Sashe 130
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Envelop Ummin ta mika mata "ga kudadenki na kunshi ki kaiwa Baffanki"
Da tsananin mamaki Rahima take kallon Ummi saboda da idanunta ta ga Salame da aihinin wanda aka bata ranar da tayiwa bakin Mom Arifah. Sauran wanda tayi kuwa ba wani yawa gareshi ba to ta ina kudin yayi wannan kaurin. Kasa shiru tayi muryarta tana rawa tace "Ummi ba kin bawa Umma wancan kudin ba?"
Mairama ranta taji ya baci a tunaninta Salame ce ta fadawa Rahima ta karbe kudin. So tayi ta rufa mata asiri shine ta sake hada mata dubu dari da sauran kudin da ta samu.
"Wancan kyauta ce zanyi mata ranar babu kudi a hannuna shine na bata naki amma gashi na dawo miki dasu"
Tasan Ummin ta fada ne kawai ba yarda tayi ba. Kuka ta fashe dashi tana kara son kanwar Ummanta da danta Emzee. Cike da farinciki ta tafi gidansu. Baffanta yana kofar gida suna hira da abokinsa ya hangota. Bakinsa kamar gonar auduga ya tashi ya shige ciki da saurinsa yabi bayanta. A dakin Iya suka yada zango suna ta sakin murmushi ta je ta nanikewa Iya a jiki. Sunji dadi sosai yadda tayi fes da ita ta kara cikowa tayi kyau.
"Har kin gama hutun ne Rahima?" Iya take tambayarta tunda basuyi tsammanin dawowarta yanzu ba.
Bayani tayi musu ta cewa Iya don Allah ranar laraba tazo yinin Adda Radhiya. Labarin kirkin su Ummi tayi ta basu da yadda kasuwar kunshi ta bude mata. Da ta basu kudin ba karamin mamaki Baffanta yayi ba.
"Tare zamu je gidan Malamijon idan kin huta nayi mata godiya. Dubu dari harda sha uku a hannuna arzikin Rahimata" yace yana dariya.
Ta tashi taje bangaren matar gidan suka gaisa ba yabo ba fallasa ta dawo Iya ta mika mata kudi a leda "ga wannan Rahima nasa Baffanki ya raba kudin ki kaiwa Salame itama tasa albarka. Dubu talatin ne, Baffanki ma ya dauki talatin sauran kuma zan fara yi miki siyayya kinga ko maburgi baki dashi kada aure yayi mana zuwan bazata"
Ture kudin tayi kamar zatayi kuka tace "A'a Iya Baffa ya rike duka"
"Kul na kara ji mahaifiya ba abar wasa bace. Maza dauki ki kai mata ki dawo sai kuje can din da Baffanki ko"
Ba haka taso ba tunda zai zama Salame taci bulus harda kari amma bazata iya yiwa Iya musu ba. Daukar ledar tayi ta boye a cikin hijabinta ta kama hanyar gidan Alh Indararo.
A gidan Malamijo Radhiya bata san Rahima ta fita ba sai daga baya Ummi ke fada mata inda taje. Ta taho mata da kaya akwati guda masu kyau wanda bata yi wani amfanin kirki dasu ba kuma bata so dama ta bata a cikin gidan sai kawai ta nemi yaro ya rakata gidansu. Suna fita suka hangota tayi hanyar gidan Salame shine ta bi bayanta.
Da Rahima ta isa tsakar gidan kamar kaji sunyi dambe ko ina shinkafa ce tun wadda aka ci da rana da mai ta watse a wurin. Ga kwanuka a bakin kofofin dakuna wasu a tsakar wurin kadan ne aka ajiye a wurin wanke wanke. A mutumce ta gaishe da Maman Danmama tayi sallama a kofar dakin Salame.
