka maidawa Awwab saboda baki maza.
Wanka da salloli su ka gabatar sannan aka ci abinci. Ranar kafin tara sun kwanta jiki kamar anyi musu duka. Washegari ma kafin fa dora komai an kawo daga gidajen biyu shiyasa ba ta dafa komai ba. Gidan Mami da Mama suka je su kai musu tsarabarsu sannan su ka wuce gidan Ummi.
Daada baki yaki rufuwa ya ga Alheran dinsa ta kara kyau ta ciko.
"Awwab me kake bata ne?"
Kunya ta kama Awwab ya sunkuyar da kai. Ummi tana ta jansa da hira sai ya kasa sakin jikinsa. Radhiya ta rinka masa dariya saboda itama sai da ya tsokaneta wai ta gama hada shi da jambaki ta kasa kallon Mami. Ya san dariyar ta meye shiyasa ya rinka harararta. Falon sama su ka koma ita da Ummi ta dame ta da tambayar wai don Allah Yaushe za ta haihu.
"Wai ke ba kya jin kunya ne? Da girmanki kinyi aure mamanki za ta haihu kamata yayi ko maganar kika ji ki gudu" cewar Ummi
Wata jaka mai kyau irin ta babies Radhiya ta daukowa tana cewa "Humm uhmm...da ga wannan ma ki haifo wani ina so ni dai"
"Allah Ya tsareni ke dai kuje kuyi mun bar muku a haifa mu goya"
Abinka da sarauniyar shirme budar bakin Radhiya sai cewa tayi "Kinsan Hamma yanzu kullum addu'a yake wai Allah yasa ina....." tunowa tayi da tabargazar da za ta tafka ta tashi da gudu "na shiga ukuna Ummi baki ji ba ko"
Mairama dai dafe kai tayi sai da ta ji alamun ta sauka kasa tayi murmushi. Ance hali zanin dutse gara ta dena damun kanta da yawan damuwa idan tayi wani shirmen. Dadinta daya yadda Awwab yake sonta a hakan ta. Allah Ya kara musu zaman lafiya da fahimtar juna tace a zuci. Jakar ta dauka baka ce 'yar madaidaiciya mai kyau ta farke ledar da aka nadeta. Gefe ga aljihu hudu biyu a gaba da baya sai kuma wurin zura feeder da karamin flask. Da dan nauyinta ta bude sai da taji kwalla. Kaya ne a jere an ninke suna wani irin kamshi a sama da 'yar takarda ta rubuta (welcome to the world baby Tureta).
Overall ce fara da farar hula na auduga masu bala'ain laushi. Sai vest da pant mai zebra stripes. Da wasu unisex kayan babies guda uku, tawul din wanka, shawl yellow shima mai laushi amma ba na sakar kulu ba. Sai feeder, siririn flask da kayan wanka harda baby perfume.
Ummi ta rinka murmushi tana yiwa Radhiyanta da Emzee addu'a. Shima kullum idan ya kira sai yace Ummi jikinki babu matsala ko? Ba zai fito kai tsaye yace ciki bane wai shi kunya. Idan tace lafiya sai yace Allah Ya kaimu lafiya. Tana nan Daada ya sameta ta nuna masa.
"To ai tunda ta saya in sha Allah da ita zamu je haihuwar"
"Da kai za'a?"
"In sha Allah" ya bata amsa.
Tare su ka sauko yiwa Awwab sallama sun ce sun yafe masa zuwa gobe. Mami tayi musu tayin abinci da su ka koma amma Awwab ya rufe ido yace na Radhiya zai ci.
Murmushi tayi "kinyi girkin ne Radhiya?"
Kai a kasa tace "banyi ba Mami"
"To kaji sai ku dauka a nan a daren nan za ka takurawa 'yata"
"Haba Mami gobe fa zan tafi banci abincinta ba kuma" ya turo baki.
Yayi sa'a Mama na gidan ta tare masa kafin Mamin ta tsige shi tace su tafi gida. Sai da su ja fita tace "Mami 'yan hana ruwa gudu"
"Yanzu laifin me nayi?"
"Shi girkin da mace za ta yiwa miji akwai sirrin dankon soyayya. Kyalesu taje ko karfe nawa ne ta dafa masa tunda yana so."
