Sashe 67
Ku Dube Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alh Baba yace "babu wanda zan tilasta a cikinku na gama wannan yayin. Tunda ba kya so Allah Ya kawo miki naki rabon. Kai kuma ku gama magana da waccan ina bukatar amsa da wuri" yana kaiwa nan yace duka ya sallamesu su tashi su tafi. Ghazalatu kuka kamar ana yankar naman jikinta amma tasan halin Mummynta da masifa. Idan ta kuskura ta komawa Awwab sai taji babu dadi. Hussaina duniya shar ta kira Nura tace ya fara yakin neman soyayyar Ghazalatu ita ta gama nata aikin.
Awwab bai jira kowa ba ya fita ya bar gidan. Jin kansa yake kamar an zare masa wata kaya da ta tokare shi. Lallai zuciya bata da kashi. Bai tantance zafin so ba sai akan Alheran. Kinsa da Ghazalatu tayi ko kadan baiyi masa ciwo ba don tunda Mummy taje gidansu sau biyu tana cin mutumcin mahaifiyarsa yasan ko ya aureta wani kaso mai girma na kimarta ya riga ya sauka daga idanunsa.
Sallar magariba ya tsaya yi kafin ya shiga gidan. Shigarsa tayi daidai da isowarsu Mami a motar Daddy. Zahra ce ta tuku su Fauziyya na gaba su Mami na baya. Idan ka ga Zahra fuskarta tamkar wadda aka baiwa kujerar Makka. Murmushi ne yaki tafiya kamar an zana mata shi har tsokanarta Daddy yayi yace shima sai ta nemi amincewarsa sannan zai kira Imam Abdulwahab mahaifin Raji.
Kunya taji ta ruga cikin gidan kai tsaye ta tafi dakin Mami. Ummi ta gani akan sallaya ta fada jikinta tana ta dariya.
"Zahra me muka samu irin wannan murna haka"
"Ummi Alh Baba ya amince"
"Da me?" Mairama ta tambayeta tana tayata murna tun kafin taji.
Sallamar Mami yasa ta kasa cewa komai ta tashi ta koma nasu dakin da tsalle. Sai da Mami ta idar da sallah ta fada mata yadda al'amura suka juya. Ummi bata ji dadin fasawar da Ghazalatu tayi ba kuma ga dukkan alamu Mami da 'yan uwanta basu shirya ba. Indai haka ne kuwa to babu makawa Radhiya ma bazata auri Awwab ba. Meye ribarsu ayi auren da ya taba zumuncin iyaye.
Fauziyya da Zahra ma sallah suka shiga yi suka sami Radhiya ta dukunkune kanta ta cure wuri guda tana baccin wahala. Tayi kuka ne har ya saka mata ciwon kai shine bacci ya dauketa. Zayyana ta fito daga bandaki ta yayyenta kowacce da murmushi a fuskarta. Zahra ta rungumeta tana dariya itama tana tayata ta tabbata abinda yasa su kuka dazu ya wuce. Ihunsa ya tayar da Radhiya da kyar ta iya bude ido sun kumbura tayi musu sannu da zuwa.
Fauziyya ta tuna cewa dazu maganganun su Mummy su ma daga dakin Awwab sun ji bare kuma ita da suka bari a nasu dakin. Sai taji tausayinta ya kamata "kinyi sallah kuwa ko sai nazo nayi miki balotelli?"
Murmushi tayi kanta kamar ya tsage ta daure "da almakashina a jaka"
Dariya suka yi su duka yanayin dakin yana chanjawa daga shiru shiru zuwa na 'yan mata wadanda ke tsaka da jindadi. Da bin bango Radhiya ta je tayi alwala ciwon kai yayi tsanani ga zazzabi. Bayan ta idar Zahra ta taba wuyanta ganin duka jikinta yayi la'asar.
"Radhiya baki da lafiya kika zauna shiru a daki. Bari na karbo miki magani"
Da saurinta ta fita taje dakin Mami tana tambayar panadol. Ummi sai da taji babu dadi tasan halin Radhiya da saka abu a rai. Karshenta kuka ta rinka yi ya janyo mata zazzabin da ciwon kai.
"Nemo min Awwab yazo ya kaita clinic dai. Ga gajiyar hanya kuma an taho ana tsaka da biki duka babu wani hutu" Mami ta umarci Zahra tana bin bayanta zuwa dakin. Ummi ko motsi bata yi ba tana addu'ar Allah Ya kawo sauki cikin lamarin saboda tsoro da ya fara darsuwa a zuciyarta.