Daga ciki ta amsa mata irin na gatse dinnan "Su Hajiya Rahima ne...shigo mana"
Gwiwa a sake ta shiga ta gaisheta. Bata amsa ba sai kunnenta da ta kama ta murde iya karfinta amma dauriya irinta Rahima bata yi yunkurin kwacewa ba sai hawaye da yake zuba kamar an bude famfo "dama jiranki nake yi ki dawo mai shegen kwadayi. Kin bi Mairama gidanta batare da neman izinina ba sannan da muka je akanki Hajjo da Yadikko ke yi min fada"
"Umma kiyi hakuri" tace idanunta a runtse zafin murdar kunnen tana ratsata sosai.
Salame bata raga mata ba saboda bakincikin yadda har take da bakin cewa dama Mairama ce ta haifeta. Rai a bace take fada "kinje kin sami duniya da bakinki kina cewa ni bana sonki ko? Akwai uwar da kika taba yi min ne da zan so ki? Banda kaddarar haihuwarki me zai kaini gidan fakirin mahaifinki ma. Sai ana magana kiyi ta zarowa mutane idanu"
Maman Danmama tana jinsu amma bata shiga ba saboda ko taje bazai hana Salame abinda tayi niyya ba. Bacin rai sosai Rahima take ji wanda ba don Salame ce ta kawota duniya ba yau da tayi mata fitsara da rashin kunya irin wadda bata taba sani ko ji ba.
Sauran yaran suna dakin suna dariya Salame ta cigaba ido a rufe "daga yau na sake jin kinbi Mairama gidanta sai na saba miki. Har wani arziki garesu da zaki je kamar almajira kina 'yar cikina ana baki kafa da hannu kina kunshi wai ke mai sana'a"
Kasa magana tayi sai gunjin kuka. Babu abinda ke damun Salame sai frustration da tsantsar hassadar Mairama. Yanzu kowa ya bude baki a gidansu ita yake kira a yabeta a yabi 'ya'yanta. Rayuwa tayi mata ba daidai ba ace ita ce yau a kasan kanwarta wadda a da can baya take cin arzikinta. Ga Alh Indararo tayi haukan tayi hankalin duka a banza yaki sakinta. Halifa shima kuma ya koma jikin Mairaman shine itama da ubanta ba kowan kowa ba take neman bijere mata.
"Ba dake nake ba?" Ta hayayyako mata sai ji kake tas ta dauketa da mari saboda taki amsawa. Hancin Rahima sai jini Salame niyarta ta sauke duka bacin ranta yau a jikinta ta kuma daga hannu don ko jinin bata kula dashi ba Radhiya ta damke shi ta watsar dashi gefe. Kusan tare suka shigo gidan da Rahima duka abinda suka yi taji. Zuciyarta har wani daci take yi ganin yadda ake yiwa Rahiman da take kamar kwai yanzu a wurin Ummi. Ashe shiyasa Ummin ta kara janta a jiki don ta maye mata gurbin uwa.
Tayar da ita daga durkusun da tayi a gaban Salame taso yi amma taki tashi sai ma ture hannunta da take yi.
"Ki barta ta kasheni....Umma ki kasheni ki huta indai hakan zai sanyaya miki zuciya ki dena tsanata"
Zuciya a wuya Salame ta janyo wayar rediyo "kina zaton ina wasa dake ne Rahima? Kin tashi a nan ko sai naci ub...."
Wayar ta sauke mata a jikinta ya sami fuskarta sannan ta sake dagawa a kufule sai ta sauka a gadon bayan Radhiya saboda saurin kare Rahima da tayi. A zabure Rahiman ta mike ta kawo hannu za ta riketa ta nuna mata kofa "ki fita ki tafi gidan Baffanki gani nan zuwa"
"Adda ...." tace jikinta sai rawa yake yi kukan ma ya dauke mata.
"Nace ki fita ko sai ranki ya baci" Radhiya tace cikin fada.
