← Book details Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 147 OF 157

Sashe 147

Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"I am sorry my love" yace yana kara karfin rikon da yayi mata.
"I love you so much" duk da yasan ta dade da soma bacci ba zata ji ba.
Hannunsa na dama ya sarke da nata yana shafa kanta a zuciyarsa yana addu'ar Allah Ya basu zaman lafiya da albarka a zaman aurensu kuma Ya basu hakuri da juna. Soyayyar gudan jinin Tureta da ita ya girma yana rainon abarsa a zuci tun kafin su sake haduwa. Idan da akwai abinda yafi love at first sight kuwa to shi ya fada head over heels akanta. Ita ce duniyarsa, farincikinsa, cikar burinsa.
[7/4, 7:40 PM] +234 806 334 4334: Kiran assalatu na farko ya farkar da Awwab ya tashi da sauri yayi wanka saboda kada ya makara. A hankali yake komai saboda kada ya tasheta. Da ya gama ya sa dogon wando jeans ya dora rigar sanyi akan shirt din ciki don tun dare garin yake a lumshe ga iskar nan ta tsananin sanyin arewacin Nigeria da asuba. Zama yayi a gefen gadon yana shafa fuskar Radhiya a cikin duhun dakin sai haske kadan da yake fitowa daga toilet da ya bar fitila a kunne. Tashinta yayi yace asuba tayi. Sannu a hankali ta dago kan ta daga pillon ta bude nannauyan idanunta da fitowar hawaye.

Yatsansa ya dora akan lebenta "Shhhh haba babyna kinyi bacci da kuka kin tashi dashi bai kamata ba. Idan bazaki iya tashi ba ki jirani na dawo daga masallaci"

Hannunta na dama ta dunkule ta kai masa duka a kirjinsa tana kara narkewa cike da shagwaba da hawaye "bana bukata tunda ba ka sona"

Awwab yayi murmushi tare da mikewa yana son tayar da ita sosai "zan baki amsa idan na dawo"

Kunyarsa na tare da ita tayi saurin boye fuskarta cikin lallausan duvet din "Allah Ya tsare"

"Amin Alheran" 

Yasa kai ya fita sannan ta tashi tana cije lebe don ma ya fita da ya ga raki da shagwaba mai lasisi. Duk abinta bata so ya dawo ya sameta a kwance saboda tana jin kunyarsa kada yace zai taimaka mata ba yarda zata yi ba. Shawarwarin Mama Zainab da Innawuro tsohuwar kakarta da tun farko ta fara gyara mata jiki da lalle tayi amfani dasu wurin cire son jiki ta gasa kanta da ruwan zafi sosai. Tunda akwai sanyin gari sai ta kara jindadin hakan. Bata bata lokaci sosai ba saboda gudun kada ya dawo ya sameta ta shafa mai mai kamshi da body spray sannan ta mayar da t-shirt dinsa da ya bata kafin su kwanta da dogon skirt dinta. Hijabinta ta dauko a falo tazo ta tayar da sallah tana faman runtse ido.

Lokacin da Awwab ya fito a bakin gate ya hadu da Daddy. Kunya kamar ya nutse a wurin ya ji kamar ya koma saboda wani nauyin mahaifin nasa da yake ji. Samun kansa yayi da durkusawa har kasa yana tambayar Daddy din "an tashi lafiya? Yaya baki su ka kwana?"

Sakin fuska yayi saboda ya fuskanci Awwab din a takure yake da kunya ya ce "Lafiya kalau Captain yaya kwanan diyata?"

Kara masa kunyar yayi ya kasa amsawa sai kai da ya sunkuyar yana sosa keya. Daddy yayi murmushin manya yana musu addu'ar zaman lafiya.

Da aka idar da sallah a masallacin ya so yayi saurin tafiya gida amma idon Daddy ya zaunar dashi. Tsohon sojan ba wuya ya gano bakin zaren shiyasa yayi kokarin katse wani makocinsu da yake neman jansa da hirar zaben da ya kusanto ya tashi su ka dawo.