Hankalin Mami ba karamin tashi yayi ba da ta taba jikin Radhiya. Jiki yayi mugun zafi fuskarta har wani ja take yi.
Awwab yana cikin shiryawa bayan yayi wanka Zahra taje ta fada masa sakon Mami. Ya rigata fita daga dakin da sauri. Sallama ya tsaya yi a kofar nasu dakin amma da kyar ya daure bai kutsa kai ya shiga ciki ba. Mami ta fito da Radhiya da ta tallafo a jikinta.
"Me ya sameta haka Mami?" Awwab yace a raunane. Abinda zai kashe bakin Radhiya da wannan kuzarin nata ba karami bane shima ya sani.
"Kuje mota bari na dauko mayafi. Zazzabi ne ina jin da ciwon kai"
A hankali ta rinka tafiya ganin Awwab ya sake tayar mata da hankali. Tana son shi dole ta barshi idan ba tana son abinda Ummi take guje mata ya faru da ita ba. Wasu hawaye ne suka zubo mata duk yadda taso daurewa ta kasa.
Sai da ya dan matso da kansa kusa da ita yana son rage mata damuwa ya tsokaneta dacewa "come on Schatzi bana son shagwaba fa. Ke da zansa a yiwa allura kamar hudu kuma kike min kuka"
Duk da ciwon haka ta harare shi yayi murmushi yana cewa "in dauke ki ne?"
A dole ta daga kafa tana jin kunyarsa. Da Mami suka je asibitin aka dubata likitan yace banda zazzabi harda damuwa. Mami sai ta alakanta komai ga abinda ya faru a gidan zuwan su Gambo. A take ta yanke shawarar sanar da Daddy yayiwa yaran magana gobe idan sun amince wa juna ayi bikin kowa ya huta.
Da suka koma gida ta fita tana jiran Radhiya shiru Awwab ya hanata fitowa ta shige ciki tana fadawa Ummi wai ta ga alama ciwon soyayya ne yake damunta. Ummi dai dariyar yake tayi, neman abokin shawara take gashi Zainab bata nan.
A wajen Awwab ya tsare Radhiya da tambayoyin son jin damuwarta duk da shima yana tunanin ko abin dazu ne "me kika sa a ranki har ya saka kiki fever?"
"Babu komai Hamma"
"Saboda zuwan Mummy ne dazu ko? Komai ya wuce kinji yanzu babu zancen Ghazalatu ma. Ke kadai ce dani Schatzi kuma kin isheni don son da nake miki bana jin akwai wadda zata sami rabinsa a wurina"
Kalaman sun mata dadi, da babu wannan matsalar da tafi kowa farinciki amma yanzu bata da wani abin yi sama da murmushi ta fake da rashin lafiya. Shima da ya ga shirun nata yayi yawa duk sai ya damu.
"I miss my Alheran, wannan mara lafiyar duk ta hanani ganinta. Kije ki kwanta and please take care of yourself for Awwab"
"Hammana sai da safe" yaji tace da karamar murya tana tafiya sai bayanta kadai yake iya gani.
Haka kawai yaji jikinsa yayi sanyi zuciyarsa tana tabbatar masa da cewa akwai wani babban al'amari a tattare da Alheran. Ko ma meye yayi niyar jira zuwa wayewar gari taji karfin jikinta sai ta fada masa damuwarta.
Daddy kuwa a daren ya kira Imam Abdulwahab ya fada masa basu da masaniya akan cewa akwai alaka tsakanin Raji da Zahra har aka yi mata miji. Imam yace basu yi sati da sani ba shi da matarsa. Sai da suka ga shige da ficen asibitin nasa yayi yawa suka matsa Munnirat kanwarsa ta sanar dasu. A lokacin hakuri kawai ya bashi tunda suna da labarin aurenta ya kusa. Major yace to aure ya tashi saboda ta sanar bata son angon nata. Yanzu haka ya kira ya sanar dashi ne cewa asabar mai zuwa ya kamata daurin aurenta amma za'a basu dama idan sun amince ya turo Raji neman aurenta. Bayerabe yasan darajar alkhairi kuma yana mutunta duk wanda ya karrama shi. Imam Abdulwahab ya rinka kwararowa Major da iyalinsa addu'a kuma ya tabbatar masa in sha Allah ranar asabar Zahra zata yi aure kamar yadda aka tsara tun farko. Da kansa yaje dakin Raji da yake kwance yana jinyar zuciyarsa yayi masa kyakkyawan albishir. A take ya wartsake sai gashi har asuba suna waya da Zahra wadda itama ta ware baka ce ita ce take ta koke koke a kwanakin da suka gabata ba.