Da sauri kuwa ta fita tana hawaye. Radhiya ta juyo tana yiwa Salame wani irin kallo da ya tsirga mata ciki. Idanu ne na Zayyanu Tureta take gani cikin tsananin bacin rai da zafin zuciya. Kujera Radhiya ta janyo ta zauna bayanta yana uban zugi saboda dukan ya shigeta sosai. Yaran ta kalla ta daka musu tsawa tace su fice kafin ta kirga uku. Ko biyu bata kai ba suka kama gabansu a guje ya rage daga ita sai Salame.
A rayuwarta bata taba tsorata irin na yau ba. Gani take kamar an hada mata Zayyan da Mairama a jikin mutum guda ne. Boye tsoron tayi tace "zaki rama dukan ne?"
"Zan so na rama Gwaggo Salame sai dai kinci arzikin Malamijo kuma dukanki zai janyo min fushin uwa. Yau ne na biyu da naga irin abinda kike yiwa Rahima saboda Baffanta talaka ne. Sai dai mijin naki na yanzu ma bana jin zai iya kwatarki daga hannun hukuma ko yaso"
A tsorace ta nunata da yatsa "Ke ki kiyayeni bana son rashin kunya don ko uwar da ta haifeki tayi kadan"
"Ki dena zagar min Ummina, bansan me tayi miki kika tsaneta ba amma inda ta kai bazaki taba zuwa rabinsa ba har abada da wannan algae (gansa kuka) din na bakinki"
"Wato dai turoki tayi ki fada min magana saboda baku da tarbiya ko?"
"Baki ga rashin tarbiyata ba amma yanzu zan nuna miki"
Emzee ta kira ya dauka zai fara janta da hira tace ya saurareta "motar sojoji nawa zaka iya turowa a kama Gwaggo Salame batare da kowa ya sani ba"
Cikin Salame yace tsuuuu da taji muryar Emzee kuma ana zancen motar sojoji. Ko tunanin cewa shi dalibi ne bata yi ba tsoronta kawai kada a kama ta.
Abinda tace ya saka shi tunani "Adda kada kice min kema kin gano ita ta makanta Ummi"
"What???" Radhiya tace jikinta na bari Salame kuwa sulalewa tayi a kasa saboda ba karamin tsoron hatsabibancin Radhiya take yi ba tuntuni. Yarinya ce kamar aljana bata da tsoro ko kadan.
"Kuna tare ne?" Ya tambayeta saboda bai fahimci zancen ba.
"Ina gidanta yanzu haka. Emzee kayi min bayani sosai"
"Adda dalilin da yasa ta tsani Ummi saboda tana son Daada ne, sannan ita ta yiwa Ummi asiri don ta auri wannan Alhajin da take gidansa yanzu"
Kuka yaji Radhiya ta fashe dashi jikinta yana wata irin rawa sanyi na ratsata. Tsorata Salame da taso yi akan Rahima sai ya koma bakincikin muguntar da ta yiwa mahaifiyarsu.
"Makantar shekara goma Gwaggo Salame na rantse bazamu yafe miki ba" tace tana wani irin kuka.
Maman Danbaba tana jin abinda ta fada ta garzaya ta kirawo Alh Indararo ashe yana cikin daki ya dawo da wuri.
Jikin Salame na rawa ta mike da dafa bango "kizo ki fita daga gidan tunda abin naku ya koma sharri" tana rarraba idanu kada wani ya shigo.
"Adda" Radhiya taji Emzee ya kirata "me ya kaiki gidanta ba dazu kuka iso ba?"
"Rahima na biyo" ta amsa cikin kuka.
Kansa ne ya daure sosai "Rahima kuma?"
"Eh Emzee, don baka ga irin dukan da take yi mata ba"
"Me ya hadata da Rahima kuma? Ko wacce kike nufi na kasa fahimta" yace jikinsa a sanyaye yana tsananta addu'a kada abinda yake zargin tana nufi ya tabbata.
"Rahima dai mana"
"Wadda nake gani tare da Zayyana?" Yace a tsorace.
"Eh" ta soma gajiya da tambayoyin ga serious maganar da ya kamata suyi.
Muryarsa taji kamar zaiyi kuka a raunane "Adda kina nufin Rahima 'yar Gwaggo Salame ce?"