Gyangyadi Radhiya take yi akan abin sallah ta jingina bayanta da gadon ta ji ana rufe kofa. Cikin sauri ta cire hijabin ta hada da abin sallar ta ninke ta koma gadon ta rufa har ka. Sauran rufar ma a idon Awwab tayi saboda bude kofar dakin da yayi da sallama. A zuci ta amsa masa a zuwan bacci take yi. Yana kallon yadda take ta gyara kwanciya irin na masu baccin karya ya kyaleta sai da ya cire kayansa don yasan ba dadin kwanciya dasu zaiji ba ya saka jallabiya.

Zagayawa yayi gefen gadon bangaren da fuskarta ke kallo ya durkusa. Da sauri da sauri take fitar da numfashi saboda tsabar kaduwa ga hawayen tausayin kanta tana yi. Hannun Awwab ta ji ya janye rufar da tayi ya bude fuskarta. Cikin gashinta da ya bazu akan pillow din ya sarke yatsunsa yana jin yadda ta soma rawar jiki.

Idanunsa yake lumshewa yana budewa a kanta cike da kasala ya ce "Da kinyi soja yau da nayi musu dariya saboda kin basu kunya karshe. Abu kadan sai kuka jikinki yayi ta rawa."

Bakinta ta turo "to ba kaine ba..."

Ya karyar da kai idanunsa a kan bakinta "Saboda kin fini baki Schatzi, nima fa kukan nan ya kamata nayi tunda jiya aka kawoni" 

Dariyar da bata shiryawa bace ta kama ta. Yadda take dariyar ma baiki ya koma gareta ba saboda tamkar wanda aka sakawa magnet haka yake jin kansa. Sai dai yana tausayinta don yasan taji jiki...Allah Ya taimake shi an ware musu wuri ba a cikin gidan aka basu daki ba da an tafka abin kunya yadda ta rinka kiraye kirayen mutane.

"Yaya jikin naki my amazing wife?"

Juyawa take son yi daya barin saboda kunyar tambayar da yayi mata ya rike mata hannu yana girgiza kai.

"Ko zaki juya ki bari na fada miki abinda nayi niyya kafin kiyi bacci jiya" kasa kunnuwa tayi saboda ko me Awwab zai fada mata abin so ne a gareta. Ba tun yau ba ya kware wajen fada mata kalmomin da kan sa ta kwana tana murmushi ita kadai. Idonsa sarke da juna suna aikawa juna sakonni da fahimtarsu sai su din ya soma magana da muryar nan mai tsuma zuciyar Alheran Radhiya.

"Na karbi amanarki kuma na baki tawa. Matsayinki bana jin akwai wadda za ta taba samu a zuciyata. A kanki nasan mecece soyayya kuma nasan amfanin shakuwa. Baby kin faranta min rai sosai jiya duk da kin so cika min kunne da kuka...." murmushi tayi ta kawar da kanta shi kuwa tafin hannuwanta ya bi ya sumbata. Kafin ya cigaba da cewa,

"You have my love" ta dago kai kadan ta dube shi.

"You have my trust" ya matse hannunta yadda ba zata ji zafi ba.

"And you have my respect" ya duka tare da kissing goshinta.

Zai dago Radhiya ta zura duka hannuwanta ta rungumeshi a jikinta. Suna shakar kamshin jikin juna a haka ya dawo kusa da ita ya kwanta karatun nasu ya tattara ya koma na sababbin auren da suke matukar so da kaunar juna. Radhiya tayi dauriyar kin yi masa kuka amma ta kasa daga karshe. Kuka ne da tasan ba na wahala bane kawai harda wata irin soyayyar Awwab mara misaltuwa. Shi ma yana namiji yaya mamakin ganin yana tayata hawaye a lokacin da sabuwar soyayyarta take huda kowane bari na jikinsa tana sake samun mazauni. A take a wannan lokacin jikinsa yake fada masa cewa da wahala matuka wata mace ta sake samun gurbi irin na Alheran....son ta a jinin jikinsa yake. It has always been Radhiyan Hamma Awwab.