SABUWAR RAYUWAR
"To Alhamdulillah al'amura sun daidaita Alh Baba ya amince da auren Awwab da Radhiya sannan duk da ba haka muka so ba Ghazalatu tace ta fasa. Allah Ya sani Ummin Awwab ban so kuka san wannan matsalar ba ko kadan a madadin Gambo muna masu baki hakuri akan cin zarafin da tayi muku jiya"
Ummi ta shiga girgiza kai "bamu hakurin tamkar kuna nuna akwai bambanci tsakaninmu ne Daddy. Wallahi har raina banji haushi ba saboda haka magana ta wuce"
Mami tayi murmushin jindadi sannan Daddy ya kalli Awwab da duk motsin Radhiya akan idonsa yake yana kokarin hada ido da ita amma taki dago kai. Gyaran murya yayi Awwab din yayi saurin juyar da kansa daya gefen yana murmushi.
"Awwab ga kanwarka nan na baka amana ko bayan raina ban yarda ka rabu da ita ba. Idan ta bata maka ko tayi ba daidai ba ka hukuntata amma ban yarda diyar Zayyan tayi kuka saboda rashin adalcin gidan aure ba"
Farincikin da Awwab yake ji a wannan lokacin bazai misaltu ba. Dan taki kalilan ya rage masa da mallakar abar kaunarsa. Yana sake dawowa ko sati daya ne hutun yake so a daura aurensu.
"In sha Allahu bazan baku kunya ba"
"Radhiya baki ce komai ba" Daddy yace yana kallonta yana murmushi.
"Ai ka kashe bakin nata Daddy yau daya dai ga kunya ga sauran zazzabi 'yata bata da ta cewa" inji Mami.
Hawayen zuci Radhiya take yi na samu da rashi da ya sameta a lokaci guda. A hankali sautin kukanta ya fito fili. Yadda Awwab ya gigice sai ya baka tausayi ana ta tambayarta ko jikin ne ta kasa magana. Ummi jikinta yayi sanyi amma ta san har ga Allah hakan da tayi shine daidai. Tafi kowa sanin ciwon da ta kunsa saboda juya mata baya da Salame tayi da rashin kyakkyawar alaka mai tattare da shakuwa da tayi karanci a nasu gidan. Banda ma yanzu da abubuwa suke dan chanjawa amma a da kam gidansu nafsi nafsi kawai akeyi kuma bata cire kanta a ciki ba saboda haka a ka sabar musu.
"Radhiya ko bakya son auren ne?" Daddy yace bayan ya karar da duka tambayoyin da yake jin zaiyi mata.
A razane Awwab ya kalle shi yace "Daddy?"
Awwab bai jira kowa ba ya fita ya bar gidan. Jin kansa yake kamar an zare masa wata kaya da ta tokare shi. Lallai zuciya bata da kashi. Bai tantance zafin so ba sai akan Alheran. Kinsa da Ghazalatu tayi ko kadan baiyi masa ciwo ba don tunda Mummy taje gidansu sau biyu tana cin mutumcin mahaifiyarsa yasan ko ya aureta wani kaso mai girma na kimarta ya riga ya sauka daga idanunsa.
Sallar magariba ya tsaya yi kafin ya shiga gidan. Shigarsa tayi daidai da isowarsu Mami a motar Daddy. Zahra ce ta tuku su Fauziyya na gaba su Mami na baya. Idan ka ga Zahra fuskarta tamkar wadda aka baiwa kujerar Makka. Murmushi ne yaki tafiya kamar an zana mata shi har tsokanarta Daddy yayi yace shima sai ta nemi amincewarsa sannan zai kira Imam Abdulwahab mahaifin Raji.
Kunya taji ta ruga cikin gidan kai tsaye ta tafi dakin Mami. Ummi ta gani akan sallaya ta fada jikinta tana ta dariya.
"Zahra me muka samu irin wannan murna haka"
"Ummi Alh Baba ya amince"
"Da me?" Mairama ta tambayeta tana tayata murna tun kafin taji.
Sallamar Mami yasa ta kasa cewa komai ta tashi ta koma nasu dakin da tsalle. Sai da Mami ta idar da sallah ta fada mata yadda al'amura suka juya. Ummi bata ji dadin fasawar da Ghazalatu tayi ba kuma ga dukkan alamu Mami da 'yan uwanta basu shirya ba. Indai haka ne kuwa to babu makawa Radhiya ma bazata auri Awwab ba. Meye ribarsu ayi auren da ya taba zumuncin iyaye.