"Kanwar Halifa ba..."
Da tsananin mamaki Rahima take kallon Ummi saboda da idanunta ta ga Salame da aihinin wanda aka bata ranar da tayiwa bakin Mom Arifah. Sauran wanda tayi kuwa ba wani yawa gareshi ba to ta ina kudin yayi wannan kaurin. Kasa shiru tayi muryarta tana rawa tace "Ummi ba kin bawa Umma wancan kudin ba?"
Mairama ranta taji ya baci a tunaninta Salame ce ta fadawa Rahima ta karbe kudin. So tayi ta rufa mata asiri shine ta sake hada mata dubu dari da sauran kudin da ta samu.
"Wancan kyauta ce zanyi mata ranar babu kudi a hannuna shine na bata naki amma gashi na dawo miki dasu"
Tasan Ummin ta fada ne kawai ba yarda tayi ba. Kuka ta fashe dashi tana kara son kanwar Ummanta da danta Emzee. Cike da farinciki ta tafi gidansu. Baffanta yana kofar gida suna hira da abokinsa ya hangota. Bakinsa kamar gonar auduga ya tashi ya shige ciki da saurinsa yabi bayanta. A dakin Iya suka yada zango suna ta sakin murmushi ta je ta nanikewa Iya a jiki. Sunji dadi sosai yadda tayi fes da ita ta kara cikowa tayi kyau.
"Har kin gama hutun ne Rahima?" Iya take tambayarta tunda basuyi tsammanin dawowarta yanzu ba.
Bayani tayi musu ta cewa Iya don Allah ranar laraba tazo yinin Adda Radhiya. Labarin kirkin su Ummi tayi ta basu da yadda kasuwar kunshi ta bude mata. Da ta basu kudin ba karamin mamaki Baffanta yayi ba.
"Tare zamu je gidan Malamijon idan kin huta nayi mata godiya. Dubu dari harda sha uku a hannuna arzikin Rahimata" yace yana dariya.
Ta tashi taje bangaren matar gidan suka gaisa ba yabo ba fallasa ta dawo Iya ta mika mata kudi a leda "ga wannan Rahima nasa Baffanki ya raba kudin ki kaiwa Salame itama tasa albarka. Dubu talatin ne, Baffanki ma ya dauki talatin sauran kuma zan fara yi miki siyayya kinga ko maburgi baki dashi kada aure yayi mana zuwan bazata"
Ture kudin tayi kamar zatayi kuka tace "A'a Iya Baffa ya rike duka"
"Kul na kara ji mahaifiya ba abar wasa bace. Maza dauki ki kai mata ki dawo sai kuje can din da Baffanki ko"
Ba haka taso ba tunda zai zama Salame taci bulus harda kari amma bazata iya yiwa Iya musu ba. Daukar ledar tayi ta boye a cikin hijabinta ta kama hanyar gidan Alh Indararo.
A gidan Malamijo Radhiya bata san Rahima ta fita ba sai daga baya Ummi ke fada mata inda taje. Ta taho mata da kaya akwati guda masu kyau wanda bata yi wani amfanin kirki dasu ba kuma bata so dama ta bata a cikin gidan sai kawai ta nemi yaro ya rakata gidansu. Suna fita suka hangota tayi hanyar gidan Salame shine ta bi bayanta.
Da Rahima ta isa tsakar gidan kamar kaji sunyi dambe ko ina shinkafa ce tun wadda aka ci da rana da mai ta watse a wurin. Ga kwanuka a bakin kofofin dakuna wasu a tsakar wurin kadan ne aka ajiye a wurin wanke wanke. A mutumce ta gaishe da Maman Danmama tayi sallama a kofar dakin Salame.