Kitchen Radhiya ta shiga Awwab ya tafi yin wanka. Aikin nata ya dauki kusan awa guda da rabi har ya gama shiri ya shigo tace ya fita kada kamshin girki ya kama masa kaya.
"Tayaki zanyi"
"Nagode Hammana just wait for me a falo"
Kallo ya zauna yi amma zaman duk ya isheshi saboda yau baya son abinda zai nesanta shi da ita. Tunanin yadda zaiyi managing rayuwarsa idan ya tafi ya addabe shi sai gata ta fito tara da arba'in da wani tray mai murfi silver. Murfin zurfi gareshi da fadi marikinsa a mulmule.
Kan dinning table ta ajiye ta koma ta dauko banana and coconut shake da ta hada tun kafin ta fara komai yayi sanyi sosai.
"Hammana na gama" tace tana fiddo plates.
"Inzo inyi miki wanka sai mu ci?" Yace yana murmushi.
"Na yafe please ka zo kaci kafin nayi wanka"
Hannunsa ta kama ta ja masa kujera ya zauna sannan ta ce ya ci ta shige dakin. Murfin ya bude saboda kamshin da ya cika masa hanci. Kaza ta gasa tayi golden brown irin gashin larabawa ta zagayeta da hadin salad wanda ta kawata da kayan lambu daban daban ga chips a gefe daya. Rufewa yayi bazai iya ci ba bata nan.
Da Zayyan ya dawo Salame har kasa ta durkusa ta gaishe shi ta kuma roki gafararsa wannan karon da zuciya daya take yi saboda duk abinda zai kawo hawaye a idanun Rahima gudunsa take. Kwananta biyu ta tattara ta koma da shatara ta arziki daga wurin Mairama. Rayuwa bata da tabbas, yadda ka dauketa haka za ta zo maka.
Rayuwarsu ta cigaba da tafiya gidan Mami shiru da ga ita sai Zayyana su Fauziyya an koma Katsina, Zahra kuma rana daya ma su ka tashi da su Awwab sun koma Germany. Ibrahim yana Kano, Emzee a Kaduna kowa ya cigaba da harkokinsa.
***********
Zaune suke a cikin jirgi kamar Radhiya za ta shige kirjinsa ta dora kan ta a kafadar Awwab, yatsun hannuwansu na sarke da juna yana yi mata rada a kunne tana dariya.
Dago kai tayi tana tura baki "ka ga bana so"
"Ni ina so baby, ina jira ki kirani bayan na koma ki tabbatar min kawai"
Gabadaya zancen ma kunya yake bata so take a canja wani. Ta yaya zaiyi ta cewa wai yana jin tana da ciki zai fara siyayyar haihuwa tun yanzu.
"Wane suna kike son mu saka kinsan tun yanzu zamu fara shawara"
"Kai Hamma wai me yasa kake min haka ne. Ni wallahi kunyarka nake ji"
Ido ya bude yana mata wani irin kallo "Really? Da gaske kunyata kike ji with all the......"
"Shhhh" tayi saurin rufe masa baki da hannunta ya rinka cizon cikin hannun sai da ta dauke tana kai masa duka.
"Ke ce da wani abu za ki hanani fadar gaskiya"
"Ni dai mu bar zancen nan ko na canja seat"
Alamun zip ya yiwa bakinsa ya koma ya narke mata jiki tana biye masa suna hirarsu ta masoya. Kwanaki goman da su kayi a Greece sun kafa tarihi a rayuwarsu domin kuwa sunyi su ne cikin kulawa da tsantsar kaunar juna. Kowa kokarin zarta dayan yake wurin kyautatawa ga shakuwarsu ta kara karfi kusan komai tare suke yi. Wani lokacin sai su cinye rabin dare suna hira kawai da bawa juna labarai. Yawo kuwa anyi kamar kafafu zasu tsinke.