Fauziyya da Zahra ma sallah suka shiga yi suka sami Radhiya ta dukunkune kanta ta cure wuri guda tana baccin wahala. Tayi kuka ne har ya saka mata ciwon kai shine bacci ya dauketa. Zayyana ta fito daga bandaki ta yayyenta kowacce da murmushi a fuskarta. Zahra ta rungumeta tana dariya itama tana tayata ta tabbata abinda yasa su kuka dazu ya wuce. Ihunsa ya tayar da Radhiya da kyar ta iya bude ido sun kumbura tayi musu sannu da zuwa.
Fauziyya ta tuna cewa dazu maganganun su Mummy su ma daga dakin Awwab sun ji bare kuma ita da suka bari a nasu dakin. Sai taji tausayinta ya kamata "kinyi sallah kuwa ko sai nazo nayi miki balotelli?"
Murmushi tayi kanta kamar ya tsage ta daure "da almakashina a jaka"
Dariya suka yi su duka yanayin dakin yana chanjawa daga shiru shiru zuwa na 'yan mata wadanda ke tsaka da jindadi. Da bin bango Radhiya ta je tayi alwala ciwon kai yayi tsanani ga zazzabi. Bayan ta idar Zahra ta taba wuyanta ganin duka jikinta yayi la'asar.
"Radhiya baki da lafiya kika zauna shiru a daki. Bari na karbo miki magani"
Da saurinta ta fita taje dakin Mami tana tambayar panadol. Ummi sai da taji babu dadi tasan halin Radhiya da saka abu a rai. Karshenta kuka ta rinka yi ya janyo mata zazzabin da ciwon kai.
"Nemo min Awwab yazo ya kaita clinic dai. Ga gajiyar hanya kuma an taho ana tsaka da biki duka babu wani hutu" Mami ta umarci Zahra tana bin bayanta zuwa dakin. Ummi ko motsi bata yi ba tana addu'ar Allah Ya kawo sauki cikin lamarin saboda tsoro da ya fara darsuwa a zuciyarta.
Hankalin Mami ba karamin tashi yayi ba da ta taba jikin Radhiya. Jiki yayi mugun zafi fuskarta har wani ja take yi.
Awwab yana cikin shiryawa bayan yayi wanka Zahra taje ta fada masa sakon Mami. Ya rigata fita daga dakin da sauri. Sallama ya tsaya yi a kofar nasu dakin amma da kyar ya daure bai kutsa kai ya shiga ciki ba. Mami ta fito da Radhiya da ta tallafo a jikinta.
"Me ya sameta haka Mami?" Awwab yace a raunane. Abinda zai kashe bakin Radhiya da wannan kuzarin nata ba karami bane shima ya sani.
"Kuje mota bari na dauko mayafi. Zazzabi ne ina jin da ciwon kai"
A hankali ta rinka tafiya ganin Awwab ya sake tayar mata da hankali. Tana son shi dole ta barshi idan ba tana son abinda Ummi take guje mata ya faru da ita ba. Wasu hawaye ne suka zubo mata duk yadda taso daurewa ta kasa.
Sai da ya dan matso da kansa kusa da ita yana son rage mata damuwa ya tsokaneta dacewa "come on Schatzi bana son shagwaba fa. Ke da zansa a yiwa allura kamar hudu kuma kike min kuka"
Duk da ciwon haka ta harare shi yayi murmushi yana cewa "in dauke ki ne?"
A dole ta daga kafa tana jin kunyarsa. Da Mami suka je asibitin aka dubata likitan yace banda zazzabi harda damuwa. Mami sai ta alakanta komai ga abinda ya faru a gidan zuwan su Gambo. A take ta yanke shawarar sanar da Daddy yayiwa yaran magana gobe idan sun amince wa juna ayi bikin kowa ya huta.
Da suka koma gida ta fita tana jiran Radhiya shiru Awwab ya hanata fitowa ta shige ciki tana fadawa Ummi wai ta ga alama ciwon soyayya ne yake damunta. Ummi dai dariyar yake tayi, neman abokin shawara take gashi Zainab bata nan.
A wajen Awwab ya tsare Radhiya da tambayoyin son jin damuwarta duk da shima yana tunanin ko abin dazu ne "me kika sa a ranki har ya saka kiki fever?"
"Babu komai Hamma"
"Saboda zuwan Mummy ne dazu ko? Komai ya wuce kinji yanzu babu zancen Ghazalatu ma. Ke kadai ce dani Schatzi kuma kin isheni don son da nake miki bana jin akwai wadda zata sami rabinsa a wurina"
Kalaman sun mata dadi, da babu wannan matsalar da tafi kowa farinciki amma yanzu bata da wani abin yi sama da murmushi ta fake da rashin lafiya. Shima da ya ga shirun nata yayi yawa duk sai ya damu.