Daga ciki ta amsa mata irin na gatse dinnan "Su Hajiya Rahima ne...shigo mana"
Gwiwa a sake ta shiga ta gaisheta. Bata amsa ba sai kunnenta da ta kama ta murde iya karfinta amma dauriya irinta Rahima bata yi yunkurin kwacewa ba sai hawaye da yake zuba kamar an bude famfo "dama jiranki nake yi ki dawo mai shegen kwadayi. Kin bi Mairama gidanta batare da neman izinina ba sannan da muka je akanki Hajjo da Yadikko ke yi min fada"
"Umma kiyi hakuri" tace idanunta a runtse zafin murdar kunnen tana ratsata sosai.
Salame bata raga mata ba saboda bakincikin yadda har take da bakin cewa dama Mairama ce ta haifeta. Rai a bace take fada "kinje kin sami duniya da bakinki kina cewa ni bana sonki ko? Akwai uwar da kika taba yi min ne da zan so ki? Banda kaddarar haihuwarki me zai kaini gidan fakirin mahaifinki ma. Sai ana magana kiyi ta zarowa mutane idanu"
Maman Danmama tana jinsu amma bata shiga ba saboda ko taje bazai hana Salame abinda tayi niyya ba. Bacin rai sosai Rahima take ji wanda ba don Salame ce ta kawota duniya ba yau da tayi mata fitsara da rashin kunya irin wadda bata taba sani ko ji ba.
Sauran yaran suna dakin suna dariya Salame ta cigaba ido a rufe "daga yau na sake jin kinbi Mairama gidanta sai na saba miki. Har wani arziki garesu da zaki je kamar almajira kina 'yar cikina ana baki kafa da hannu kina kunshi wai ke mai sana'a"
Kasa magana tayi sai gunjin kuka. Babu abinda ke damun Salame sai frustration da tsantsar hassadar Mairama. Yanzu kowa ya bude baki a gidansu ita yake kira a yabeta a yabi 'ya'yanta. Rayuwa tayi mata ba daidai ba ace ita ce yau a kasan kanwarta wadda a da can baya take cin arzikinta. Ga Alh Indararo tayi haukan tayi hankalin duka a banza yaki sakinta. Halifa shima kuma ya koma jikin Mairaman shine itama da ubanta ba kowan kowa ba take neman bijere mata.
"Ba dake nake ba?" Ta hayayyako mata sai ji kake tas ta dauketa da mari saboda taki amsawa. Hancin Rahima sai jini Salame niyarta ta sauke duka bacin ranta yau a jikinta ta kuma daga hannu don ko jinin bata kula dashi ba Radhiya ta damke shi ta watsar dashi gefe. Kusan tare suka shigo gidan da Rahima duka abinda suka yi taji. Zuciyarta har wani daci take yi ganin yadda ake yiwa Rahiman da take kamar kwai yanzu a wurin Ummi. Ashe shiyasa Ummin ta kara janta a jiki don ta maye mata gurbin uwa.
Tayar da ita daga durkusun da tayi a gaban Salame taso yi amma taki tashi sai ma ture hannunta da take yi.
"Ki barta ta kasheni....Umma ki kasheni ki huta indai hakan zai sanyaya miki zuciya ki dena tsanata"
Zuciya a wuya Salame ta janyo wayar rediyo "kina zaton ina wasa dake ne Rahima? Kin tashi a nan ko sai naci ub...."
Wayar ta sauke mata a jikinta ya sami fuskarta sannan ta sake dagawa a kufule sai ta sauka a gadon bayan Radhiya saboda saurin kare Rahima da tayi. A zabure Rahiman ta mike ta kawo hannu za ta riketa ta nuna mata kofa "ki fita ki tafi gidan Baffanki gani nan zuwa"
"Adda ...." tace jikinta sai rawa yake yi kukan ma ya dauke mata.
"Nace ki fita ko sai ranki ya baci" Radhiya tace cikin fada.
Da sauri kuwa ta fita tana hawaye. Radhiya ta juyo tana yiwa Salame wani irin kallo da ya tsirga mata ciki. Idanu ne na Zayyanu Tureta take gani cikin tsananin bacin rai da zafin zuciya. Kujera Radhiya ta janyo ta zauna bayanta yana uban zugi saboda dukan ya shigeta sosai. Yaran ta kalla ta daka musu tsawa tace su fice kafin ta kirga uku. Ko biyu bata kai ba suka kama gabansu a guje ya rage daga ita sai Salame.