Shiru Radhiya ta ji Awwab ya dena magana ashe bacci ne ya kwashe shi. So da tausayinsa take ji saboda idan sun sauka a Abuja yau jibi da yamma zai tafi. Sabon da su ka yi da juna a kwanakin su tare yayi karfin da ba karamin ji zasuyi a jikinsu ba idan sun rabu. Gashi zaiyi a kalla sati uku ko hudu kafin ya sami kansa. Saboda tsarin aikin nasu mutum zaiyi aiki na wasu awanni ne masu yawa sannan ya sami break wani ya karba. Haka suke yi shiyasa su kan dauki kwanaki ko watanni batare da iyalansu ba. Kullum suna tare kamar cingam idan tayi nesa dashi bata san yadda zasu ji ba. Hannunsa ta kara damkewa a hankali itama bacci yayi gaba da ita.
Sanarwar saukar jirgin cikin mintuna kalilan ne ya tashesu. Radhiya ta gyara fuskarta ta gyarawa Awwab wuyan rigarsa da ya lankwashe su ka jira saukar jirgin.
Dreban Daddy ne yazo daukarsu tare da Zayyana da Rahima wadanda su ka kankame Radhiya suna murna. Anje shiga mota Awwab ya ja Radhiya gefe.
"Schatzi ki rage tsallen nan kada ki taba lafiyar ajiyata" yayi maganar yana kallon saitin cikinta.
Dariya ta yi "Na shiga dari Hammana idan ya zama gaske za ka barni na sakata na wala kuwa?"
"Sosai ma, indai ba zai dami babyna ba"
Gidan Mami su ka wuce Radhiya ta sami kanta da matsananciyar jin kunyarta kuwa. Mami ta taho da murnarta za ta rungumeta ta zube a kasa tana kwasar gaisuwa.
"Kaniyarki Radhiya, surukar ki na can Maitama" tayi nuni da kofar gidan tana nufin Ummi "zo nan in gani idan ya kula min da ke yadda ya kamata"
"Mami ni zaki fara dubawa ko tana kula dani" Awwab yace yana zama a hannun kujera.
"Waye yake ta katon mutum kamar ka? Zayyana dauko musu mukullinsu aje a huta abincinku ma yana can"
Duk wani nauyi ya kama Radhiya da kyar ta iya tashi bayan Mami ta matsa mata. Suna fita su ka shiga gidan Mama Radhiya ta dauki DK yaron sai girma yake karawa ga wayo. Da murna ta rungume Maman ita kuwa baki yaki rufuwa ganin 'ya'yan nata sunyi shar da su gwanin ban sha'awa. Abincin da ta dafa musu ita ma su Rahima sun kai musu nasu gidan.
Awwab ne ya bude kofar yana rike da hannunta "finally we are home...shiga da kafar dama kuma kiyi addu'a"
Umarninsa ta bi su ka shiga tare. Numfashinta ne ya tsaya a bakinta saboda irin dukiyar da mahaifinta ya narkar a falon kawai. Awwab ne ya ke janta sai da su ka shiga kitchen, store da dakunan gidan guda uku wanda daya da yafi kusa da kofa falo aka maidawa Awwab saboda baki maza.
Wanka da salloli su ka gabatar sannan aka ci abinci. Ranar kafin tara sun kwanta jiki kamar anyi musu duka. Washegari ma kafin fa dora komai an kawo daga gidajen biyu shiyasa ba ta dafa komai ba. Gidan Mami da Mama suka je su kai musu tsarabarsu sannan su ka wuce gidan Ummi.
Daada baki yaki rufuwa ya ga Alheran dinsa ta kara kyau ta ciko.
"Awwab me kake bata ne?"
Kunya ta kama Awwab ya sunkuyar da kai. Ummi tana ta jansa da hira sai ya kasa sakin jikinsa. Radhiya ta rinka masa dariya saboda itama sai da ya tsokaneta wai ta gama hada shi da jambaki ta kasa kallon Mami. Ya san dariyar ta meye shiyasa ya rinka harararta. Falon sama su ka koma ita da Ummi ta dame ta da tambayar wai don Allah Yaushe za ta haihu.