Bacci suka koma irin wanda da wuya in sun taba yin irinsa mai tattare da nutsuwa da kwanciyar hankali. Basu san lokacin da Zayyana tazo wurin goma ba tayi ta doka sallama da breakfast dinsu har ta gaji. Kofar net da aka zagaye karamar barandar da ke gaban katuwar golden kofar gidansu mai kyau ta bude ta ajiye kwandon tunda a rufe komai yake da wani kyalle mai kyau. Komawa tayi ta fadawa Mama ita fa taji shiru.

Shadaya saura wayar Awwab ta soma ruri ya dauka da sauri zai kashe saboda kada karar ta tasar masa Radhiya dake kwance akan faffadan kirjinsa. Sunan Mama ya gani babu damar kashewa kenan yayi kokarin zame jikinsa Radhiya ta kara cukwikuye shi tana zumburo baki. Murmushi ya saki ya kawar da gashinta daga kan fuskar yace  "so adorable".

Wani kiran ne ya sake shigowa still dai Mama ce ya danyi gyaran murya kafin yayi mata sallama sannan ya gaisheta.

"Awwab kayi hakuri surukanka zasu wuce ne mutanen Sakkwato da Sumaila shine suke son yiwa Radhiya sallama. Sai na ga ya dace ka fara shigowa kayi musu bangajiya"

"Mama ni kadai zan shigo?" Ya ce kamar zaiyi kuka don tsakaninsa da Allah kunya yake ji ya shiga gidan.

"Ka nemi 'yan uwanka su Bilal kuyi sauri. Ina kanwar taka ina fata ta tashi ta shirya ba jimawa zasu shigo"

Shirun da yayi da guntuwar in'ina ya fahimtar da Hajiya Mama komai. Murmushi tayi mai sauti Awwab ya rasa me zaiyi sai ya ga Radhiyan ma ta farka kawai shiru tayi tana kunyar tashi.

"Bani ita Awwab" yaji Mama tace.

Dora mata wayar yayi a kunne kafin ta soma magana Mama tace "saurareni da kyau Radhiya kin tuna me nace jiya ko?"

"Uhmm" tace a hankali.

"Tau, ki shiga ruwan zafi sosai kinga gobe akwai tafiya gabanmu idan ba so kike ayi ta zancenki ba ki gyara kanki. Zan shigo anjima idan bakiyi ba zan gane kuma kinsan sauran"

Rufe kanta tayi ta mikawa Awwab wayarsa. Tana ji ya tashi ya shiga toilet bai dade ba ya fito ya yaye rufar da tayi sai da tayi masa ihun ganinsa da tawul kadai gashi ya cire mata abinda ta rufe kanta. 

"Muje muyi wanka" kawai yace ya sunkuceta yana cewa ashe buhun sumunti ce bai sani ba. Duk wani zille zille da taso yi bai barta ta fita ba a haka akayi wankan. Bayan sun gama ya hada mata ruwa mai zafi a robar da ta zauna dazu wadda saboda hakan Mama ta saka musu ita.

"Kin sanni da kunne ina jin me Mama take fada" ya kashe mata ido ya fita ya barta da tulin kunya.

Lokacin da ta fito ya gama saka kaya sai wannan kamshin nasa na musamman take ji. Shadda ce ya saka mara nauyi ga hularsa a gefe.

"Ba don ina tsoron kaina ba kuma dai ana jirana da na tsaya shiryaki da kaina baby" yace lokacin da ya ajiye brush din da ya taje saisayayyen kansa.

"Na yafe fita ka tafi"
Chapter 147 · 0% Book details