A rayuwarta bata taba tsorata irin na yau ba. Gani take kamar an hada mata Zayyan da Mairama a jikin mutum guda ne. Boye tsoron tayi tace "zaki rama dukan ne?"
"Zan so na rama Gwaggo Salame sai dai kinci arzikin Malamijo kuma dukanki zai janyo min fushin uwa. Yau ne na biyu da naga irin abinda kike yiwa Rahima saboda Baffanta talaka ne. Sai dai mijin naki na yanzu ma bana jin zai iya kwatarki daga hannun hukuma ko yaso"
A tsorace ta nunata da yatsa "Ke ki kiyayeni bana son rashin kunya don ko uwar da ta haifeki tayi kadan"
"Ki dena zagar min Ummina, bansan me tayi miki kika tsaneta ba amma inda ta kai bazaki taba zuwa rabinsa ba har abada da wannan algae (gansa kuka) din na bakinki"
"Wato dai turoki tayi ki fada min magana saboda baku da tarbiya ko?"
"Baki ga rashin tarbiyata ba amma yanzu zan nuna miki"
Emzee ta kira ya dauka zai fara janta da hira tace ya saurareta "motar sojoji nawa zaka iya turowa a kama Gwaggo Salame batare da kowa ya sani ba"
Cikin Salame yace tsuuuu da taji muryar Emzee kuma ana zancen motar sojoji. Ko tunanin cewa shi dalibi ne bata yi ba tsoronta kawai kada a kama ta.
Abinda tace ya saka shi tunani "Adda kada kice min kema kin gano ita ta makanta Ummi"
"What???" Radhiya tace jikinta na bari Salame kuwa sulalewa tayi a kasa saboda ba karamin tsoron hatsabibancin Radhiya take yi ba tuntuni. Yarinya ce kamar aljana bata da tsoro ko kadan.
"Kuna tare ne?" Ya tambayeta saboda bai fahimci zancen ba.
"Ina gidanta yanzu haka. Emzee kayi min bayani sosai"
"Adda dalilin da yasa ta tsani Ummi saboda tana son Daada ne, sannan ita ta yiwa Ummi asiri don ta auri wannan Alhajin da take gidansa yanzu"
Kuka yaji Radhiya ta fashe dashi jikinta yana wata irin rawa sanyi na ratsata. Tsorata Salame da taso yi akan Rahima sai ya koma bakincikin muguntar da ta yiwa mahaifiyarsu.
"Makantar shekara goma Gwaggo Salame na rantse bazamu yafe miki ba" tace tana wani irin kuka.
Maman Danbaba tana jin abinda ta fada ta garzaya ta kirawo Alh Indararo ashe yana cikin daki ya dawo da wuri.
Jikin Salame na rawa ta mike da dafa bango "kizo ki fita daga gidan tunda abin naku ya koma sharri" tana rarraba idanu kada wani ya shigo.
"Adda" Radhiya taji Emzee ya kirata "me ya kaiki gidanta ba dazu kuka iso ba?"
"Rahima na biyo" ta amsa cikin kuka.
Kansa ne ya daure sosai "Rahima kuma?"
"Eh Emzee, don baka ga irin dukan da take yi mata ba"
"Me ya hadata da Rahima kuma? Ko wacce kike nufi na kasa fahimta" yace jikinsa a sanyaye yana tsananta addu'a kada abinda yake zargin tana nufi ya tabbata.
"Rahima dai mana"
"Wadda nake gani tare da Zayyana?" Yace a tsorace.
"Eh" ta soma gajiya da tambayoyin ga serious maganar da ya kamata suyi.
Muryarsa taji kamar zaiyi kuka a raunane "Adda kina nufin Rahima 'yar Gwaggo Salame ce?"
"Kanwar Halifa ba..."