"I miss my Alheran, wannan mara lafiyar duk ta hanani ganinta. Kije ki kwanta and please take care of yourself for Awwab"
"Hammana sai da safe" yaji tace da karamar murya tana tafiya sai bayanta kadai yake iya gani.
Haka kawai yaji jikinsa yayi sanyi zuciyarsa tana tabbatar masa da cewa akwai wani babban al'amari a tattare da Alheran. Ko ma meye yayi niyar jira zuwa wayewar gari taji karfin jikinta sai ta fada masa damuwarta.
Daddy kuwa a daren ya kira Imam Abdulwahab ya fada masa basu da masaniya akan cewa akwai alaka tsakanin Raji da Zahra har aka yi mata miji. Imam yace basu yi sati da sani ba shi da matarsa. Sai da suka ga shige da ficen asibitin nasa yayi yawa suka matsa Munnirat kanwarsa ta sanar dasu. A lokacin hakuri kawai ya bashi tunda suna da labarin aurenta ya kusa. Major yace to aure ya tashi saboda ta sanar bata son angon nata. Yanzu haka ya kira ya sanar dashi ne cewa asabar mai zuwa ya kamata daurin aurenta amma za'a basu dama idan sun amince ya turo Raji neman aurenta. Bayerabe yasan darajar alkhairi kuma yana mutunta duk wanda ya karrama shi. Imam Abdulwahab ya rinka kwararowa Major da iyalinsa addu'a kuma ya tabbatar masa in sha Allah ranar asabar Zahra zata yi aure kamar yadda aka tsara tun farko. Da kansa yaje dakin Raji da yake kwance yana jinyar zuciyarsa yayi masa kyakkyawan albishir. A take ya wartsake sai gashi har asuba suna waya da Zahra wadda itama ta ware baka ce ita ce take ta koke koke a kwanakin da suka gabata ba.
SABUWAR RAYUWAR
"To Alhamdulillah al'amura sun daidaita Alh Baba ya amince da auren Awwab da Radhiya sannan duk da ba haka muka so ba Ghazalatu tace ta fasa. Allah Ya sani Ummin Awwab ban so kuka san wannan matsalar ba ko kadan a madadin Gambo muna masu baki hakuri akan cin zarafin da tayi muku jiya"
Ummi ta shiga girgiza kai "bamu hakurin tamkar kuna nuna akwai bambanci tsakaninmu ne Daddy. Wallahi har raina banji haushi ba saboda haka magana ta wuce"
Mami tayi murmushin jindadi sannan Daddy ya kalli Awwab da duk motsin Radhiya akan idonsa yake yana kokarin hada ido da ita amma taki dago kai. Gyaran murya yayi Awwab din yayi saurin juyar da kansa daya gefen yana murmushi.
"Awwab ga kanwarka nan na baka amana ko bayan raina ban yarda ka rabu da ita ba. Idan ta bata maka ko tayi ba daidai ba ka hukuntata amma ban yarda diyar Zayyan tayi kuka saboda rashin adalcin gidan aure ba"
Farincikin da Awwab yake ji a wannan lokacin bazai misaltu ba. Dan taki kalilan ya rage masa da mallakar abar kaunarsa. Yana sake dawowa ko sati daya ne hutun yake so a daura aurensu.
"In sha Allahu bazan baku kunya ba"
"Radhiya baki ce komai ba" Daddy yace yana kallonta yana murmushi.
"Ai ka kashe bakin nata Daddy yau daya dai ga kunya ga sauran zazzabi 'yata bata da ta cewa" inji Mami.
Hawayen zuci Radhiya take yi na samu da rashi da ya sameta a lokaci guda. A hankali sautin kukanta ya fito fili. Yadda Awwab ya gigice sai ya baka tausayi ana ta tambayarta ko jikin ne ta kasa magana. Ummi jikinta yayi sanyi amma ta san har ga Allah hakan da tayi shine daidai. Tafi kowa sanin ciwon da ta kunsa saboda juya mata baya da Salame tayi da rashin kyakkyawar alaka mai tattare da shakuwa da tayi karanci a nasu gidan. Banda ma yanzu da abubuwa suke dan chanjawa amma a da kam gidansu nafsi nafsi kawai akeyi kuma bata cire kanta a ciki ba saboda haka a ka sabar musu.
"Radhiya ko bakya son auren ne?" Daddy yace bayan ya karar da duka tambayoyin da yake jin zaiyi mata.
A razane Awwab ya kalle shi yace "Daddy?"