"Wai ke ba kya jin kunya ne? Da girmanki kinyi aure mamanki za ta haihu kamata yayi ko maganar kika ji ki gudu" cewar Ummi
Wata jaka mai kyau irin ta babies Radhiya ta daukowa tana cewa "Humm uhmm...da ga wannan ma ki haifo wani ina so ni dai"
"Allah Ya tsareni ke dai kuje kuyi mun bar muku a haifa mu goya"
Abinka da sarauniyar shirme budar bakin Radhiya sai cewa tayi "Kinsan Hamma yanzu kullum addu'a yake wai Allah yasa ina....." tunowa tayi da tabargazar da za ta tafka ta tashi da gudu "na shiga ukuna Ummi baki ji ba ko"
Mairama dai dafe kai tayi sai da ta ji alamun ta sauka kasa tayi murmushi. Ance hali zanin dutse gara ta dena damun kanta da yawan damuwa idan tayi wani shirmen. Dadinta daya yadda Awwab yake sonta a hakan ta. Allah Ya kara musu zaman lafiya da fahimtar juna tace a zuci. Jakar ta dauka baka ce 'yar madaidaiciya mai kyau ta farke ledar da aka nadeta. Gefe ga aljihu hudu biyu a gaba da baya sai kuma wurin zura feeder da karamin flask. Da dan nauyinta ta bude sai da taji kwalla. Kaya ne a jere an ninke suna wani irin kamshi a sama da 'yar takarda ta rubuta (welcome to the world baby Tureta).
Overall ce fara da farar hula na auduga masu bala'ain laushi. Sai vest da pant mai zebra stripes. Da wasu unisex kayan babies guda uku, tawul din wanka, shawl yellow shima mai laushi amma ba na sakar kulu ba. Sai feeder, siririn flask da kayan wanka harda baby perfume.
Ummi ta rinka murmushi tana yiwa Radhiyanta da Emzee addu'a. Shima kullum idan ya kira sai yace Ummi jikinki babu matsala ko? Ba zai fito kai tsaye yace ciki bane wai shi kunya. Idan tace lafiya sai yace Allah Ya kaimu lafiya. Tana nan Daada ya sameta ta nuna masa.
"To ai tunda ta saya in sha Allah da ita zamu je haihuwar"
"Da kai za'a?"
"In sha Allah" ya bata amsa.
Tare su ka sauko yiwa Awwab sallama sun ce sun yafe masa zuwa gobe. Mami tayi musu tayin abinci da su ka koma amma Awwab ya rufe ido yace na Radhiya zai ci.
Murmushi tayi "kinyi girkin ne Radhiya?"
Kai a kasa tace "banyi ba Mami"
"To kaji sai ku dauka a nan a daren nan za ka takurawa 'yata"
"Haba Mami gobe fa zan tafi banci abincinta ba kuma" ya turo baki.
Yayi sa'a Mama na gidan ta tare masa kafin Mamin ta tsige shi tace su tafi gida. Sai da su ja fita tace "Mami 'yan hana ruwa gudu"
"Yanzu laifin me nayi?"
"Shi girkin da mace za ta yiwa miji akwai sirrin dankon soyayya. Kyalesu taje ko karfe nawa ne ta dafa masa tunda yana so."
Kitchen Radhiya ta shiga Awwab ya tafi yin wanka. Aikin nata ya dauki kusan awa guda da rabi har ya gama shiri ya shigo tace ya fita kada kamshin girki ya kama masa kaya.
"Tayaki zanyi"
"Nagode Hammana just wait for me a falo"
Kallo ya zauna yi amma zaman duk ya isheshi saboda yau baya son abinda zai nesanta shi da ita. Tunanin yadda zaiyi managing rayuwarsa idan ya tafi ya addabe shi sai gata ta fito tara da arba'in da wani tray mai murfi silver. Murfin zurfi gareshi da fadi marikinsa a mulmule.
Kan dinning table ta ajiye ta koma ta dauko banana and coconut shake da ta hada tun kafin ta fara komai yayi sanyi sosai.
"Hammana na gama" tace tana fiddo plates.
"Inzo inyi miki wanka sai mu ci?" Yace yana murmushi.
"Na yafe please ka zo kaci kafin nayi wanka"
Hannunsa ta kama ta ja masa kujera ya zauna sannan ta ce ya ci ta shige dakin. Murfin ya bude saboda kamshin da ya cika masa hanci. Kaza ta gasa tayi golden brown irin gashin larabawa ta zagayeta da hadin salad wanda ta kawata da kayan lambu daban daban ga chips a gefe daya. Rufewa yayi bazai iya ci ba bata nan.